Aminiya:
2025-08-03@15:07:57 GMT

Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba

Published: 3rd, August 2025 GMT

Rundunar Sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar DSS sun ceto Injiniya Joshua Saleh, wani malami a Jami’ar Taraba, wanda ’yan bindiga suka sace.

An sace malamin ne a ranar 31 ga watan Yuli, 2025, a hanyar Chinkai–Kente zuwa Wukari, da ke Ƙaramar Hukumar Wukari a Jihar Taraba.

Sai an samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu za mu ajiye makamai — Hamas An ƙara hakimai 6 a Masarautar Katsina

Bayan samun sahihan bayanai, sojoji da DSS suka fara bincike tare da ƙoƙarin ceto shi a wurare da dama, ciki har da Kente, Sondi 1 da 2, Yaku, da Warawa.

A cewar Laftanar Umar Muhammed, mai magana da yawun rundunar, sojojin sun yi arangama da ’yan bindigar, inda suka yi musayar wuta.

’Yan bindigar sun gaza jure ruwan wutar da sojoji suka musu, wanda hakan ya sa suka tsere suka bar malamin.

Kwamandan Runduna ta 6, Brigediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba wa sojojin bisa ƙwarewar da suka nuna da kuma yadda suka haɗa kai da sauran jami’an tsaro wajen ceto malamin.

Janar Uwa, ya tabbatar wa jama’a cewa sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi da tabbatar da zaman lafiya a Jihar Taraba.

Ya kuma roƙi jama’a da su kasance masu lura tare da bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen yaƙi da miyagun laifuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa Kwanturola Janar na Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa, Bashir Adewale Adeniyi na ta shan suka daga mutane daban-daban.

Yayin da wasu ke ganin abin da shugaban ya yi da cewa ya dace, wasu kuwa na ganin hakan ya yi hannun riga ga tanade-tanaden kundin tsarin mulkin kasa.

Shin ko me dokar kasa ta ce game da wannan karin wa’adi da shugaban kasan ya yi?

NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa
  • An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba
  • Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta 
  • Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli
  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka