Amurka Ta Sanar Da Fara Kai Farmakin Soja Mai Sunan ” Mashin Kudu” Akan Yankin Latin
Published: 14th, November 2025 GMT
Ministan yakin Amurka Pete Hegseth ya bayyana cewa kasar tasa ta fara kai farmakin da ta kira ” Mashin Kudu” akan dillalan muggan kwayoyi.
Ministan yakin na Amurka ya rubuta a Shafin X cewa; manufar wannan farmakin shi ne kare kasarmu, da kawo karshen masu dillancin muggan makamai ‘yan ta’adda, da kare kasarmu daga muggan kwayoyin da suke kashe mana ‘yan kasa.
Gwamnatin Donald Trump dai ta bude kai hare-hare akan jiragen ruwan a doron ruwan Carrebia da tekun Pacific bisa abinda take riya cewa masu fataucin muggan kwayoyi ne.
Sai dai har yanzu babu wani dalili guda daya da Amurkan ta gabatar da shi wanda yake nuni da cewa wadannan jiraegen ruwa da take kai wa harin suna dauke da muggan kwayoyi.
Amurka din ta girke jiragen ruwa na yaki da su ka hada da “Gerald Ford”.
Kafafen watsa labarun Amurka da su ka hada da ” CBS” sun ambaci cewa, makusantan Donald Trump sun ba shi shawarar kai hare-hare a cikin kasar Venezuela.
A nata gefen, gwamantin kasar ta Venezuela ta sanar da girke sojoji a fadin kasar domin fuskantar duk wani hari daga kasar Amurka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ana Samun Kwararar ‘Yan Hijira Daga Mali Zuwa Kasar Cote De Voire November 14, 2025 Adadin Ma’adanin “Colbat” Da DRC Ta Bai Wa Duniya Ya Kai Ton 1,000 November 14, 2025 Unrwa: Fiye Da Gidaje 282,000 “Isra’ila” Ta Rusa A Gaza November 14, 2025 Limamin Juma’a Ya Bukaci Ganin An Kai Karar Donald Trump A Kotunan Duniya November 14, 2025 Iran ce ta farko wajen fitar da dabino a duniya November 14, 2025 Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza November 14, 2025 Kwamitin Tsaro ya tsawaita wa’adin aikin tawagar MDD a Afrika ta Tsakiya November 14, 2025 Tehran da Ankara sun jaddada muhimmancin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin November 14, 2025 Iran ta yi tir da G7 kan goyon bayan takunkuman Amurka November 14, 2025 Iran da China na bunkasa alakoki da hadin gwiwa a tsakaninsu November 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik Badruddeen Huthi ya bayyana cewa dole ne musulman kasar Yemen maza da mata sun bi tafarkin addinin musulunci na kaiwa ga daukaka idan suna son daukaka.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran nakalto Al-Huthi yana fadar haka a jiya Laraba da yamma a lokacinda yake magana kan zagayowar ranar haihuwar Fatimah Azzahra diyar manzon Allah (s).
Malamin ya kara da cewa, Fatimah (a) abin koikoyo ne ga dukkan musulmi maza da mata a sanin Allah da halaye masu kyau don samun kusance ga Allah madaukakin sarki.
Al-Huthi ya kara da cewa a halin yanzu musulmi a ko ina suke a duniya suna fuskantar matsaloli, musamman musulman kasar Falasdinu wadanda HKI ta kashe dubban mutane daga cikinsu a cikin yan shekaru da suka gabata. Sun kashe mata da maza yara kanana hatta wadanda suke cikin iyayensu basu barsu ba.
Ya ce mafita ga musulmi itq ce koyi da iyalan gidan manzon Allah (s) musamman Fatima (a) don samun guzurin samun karfin fuskantar makiya a ko ina suke.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD December 10, 2025 Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa. December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci