Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5
Published: 3rd, August 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da babban shirin dashen bishiyoyi miliyan biyar a shekarar 2025.
An fara dashen ne yankin Yanbawa da ke Ƙaramar Hukumar Makoda.
Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin GudiGwamnan ya ce wannan shiri na nufin yaƙi da sauyin yanayi, farfaɗo da ƙasar da ta lalace, da kuma kare muhalli.
Ya ce an fara dashen bishiyoyin a wannan fili tun shekarar 1972, amma aka bari ya lalace.
Yanzu gwamnatinsa ta gyara shi don ya taimaka wajen shawo kan matsalolin fari da sauyin yanayi.
Ya ƙara da cewa wannan shiri yana daga cikin ayyukan muhalli da gwamnatinsa ta aiwatar cikin shekara guda.
Ayyukan sun haɗa da gyaran gonakin dasa itatuwa a Garun Malam da Garko, waɗanda yanzu suke samar da dubban ƙananan itatuwa da ake rabawa a Kananan Hukumomin 44 na jihar.
Ya ce tuni aka farfaɗo da sama da hekta 200,000 na ƙasa da ta lalace.
Hakazalika, ya ce an samar da wata gona mai hekta 100 domin koya wa manoma dabarun noman itatuwa da kayan gona.
Gwamnan, ya bayyana cewa suna haɗin gwiwa da Ƙungiyar Abinci da Aikin Gona ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO), don koyar da yadda ake amfani da ƙasa yadda ya kamata da kula da muhalli.
Ya ce sun kuma fara shirye-shiryen ilmantar da makarantu da al’umma game da sauyin yanayi da muhimmancin kula da muhalli.
Don ɗorewar wannan shiri, gwamnan ya ce an kafa dokar sauyin yanayi da tsarin aiki a Jihar Kano, wanda ya sanya mata hannu.
Haka kuma an kafa ɗakin gwajin gurɓacewar iska da ruwa a Jami’ar Northwest don binciken muhalli.
Ya ce yanzu haka suna fitar da rahotannin lafiyar iska da ruwa a kowane mako daga sabon ɗakin binciken.
Wannan ya nuna cewa gwamnatin tana amfani da kimiyya da bayanai wajen yaƙi da sauyin yanayi.
Gwamnatin ta sake ɗaukar masu tsaron daji, tare da biyansu albashi, sannan ta ɗauki sabbin ma’aikata don kare dazuka a faɗin jihar.
“Dukkanin itacen da muka dasa dole ne ya girma,” in ji gwamnan.
“Shi ya sa muke gina ƙwararrun cibiyoyi da tsarin lura da yadda shirin ke tafiya.”
Za a raba itatuwan a makarantu, wuraren ibada, gonaki, gidaje, wuraren jama’a, da kuma gefen tituna a cikin gari da karkara.
Gwamnan, ya umarci shugabannin Ƙananan Hukumomi 44 su ɗauki shirin da muhimmanci, su tabbatar da gaskiya wajen raba itatuwan.
“Yanzu ne lokacin da ya dace mu dakatar da yaɗuwar hamada, mu yaƙi sauyin yanayi, da hana zaizayar ƙasa.
“Mu daina sare itatuwa ba tare da tunani ba. Kowa ya dasa, ya kula, kuma ya kare itatuwa don kare ƙasarmu da makomar ’ya’yanmu,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga shugabannin gargajiya, matasa, ƙungiyoyi, makarantu da kasuwanni su haɗa kai wajen samar da kyakkyawan muhalli a Kano.
“A yau ne muka ɗauki alhakin gyara ƙasarmu. Allah Ya taimake mu a wannan aikin alheri,” a cewarsa.
Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Muhammad Dahiru Hashim, ya ce wannan shiri na dasa itatuwa ya nuna irin jajircewar Gwamnan wajen kare muhalli.
Ya bayyana cewa shekara guda da ta wuce, suka fara shirin dasa itatuwa miliyan uku.
Wannan sabon shirin ya ƙara faɗaɗa, kuma an yi amfani da itatuwan da aka noma a cikin jihar.
Ya ce an sake farfaɗo da gonakin gwamnati da ke Gwale da Gwarzo, waɗanda yanzu ke samar da itatuwa don ɗorewar wannan shiri.
Ya ƙara da cewa tun da farko Gwamna Abba, ya nuna irin ƙwarewarsa wajen kare muhalli.
Aikin farko da ya halarta bayan ya hau mulki shi ne bikin Ranar Muhalli ta Duniya ta 2023, wanda ya nuna wa jama’a cewa gwamnatinsa na ɗaukar sauyin yanayi da muhimmanci.
“Jihar Kano ba kawai tana dasa itatuwa ba ne. Muna gyara muhalli, muna tsaftace iska, kuma muna dakatar da yaɗuwar hamada.
“Wannan shiri yana nuna sauyi, da kuma makomarmu,” in ji shi.
Ya kuma yaba wa ma’aikatan ma’aikatar muhalli, shugabannin gargajiya, saboda irin goyon bayan da suka bayar don nasarar wannan shiri.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Abba Kabir Yusuf gwamnati da sauyin yanayi dasa itatuwa wannan shiri
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027.
Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta.
Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo“Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna cewa ba sa son a samu hamayya a lokacin zaɓe,” in ji shi.
Galadima ya kuma yi gargadi kan shirin nada wani da ya kira mai lam’a a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin rudani.
“Ina fatan ba gaskiya ba ne, domin idan wannan mutumin ya zama shugaban INEC, ka tabbata cewa wannan gwamnati na neman tayar da yaƙin basasa,” in ji shi.
Sai dai bai ambaci sunan mutumin ba.
Dangane da batun fara yaƙin neman zaɓe da wuri da wasu jam’iyyu ke yi, Buba Galadima ya zargi INEC da gazawa wajen aiwatar da tanade-tanaden dokokin zaɓe.
“Wannan batun fara yaƙin neman zaɓe kafin INEC ta ba da izini, gwamnatin da ke kan mulki ce ta fara shi. Wannan yana nuna cewa INEC ba za ta iya zama mai adalci a irin wannan yanayin siyasa da muke ciki ba,” in ji shi.