A cewar sanarwar, AIHS za ta taimaka wajen haɓaka tambarin dangote da haɓaka dabarun haɗin gwiwa tare da masu ruwa da tsaki.

Kodinetan shirin Barista Festus Adebayo ya shaida wa manema labarai cewa, za a iya cike giɓin gidaje a ƙasar ta hanyar haɗin gwiwar Haɗin kan Jama’a masu zaman kansu (PPP).

Ya ce: “Kwarewa da haɗin gwiwa su ne manyan abubuwan da muka a gaba, idan aka yi la’akari da saurin ci gaban fasaha a cikin gine-ginen gidaje, samar da kudaɗe da kuma inganta tsarin.

Ya ce taken taron na wannan shekara, Maimaita Gidaje Ta Hanyar Sabuntawa, wanda daidai yake da ainihin darajar kamfanin.

Barista Adebayo ya ce yana da ƙwarin gwiwar cewa haɗin gwiwa da kamfanin Simintin dangote zai taimaka wajen magance matsalar ƙarancin gidaje a ƙasar.

Ya ce sama da kashi 82 cikin 100 na mahalartan suna riƙe da matsayi na yanke shawara, tare da tabbatar da masu hulda kai tsaye tare da mutanen da ke da ikon saye.

Idan dai za a iya tunawa, Cibiyar Gine-gine ta Nijeriya (NIOB) da masu ruwa da tsaki a harkar gidaje sun bayyana kamfanin dangote a matsayin daya daga cikin manyan hanyoyin bunƙasa gidaje a Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Bayan shekar 22 da kuɓutar da Nijeriya daga mulkin soja, dimokuraɗiyya na ci gaba da fama da rauni mai tsanani. Alamun cutar sun bayyana ne a cinikin baragurbin wakilai (delegates), amfani da kuɗin ƙasa da aka wawure ta hanyar haram wajen gudanar da yaƙin neman zaɓe, maƙudan kuɗin da ake ware wa Hukumar Zaɓe ta ƙasa (INEC), ƙarancin yawan masu kada ƙuri’a, sayen ƙuri’u a bainar jama’a, tashin hankali yayin zaɓe, da kuma yaɗuwar fargaba, musamman a tsakanin matasa, cin amana na ƴan siyasa, canja sheƙa da zaɓaɓɓu ke yi, da dai sauran makamantansu.                                       

Asalin matsalar ita ce, rashin shiga cikin gudanar da gwamnati a siyasance (eɗclusion) na masu gaskiya da riƙon amana, matasa, mata, masu fama da naƙasa, ƴan gudun hijira da jam’iyyun da ke da ƙaramin ƙarfi, duk sun kasance a wajen filin. 

Wannan ba kawai rashin adalci ba ne, har ma ya saɓa wa kundin tsarin mulki, kuma barazana ce ga zaman lafiya da ci gaban ƙasa. Idan ka duba, za ka fahimci cewa; dimokuraɗiyyarmu na hannun wasu tsirarun mutane da shugabannin jam’iyyu masu ƙarfi, wadanda suka killace matasa da sauran ƴan Nijeriya daga samun damar shiga siyasa ko a saurare su ko la’akari da tasu gudunmawar. ɗimokuraɗiyyar cikin gida a jam’iyyu, abin dariya ne kawai, domin an mayar da zaɓe na cikin gida zuwa ciniki, wato ba ni kuɗi ga ƙuri’a. Inda a wani ɓangaren kuma, INEC na fuskantar ƙalubalen rashin ƴanci da rashin ƙwarin guiwar aiwatar da dokokinta. 

Har ila yau, ƴan gudun hijira da sauran al’umma masu rinjaye ana ci gaba da ware su daga zaɓe. Haka nan, hukumar zaɓen jihohi, musamman yadda aka gani a zaɓen ƙananan hukumomi a Kaduna da Bauchi, sun zama wani kwafi da ya ci mutuncin dimokuraɗiyya. Wannan ya saɓa wa sassa da dama na Kundin Tsarin Mulki na 1999 (Sashe 14(2)(a), 15(1), 40, 153(1)(f), 221, 318(1), da Jadawali na Bakwai), da ɗokokin ƙungiyar Tarayyar Afirka da kuma Majalisar ɗinkin ɗuniya.   

Yadda Wannan Tsari Na Matasa Zai Taimaka Wajen Ceto Siyasarmu:

1-Yarjejeniya Ta ƙasa ɗon Siyasa Mai Inganci (National Charter for Inclusion): A samar da wata Yarjejeniya ta haɗin gwiwa tsakanin Ma’aikatar Matasa ta ƙasa, ƙungiyar Gamayyan Jamíyyun Siyasa (IPAC), Hukumar Zaɓe ta ƙasa (INEC), ƙungiyoyin Fararen Hula da Majalisar Matasa ta Nijeriya. Wannan yarjejeniya za ta kafa ƙa’idoji da dokokin da za su tilasta dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyu, tabbatar da adalci wajen zaɓuɓɓuka da kuma bai wa dukkannin jam’iyyun da suka shiga zaɓe damar ba da gudunmuwa wajen shugabanci a kowane mataki da kuma bai wa matasa, mata, ƴan gudun hijira da kowa da kowa damar ƴancin tsayawa takara cikin adalci.  

2- Sauyi Mai Zurfi Ga Jam’iyyu da Tsarin Zaɓe:

Ya zama wajibi jam’iyyu su buɗe ƙofa. A kafa dokar da za ta tilasta duk mai son tsayawa takara gabatar da “Tsarin Ayyuka” (Project Plans) kafin hawa kujera, sannan ya fitar da “Rahoton ƙarshe” (End-of-Term Reports), bayan barin gado ko da kuwa zai koma kuwa. A daƙile kuɗin da ake nema marasa tushe daga masu neman takara, musamman na hukumomin zaɓen jihohi, (Misalin KAɗ-SIECOM). A tabbatar da cikakken amfani da Sashe na 7 na Kundin Tsarin Mulki da ɗokar Zaɓe ta 2022.   

3- Runguman ɗimokuraɗiyyar ɗijital Hannu Biyu (ɗigital ɗemocracy)

A kafa “Cibiyar ɗimokuraɗiyyar ɗijital ta ƙasa (NɗɗH)” da za ta sa ido, bayar da rahoto kai tsaye, sa ido kan kuɗin yaƙin neman zaɓe da tantance tsarin jam’iyyu. Za ta kuma ba da damar samun ilimin siyasa ta hanyar wasanni da fasahar zamani domin ƙara fahimta, rage rashin sha’awa daga matasa, da bunƙasa ilimi da riƙon amana. 

4- Ƙarfafa IPAC Youth da Shirye-shiryen Fadakarwa

A ƙarfafa ɓangaren Matasa na IPAC (IPAC Youth ɗirectorate) daga matakin ƙasa har zuwa jihohi, ta hanyar samar da doka, kasafin kuɗi da kuma tsarin aiki. Sannan, a ɗora musu alhakin wayar da kan jama’a a faɗin ƙasar nan, musamman a tsakanin wadanda aka ware daga siyasa. 

Me Za Mu Samu Idan An Bi Wannan Hanya? Za mu samu dimokuraɗiyya mai inganci da kuma tsabta, inda matasa, mata, masu fama da nakasa (PWɗs) da ƴan gudun hijira (IɗPs) za su samu bakin fada kuma a ji a cikin siyasa da shugabanci. Za a samu ƙarancin tashin hankali a lokacin zaɓe, raguwar sayen ƙuri’a da ingantaccen ilimi da wayewa a tsakanin jama’a.  Za kuma a samu jam’iyyu masu gaskiya da amana da kuma shugabanci na ƙwarai da ci gaban ƙasarmu Nijeriya. 

Matakan Aiwanar da Wannan Tsari: 

Mataki na 1:

Rubuta NSPPC tare da dukkan masu ruwa da tsaki.

Mataki na 2: Kafa tsarin dubawa tsakanin INEC, IPAC da CSO.

Mataki na 3: ƙaddamar da NɗɗH da kayan aikin ilmantarwa.

Mataki na 4: Gyaran ɗokar Zaɓe, domin shigar da wadanan al‘amura da muka gabatar a sama da sauran buƙatu. 

Kafin Mu Kammala: Makomar dimokuraɗiyyar Nijeriya na cikin hadari. Ba za mu iya ci gaba da kallon halin da ake ciki ba na rashin adalci, cin amana, zangon ƙasa ga ƙasa da al’úmarta. 

Yazama wajibi mu yi amfani da ƙarfin matasa, domin ceto Nijeriya daga bakin kuraye. ƙirƙire-ƙirƙire da buƙatar riƙon amana, su ne maganin cutar da dimokuraɗiyyarmu ke fama da ita. 

Wannan tsari nawa na zuwa ne daga gwanancewa da aiki da IPAC, shirye-shiyen fitar da saƙwanni ta ‘Bakondare Speaks’, wallafa rubuce-rubuce a manyan jaridu kamar su Premium Times, daily Trust, Guardian, Punch, Vanguard, Thisday , Leadership (A hausance da turanci)) da kuma shiga ayyukan siyasa masu tsafta da kuma alaƙa da ƙungiyoyi masu muhimmanci na siyasa.   

Yanzu ne lokacin sauyi! Muryar matasa ya kamata ta koma tsakiya wajen tsara manufofi da aiwatar da su. Yakamata dimokuraɗiyyar Nijeriya ta amfani kowa da kowa ba wasu ba kawai! 

Kafin rahoton ƙarshe na wannan taro ya isa ofishin Shugaban ƙasa ranar 12 ga Agusta, 2025 (Ranar Matasa ta ɗuniya), ina kira da babbar murya da fatan alheri ga duk dan Nijeriya da kuma dukkan wakilai da su rungumi wannan tsari. Ina kuma kira ga ƴan majalisa da masu zartarwa da su aiwatar da shi, domin ci gaban Nijeriya da kuma amfanin masu zuwa nan gaba. Yanzu ne lokacin daukar mataki na haƙiƙa da Jarumta! Allah ya yi mana albarka, ameen.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta
  • Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba
  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN