HausaTv:
2025-11-12@12:38:51 GMT

Gabon: An Daure Mata Da ‘Dan  Tsohon Shugaban Kasa Bongo Shekaru 20 A Gidan Yari

Published: 12th, November 2025 GMT

Matar tsohon shugaban kasar Gaba, Sylvia Bongo da kuma dansa Nuruddin Bongo za su yi zaman kaso na tsawon shekaru 20 saboda samunsu da laifin almubazzaranci da kudin kasa.

Kotun da ta yi shari’ar ta yanke hukunci ne akan iyalan tsohon shugaban kasar Ali Bongo  ba tare da suna gabanta ba. Kotun dai an kafa ne domin yin binciken laifuka da suke da alaka da barnata dukiyar kasa.

Kotun ta sami mai dakin tsohon shugaba Bongo, Sylvia Bongo Ondimba da laifin almundahana da dukiyar kasa da kuma yin takardu na jabu.

Shi kuwa  Nuruddin Bongo an same shi ne da laifukan da su ka hada da runton bai wa kai mukamai,wanke kudaden haram da mayar da su halaliya, sannan da shirya makarkashiya domin aikata laifuka.

Kowane daya daga cikinsu an kuma ci tararsu da kudin da sun kai saifa miliyan 100.

Dan shugaban kasar ta Gabon Nuruddin Bongo ya kore cewa ya yi almundahanar kudin kasar, kuma ya yi alkawalin ci gaba da kare hakkinsa har bayyanar gaskiya.

Mai shigar da kara na gwamnati ya bukaci ganin kotun ta musamman ta yanke wa Sylvia da Nuruddin hukuncin zaman kurkuku na shekaru 20, saboda daukar duniyar al’umma da mayar da ita ta kashin kai.

A 2023 ne dai aka yi juyin Mulki a kasar ta Gabon wanda ya kawo karshen mulkin iyalan Bongo na tsawon shekaru 55.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tanzania: MDD Ta Yi Kira Da A Yi Bincike Akan Daruruwan Mutanen Da Aka Kashe Sanadiyyar Rikcin Zabe November 12, 2025 Iran Ta Zama Memba A Kungiyar Tattara Bayanai Na  Ilimomi Da Kere-kere Ta Duniya ( ISKO) November 12, 2025 Iran: Ta’addanci barazana ce ga dukkan yankin November 12, 2025 Araghchi: Matsalar Yammacin duniya ita ce ci gaban kimiyyar Iran ba makaman nukiliya ba November 12, 2025 Sheikh Qassem: Kawar Da Hizbullah Ne Babban Burin Isra’ila A Lebanon November 12, 2025 Masar Da Sudan Sun Jaddada Wajabcin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yankin November 12, 2025 Venezuela: Maduro Ya Sanya Hannu Kan Dokar Tsaron Kasa Mai Cikakkiyar Kariya November 12, 2025 UNICEF: Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza November 12, 2025 Ministocin harkokin wajen kasashen yamma sun yi Allah wadai da ta’asar RSF a El Fasher Darfur November 11, 2025 Abdel-Aty: Diflomasiyya Ce Kawai Hanyar Da Maido Da Zaman Lafiya A Libya November 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Larijani : ‘babu wani sabon sako’ da muka aika wa Amurka

Shugaban  tsaron kasar ta Iran ya yi watsi da rahotannin da ake yayatawa cewa  iran ta bude wasu hanyoyin tuntuba da Washington, yana mai jaddada cewa ba a isar da wani sabon sako ga Amurka ba.

Ali Larijani ya jaddada cewa fifikon Iran a koyaushe shi ne dage takunkumin da aka kakaba mata, wanda ya bayyana a matsayin kokarin diflomasiyya na gwamnatin kasar.

Duk manufofin gwamnati da kokarin diflomasiyya suna mai da hankali ne kan kawo karshen takunkuman,” in ji shi.

Ya bayyana ce sakon da ake yayatawa ya samo asali ne daga shawarwarin da akayi a baya, amma Amurka ba ta nuna sha’awar cimma yarjejeniya ba.

Wannan bayanin ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da yayata cewa an bude wata hanyar tuntuba kai tsaye tsakanin Tehran da Washington kan batutuwan shirin nukiliyar Iran da na yanki.

Iran ta sha nanata cewa dage takunkumi shi ne ginshikin duk wani ci gaba na diflomasiyya, amma Amurka ta gaza nuna da gaske take don cimma yarjejeniya.

Iran da Amurka sun yi tattaunawa sau biyar a farkon wannan shekarar domin maye gurbin yarjejeniyar nukiliyar 2015.

Amma Amurka da Isra’ila sun kaddamar da hare-hare kan Iran na tsawon kwanaki 12 a jajibirin zagaye na shida, wanda ya kashe daruruwan mutane tare da lalata cibiyoyin soja da na nukiliya na Iran.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gaza : Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau 282 tun bayan aiwatar da ita November 11, 2025 Iraki : Ana zaben ‘yan majalisa don tsara makomar siyasar kasar November 11, 2025 Sudan ta soki shirun kasashen duniya game ta’asar dake faruwa a kasar November 11, 2025 Hamas ta soki kudurin Isra’ila na yin dokar hukuncin kisa kan laifin ta’addanci November 11, 2025 Iran Za Ta Harba Taurarin Dan Adam Guda Uku Zuwa Sararin Samaniya November 11, 2025 Lebanon: An Saki Hannibal Kaddafi Bayan Zaman Kaso Na Shekaru 10 November 11, 2025 An Sake Bude Gidajen Mai Da Makarantu Da Aka Rufe A Kasar Mali November 11, 2025 Trump Ya Yi Wa Ma’aikatan Filayen Jiragen Sama Barazana November 11, 2025 Donald Trump Na Amurka Ya Karbi Bakuncin Shugaban Rikon Kwaryar Kasar Syria Ahmad Shar November 11, 2025 Amnesty Ta Kira Yi Gwamnatin Najeriya Da Ta Wanke ‘Yan Ogoni 9 Da Aka Zartarwa Da Hukuncin Kisa Shekaru 30 A Baya November 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Venezuela: Maduro Ya Sanya Hannu Kan Dokar Tsaron Kasa Mai Cikakkiyar Kariya
  • Larijani : ‘babu wani sabon sako’ da muka aika wa Amurka
  • Iraki : Ana zaben ‘yan majalisa don tsara makomar siyasar kasar
  • Lebanon: An Saki Hannibal Kaddafi Bayan Zaman Kaso Na Shekaru 10
  • Wani mutum ya rasu a gidan karuwai bayan ziyartar ’yan mata
  • Donald Trump Na Amurka Ya Karbi Bakuncin Shugaban Rikon Kwaryar Kasar Syria Ahmad Shar
  • Amnesty Ta Kira Yi Gwamnatin Najeriya Da Ta Wanke ‘Yan Ogoni 9 Da Aka Zartarwa Da Hukuncin Kisa Shekaru 30 A Baya
  • Matar tsohon Shugaban Ƙasa Shagari ta rasu
  • ‘Yan Jarida 44 Ne Su Ka Yi Shahada A Sansanonin Hijira Na Gaza