Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5
Published: 3rd, August 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da babban shirin dashen bishiyoyi miliyan biyar a shekarar 2025.
An fara dashen ne yankin Yanbawa da ke Ƙaramar Hukumar Makoda.
Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin GudiGwamnan ya ce wannan shiri na nufin yaƙi da sauyin yanayi, farfaɗo da ƙasar da ta lalace, da kuma kare muhalli.
Ya ce an fara dashen bishiyoyin a wannan fili tun shekarar 1972, amma aka bari ya lalace.
Yanzu gwamnatinsa ta gyara shi don ya taimaka wajen shawo kan matsalolin fari da sauyin yanayi.
Ya ƙara da cewa wannan shiri yana daga cikin ayyukan muhalli da gwamnatinsa ta aiwatar cikin shekara guda.
Ayyukan sun haɗa da gyaran gonakin dasa itatuwa a Garun Malam da Garko, waɗanda yanzu suke samar da dubban ƙananan itatuwa da ake rabawa a Kananan Hukumomin 44 na jihar.
Ya ce tuni aka farfaɗo da sama da hekta 200,000 na ƙasa da ta lalace.
Hakazalika, ya ce an samar da wata gona mai hekta 100 domin koya wa manoma dabarun noman itatuwa da kayan gona.
Gwamnan, ya bayyana cewa suna haɗin gwiwa da Ƙungiyar Abinci da Aikin Gona ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO), don koyar da yadda ake amfani da ƙasa yadda ya kamata da kula da muhalli.
Ya ce sun kuma fara shirye-shiryen ilmantar da makarantu da al’umma game da sauyin yanayi da muhimmancin kula da muhalli.
Don ɗorewar wannan shiri, gwamnan ya ce an kafa dokar sauyin yanayi da tsarin aiki a Jihar Kano, wanda ya sanya mata hannu.
Haka kuma an kafa ɗakin gwajin gurɓacewar iska da ruwa a Jami’ar Northwest don binciken muhalli.
Ya ce yanzu haka suna fitar da rahotannin lafiyar iska da ruwa a kowane mako daga sabon ɗakin binciken.
Wannan ya nuna cewa gwamnatin tana amfani da kimiyya da bayanai wajen yaƙi da sauyin yanayi.
Gwamnatin ta sake ɗaukar masu tsaron daji, tare da biyansu albashi, sannan ta ɗauki sabbin ma’aikata don kare dazuka a faɗin jihar.
“Dukkanin itacen da muka dasa dole ne ya girma,” in ji gwamnan.
“Shi ya sa muke gina ƙwararrun cibiyoyi da tsarin lura da yadda shirin ke tafiya.”
Za a raba itatuwan a makarantu, wuraren ibada, gonaki, gidaje, wuraren jama’a, da kuma gefen tituna a cikin gari da karkara.
Gwamnan, ya umarci shugabannin Ƙananan Hukumomi 44 su ɗauki shirin da muhimmanci, su tabbatar da gaskiya wajen raba itatuwan.
“Yanzu ne lokacin da ya dace mu dakatar da yaɗuwar hamada, mu yaƙi sauyin yanayi, da hana zaizayar ƙasa.
“Mu daina sare itatuwa ba tare da tunani ba. Kowa ya dasa, ya kula, kuma ya kare itatuwa don kare ƙasarmu da makomar ’ya’yanmu,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga shugabannin gargajiya, matasa, ƙungiyoyi, makarantu da kasuwanni su haɗa kai wajen samar da kyakkyawan muhalli a Kano.
“A yau ne muka ɗauki alhakin gyara ƙasarmu. Allah Ya taimake mu a wannan aikin alheri,” a cewarsa.
Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Muhammad Dahiru Hashim, ya ce wannan shiri na dasa itatuwa ya nuna irin jajircewar Gwamnan wajen kare muhalli.
Ya bayyana cewa shekara guda da ta wuce, suka fara shirin dasa itatuwa miliyan uku.
Wannan sabon shirin ya ƙara faɗaɗa, kuma an yi amfani da itatuwan da aka noma a cikin jihar.
Ya ce an sake farfaɗo da gonakin gwamnati da ke Gwale da Gwarzo, waɗanda yanzu ke samar da itatuwa don ɗorewar wannan shiri.
Ya ƙara da cewa tun da farko Gwamna Abba, ya nuna irin ƙwarewarsa wajen kare muhalli.
Aikin farko da ya halarta bayan ya hau mulki shi ne bikin Ranar Muhalli ta Duniya ta 2023, wanda ya nuna wa jama’a cewa gwamnatinsa na ɗaukar sauyin yanayi da muhimmanci.
“Jihar Kano ba kawai tana dasa itatuwa ba ne. Muna gyara muhalli, muna tsaftace iska, kuma muna dakatar da yaɗuwar hamada.
“Wannan shiri yana nuna sauyi, da kuma makomarmu,” in ji shi.
Ya kuma yaba wa ma’aikatan ma’aikatar muhalli, shugabannin gargajiya, saboda irin goyon bayan da suka bayar don nasarar wannan shiri.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Abba Kabir Yusuf gwamnati da sauyin yanayi dasa itatuwa wannan shiri
এছাড়াও পড়ুন:
Zulum zai mayar da ’yan gudun hijira 5,000 Bama
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce gwamnatinsa na shirin mayar da mutum 5,000 gida daga sansanin ‘yan gudun hijira kafin wucewar damina domin su samu damar yin noma.
Mutanen za su fito ne daga garuruwan Goniri, Bula Kuriye, Mayanti, Abbaram, da Darajamal.
Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a NejaGwamnan, ya bayyana hakan ne lokacin da ya kai wa Mai Martaba Shehun Bama, Dakta Umar ibn Kyari Umar El-Kanemi, ziyara a fadarsa da ke Bama.
Ya ce an riga an kammala gina matsuguni 1,000 a Darajamal, sannan kuma aikin gina wasu a sauran garuruwan hudu.
“Mun ƙudiri aniyar dawo da ‘yan gudun hijira gida. A Mayanti, Goniri, Bula Kuriye da Abbaram muna gina gidaje, na Darajamal kuma an riga an gama,” in ji Gwamnan.
Ya ƙara da cewa gwamnati za ta kewaye yankunan da rami domin inganta tsaro.
Zulum, ya jaddada muhimmancin noma a rayuwar al’umma.
“Muna so mutanen da za a dawo da su gida su samu damar yin noma, saboda noma shi ne abin dogaron rayuwa a Borno,” in ji shi.
Ya ce zai gana da shugabannin JTF da Civilian JTF domin tsara yadda za a kare lafiyar manoma da gonaki.
Haka kuma, Zulum ya shaida wa Shehun Bama cewa gwamnatinsa ta ƙara tsaurara tsaro a garin Nguro Soye, domin samun damar yin noma.
“Daga dawowa daga Gwoza, na tsaya a sansanin sojoji da ke kusa da Banki, inda muka tattauna yadda za a tsaurara tsaro a Nguro Soye. Na bai wa sojoji da Civilian JTF kayan aiki kuma na yi alƙawarin biyan ‘yan sa-kai da ke sintiri alawus ɗin watanni shida da suka wuce,” in ji Gwamnan.
A nasa ɓangaren, Mai Martaba Shehun Bama ya yaba wa Zulum bisa ƙoƙarinsa na kyautata tsaro da jin daɗin jama’a.
“Ina yi wa gwamna godiya saboda dawo da mutanen Darajamal gida. Muna fatan sauran mutane ma za su dawo gida cikin kwanciyar hankali,” in ji Shehun.
Shehun, ya kuma roƙi gwamnatin da ta ƙara tallafa wa Civilian JTF domin kare manoma da gonaki a lokacin damina.