Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba
Published: 3rd, August 2025 GMT
Rundunar Sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar DSS sun ceto Injiniya Joshua Saleh, wani malami a Jami’ar Taraba, wanda ’yan bindiga suka sace.
An sace malamin ne a ranar 31 ga watan Yuli, 2025, a hanyar Chinkai–Kente zuwa Wukari, da ke Ƙaramar Hukumar Wukari a Jihar Taraba.
Sai an samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu za mu ajiye makamai — Hamas An ƙara hakimai 6 a Masarautar KatsinaBayan samun sahihan bayanai, sojoji da DSS suka fara bincike tare da ƙoƙarin ceto shi a wurare da dama, ciki har da Kente, Sondi 1 da 2, Yaku, da Warawa.
A cewar Laftanar Umar Muhammed, mai magana da yawun rundunar, sojojin sun yi arangama da ’yan bindigar, inda suka yi musayar wuta.
’Yan bindigar sun gaza jure ruwan wutar da sojoji suka musu, wanda hakan ya sa suka tsere suka bar malamin.
Kwamandan Runduna ta 6, Brigediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba wa sojojin bisa ƙwarewar da suka nuna da kuma yadda suka haɗa kai da sauran jami’an tsaro wajen ceto malamin.
Janar Uwa, ya tabbatar wa jama’a cewa sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi da tabbatar da zaman lafiya a Jihar Taraba.
Ya kuma roƙi jama’a da su kasance masu lura tare da bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen yaƙi da miyagun laifuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa Kwanturola Janar na Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa, Bashir Adewale Adeniyi na ta shan suka daga mutane daban-daban.
Yayin da wasu ke ganin abin da shugaban ya yi da cewa ya dace, wasu kuwa na ganin hakan ya yi hannun riga ga tanade-tanaden kundin tsarin mulkin kasa.
Shin ko me dokar kasa ta ce game da wannan karin wa’adi da shugaban kasan ya yi?
NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aureWannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan