Kano Ta Kaddamar da Kwamitin Jagoranci Don Shirin Tarayyar Turai na Ilimi da Ƙarfafa Matasa
Published: 12th, November 2025 GMT
Daga Khadijah Aliyu
Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da Kwamitin Jagorancin Shirin Ilimi da Ƙarfafa Matasa a Arewa maso Yammacin Najeriya (EYEPINN) wanda kungiyar Tarayyar Turai ke daukar nauyinsa domin fadada damar samun ingantaccen ilimi da kuma karfafa gwiwar matasa a yankin.
An gudanar da bikin kaddamarwar ne a Kano, karkashin jagorancin Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda.
Yayin jawabinsa, Dakta Makoda ya bayyana shirin EYEPINN a matsayin “Alƙawari mai Manufa”, yana mai cewa manufar shirin ita ce cike gibi a fannin ilimi, karfafa haɗin kai, da kuma baiwa matasa kwarewar da ta dace domin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a jihar.
Ya ce sabon kwamitin da aka kaddamar zai yi jagoranci kan dabaru, tsare-tsare, kulawa da tabbatar da gaskiya da inganci wajen aiwatar da ayyukan EYEPINN a fadin Kano.
Dakta Makoda ya kara da cewa, mambobin kwamitin sun haɗa da wakilai daga ma’aikatun gwamnati, hukumomi da cibiyoyi masu ruwa da tsaki, abokan hulɗa, da kuma wakilan Tarayyar Turai.
A yayin taron, abokan hulɗa ciki har da UNICEF, PLAN International, UNESCO, da kuma sashen nazari na ci gaban duniya (DIME) na Bankin Duniya, sun gabatar da jawabai da suka fayyace manufofi, da sakamakon da ake sa ran samu, da tsarin haɗin gwiwa, domin ƙarfafa tsarin samar da ilimi da kuma ƙarfafa matasa a Kano da ma yankin Arewa maso Yamma baki daya.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Tarayya Turai
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfado Da Filin Jirgin Sama Na Kano
Shugaban Hukumar Gudanarwa Filayen Jiragen Sama ta Kasa (FAAN), Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya sake tabbatar da kudirin Gwamnatin Tarayya na dawo da tsohon martabar Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano.
Dakta Ganduje ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar duba aiki da ya kai filin jirgin a Kano.
Ya jagoranci wata tawaga mai ƙarfi ta jami’an FAAN domin tantance halin da filin jirgin yake ciki yanzu, ciki har da ayyukan da ake gudanarwa da kuma waɗanda aka bari da nufin samar da cikakken tsari na zamani da dorewar ci gaba.
Ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin tsofaffin filayen jiragen sama masu tarihi a Najeriya da yankin Yammacin Afirka, wanda a da yake ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin tashi da saukar jirage da ke haɗa Najeriya da sauran sassan duniya.
“Mun zo ne mu gani da idonmu, tsoffin ayyuka da sababbi, domin mu tsara sabuwar hanya ta farfado da wannan fili tare da dawo da matsayinsa cikin fitattun filayen jiragen sama na yankin,” in ji Ganduje.
Ya jaddada cewa hukumar FAAN za ta tabbatar da inganta jin daɗin fasinjoji, kiyaye ƙa’idodin tsaro, da kuma haɓaka ingancin aiki bisa ka’idodin ƙasa da ƙasa.
Dakta Ganduje ya tabbatar da cewa abubuwan da tawagar ta gano a yayin ziyarar za su zama ginshiƙi wajen tsara sabuwar manuniya ta dabarun sake farfado da filin domin ya zama abin koyi a harkar gudanar da filayen jiragen sama da kuma abin ƙarfafa tattalin arzikin Arewa.
Tawagar ta ziyarci sassa daban-daban na filin jirgin, ciki har da zauren sauka da tashin fasinjoji, hanyar tashi da saukar jirage, da kuma rukunin jigilar kaya, domin gano wuraren da ake bukatar gaggawar gyara.
ABDULLAHI JALALUDDEEN, Kano.