Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya
Published: 13th, November 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya karfafawa matasa masanan harkokin kasar Sin gwiwar zama manzonni domin inganta fahimtar juna tsakanin al’ummomin Sin da na sauran sassan duniya. Xi ya bayyana haka ne cikin amsar wasikar matasa masanan harkokin Sin 61 daga kasashe 51, wadanda za su halarci babban taron duniya kan harshen Sinanci da za a yi daga gobe Juma’a zuwa Lahadi, a birnin Beijing.
Xi Jinping ya bayyana farin cikin cewa ba Sinanci da al’adun Sin kadai wadanan matasa ke kauna ba, har da inganta fahimta game da harkokin Sin da koyi da juna tsakanin al’ummomi.
Ya kuma karfafa musu gwiwar ci gaba da gabatar da ainihin kasar Sin daga bangarori daban daban ga sassan duniya, tare da bayar da gudunmuwar hikima da karfin gina al’umma mai makoma ta bai daya ga dukkanin bil adama. (Mai fassara: FMM)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
Ban da wannan kuma, game da batun cewa kasashen kungiyar EU suna shirin cire na’urorin kamfanonin sadarwa na kasar Sin, Lin Jian ya bayyana cewa, kamfanonin kasar Sin suna aiwatar da ayyukansu bisa doka a nahiyar Turai na dogon lokaci, wadanda suka samar da kayayyaki da hidimomi masu inganci ga jama’ar Turai, tare da samar da muhimmiyar gudummawa wajen raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma da samar da ayyukan yi a nahiyar. Kasar Sin ta kalubalanci kungiyar EU da ta samar da yanayin gudanar da ciniki cikin adalci da rashin nuna bambanci ga kamfanonin kasar Sin don magance wargaza amannar da kamfanonin suka yi wa nahiyar Turai kan zuba jari. (Zainab Zhang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA