Leadership News Hausa:
2025-12-13@13:23:29 GMT

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Published: 12th, November 2025 GMT

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Ya ƙara da cewa rundunar ta samu nasarar ceto mutane 47 da aka yi garkuwa da su da kuma mutane 39 da aka ceto daga hannun masu safarar mutane, inda aka miƙa su ga iyalansu.

Kayan da aka ƙwato daga hannun waɗanda ake zargi sun haɗa da bindiga AK-47 guda ɗaya, bindiga ta gida guda ɗaya, alburusai 183, motoci uku, babur mai ƙafa uku da keke napep ɗaya, da kuma dabbobi sama da 200 na sata.

Haka kuma, ‘yansanda sun ƙwato tarin miyagun ƙwayoyi irin su Fentalin, Exol, Tramadol, da wiwi, tare da wayar wutar lantarki.

Abubakar ya sake tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da ƙoƙari wajen tabbatar da tsaro, inda ya ce, “Duk da waɗannan nasarori, har yanzu akwai aiki da yawa a gabanmu. Mun ƙuduri aniyar ƙara ƙoƙari.”

Ya gode wa Sufeton ‘Yansanda na Ƙasa, Kayode Egbetokun, da Gwamnatin Jihar Katsina bisa goyon bayansu, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai da za su taimaka wajen hana aikata laifuka.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa November 12, 2025 Manyan Labarai Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna November 12, 2025 Manyan Labarai Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba November 12, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Waiwaye Adon Tafiya: Manyan Nasarorin Da Aka Cimma A Dangantakar Kasashen Afirka Da Sin A 2025

A ci gaba da al’adar fiye da shekaru 30, Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi ya ziyarci kasashen Afirka da dama a tsakanin 5-11 ga watan Janairun 2025 don sake tabbatar da dangantakar diflomasiyya da kuma binciko sabbin hanyoyin hadin gwiwa. Wannan ziyarar ta sake tabbatar da manufar ci gaba da cin moriyar juna a tsakanin bangarorin biyu.

 

Baje kolin tattalin arziki da ciniki na Sin da Afirka na hudu a Changsha

An gudanar da wannan taron baje kolin na hudu daga 12 zuwa 15 ga watan Yunin bana a Changsha, babban birnin lardin Hunan. Baje kolin ya tattaro kusan kamfanonin Sin da Afirka 4,700, kuma an baje kolin kayayyakin Afirka sama da 800 daga kasashe da dama.

An gudanar da taron ne tare da bikin cika shekaru 25 na taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC), wanda hakan ke jaddada tsarin ci gaba na dogon lokaci na ci gaba da huldar Sin da Afirka.

 

Fadada ciniki da katse shingen haraji zuwa sifili ga kasashen Afirka

A shekarar 2025, cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka ta ci gaba da bunkasa sosai, cinikayyar Sin da Afirka a cikin watanni biyar na farko bayan katse shingen haraji ta karu da kashi 12.4% a shekara. Sin ta dakatar da haraji kashi 100 bisa 100 ga dukkan kasashen Afirka 53 wadanda suke da huldar diflomasiyya da kasar. Wannan manufar ta rage shingen ciniki sosai kuma ta inganta damar shiga kasuwa da fitar da kayayyaki daga Afirka. Wannan fadada manufofin ciniki ya nuna yadda aka sauya tsarin yarjejeniyar cinikayya daga yarjejeniya ta dan wani lokaci daya ko mai iyaka zuwa hadewar kasuwa mafi tsari kuma ta dogon lokaci.

 

Mu’amalar jama’a, al’adu, ilimi da bude ido

Tattaunawar Jama’a da Jama’a ta Afirka da Sin wacce ta gudana a watan Mayu na 2025 a Lusaka, Zambia, ta tattaro kungiyoyin jama’a, shugabannin kasuwanci, ‘yan kasuwa, da masu tsara manufofi daga Afirka da Sin. Ta jaddada hadin gwiwa tsakanin al’ummar bangarorin biyu fiye da yadda bangare daya kacal ke mu’amalarsa.

A irin wannan tattaunawar ta hadin gwiwa da ta gudana a wani taron hadin gwiwa na 2025 a birnin Jinhua na lardin Zhejiang, an sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyi 33, wadanda suka shafi ciniki, saka hannun jari na kasashen waje, kwangilar injiniyanci, gina rumbunan ajiya a kasashen waje, wadanda darajarsu ta kai yuan biliyan 40.11 (kimanin dalar Amurka biliyan 5.63).

Bayan kasuwanci, taron Jinhua ya hada da musayar al’adu da yawon bude ido, inda aka gudanar da bikin baje kolin al’adu da yawon bude ido na Afirka na farko.

 

Hadin gwiwar kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire da hukumar tarayyar Afirka

A watan Satumba na 2025, Hukumar Tarayyar Afirka (AUC) da Ma’aikatar Kimiyya da Fasaha ta Sin sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna don zurfafa hadin gwiwa a fannin kimiyya da fasaha. Daga 19-21 ga watan Nuwamban 2025 kuma, an gudanar da taron hadin gwiwa kan ci gaban kirkire-kirkire na Sin da Afrika a birnin Wuhan, da nufin daidaita hadin gwiwar kimiyya da fasaha kan bukatun ci gaban Afirka, ciki har da makamashi mara cutar da muhalli (green energy), biranen kimiyya, ci gaba mai dorewa, da sauransu.

 

Hadin gwiwar fasaha a ɓangaren kula da muhalli

Cibiyar Hadaka ta Sin da Afirka mai Amfani da Tauraron Dan Adam (CACSA), ta fadada hadin gwiwarta da Afirka a shekarar 2025. Tun kafuwarta a shekarar 2023, ta rattaba hannu kan wasu yarjejeniyoyi da kasashen Afirka 16, inda ta kafa na’urori 14 na kula da sararin samaniya masu amfani da tauraron dan adam wadanda ke tallafawa sama da hotuna 70,000 masu inganci daga hangen nesa. Wannan yana tallafawa tsare-tsaren birane, sa ido kan yadda ake amfani da kasa, kula da tekuna ko koguna, sa ido kan muhalli, da sauransu.

Ta hanyar shirye-shirye a fannin kimiyya, samar da makamashi mara cutarwa ga muhalli, da kayayyakin more rayuwa na dijital, Sin da Afirka suna zurfafa hadin gwiwa ba wai kawai a fannin kayayyakin more rayuwa da aka fi sani kamar hanyoyi, layin dogo, tashoshin jiragen ruwa ba, har ma a fannoni masu muhimmanci na “zamani” da karni na 21 ke bukata don ci gaba.

 

Masu karatu, mu tambayi kanmu mana, me wannan gagaruman sabbin nasararorin hadin gwiwar Afirka da Sin ke nufi a nan gaba?

Daga cinikayya, da samar da ababen more rayuwa zuwa hadin gwiwa na dabarun fasaha da zamantakewa ta zamani da suka hada da kimiyya da fasaha, tattalin arzikin dijital, samar da makamashi mara cutarwa ga muhalli, da kirkire-kirkire. Hakan yana nuna ci gaba daga hadin gwiwa mai karfi irin na baya zuwa ga hadin gwiwa mai fadi a bangarori daban-daban na zamani, masu amfanarwa ga juna. Yarjejeniyar Kimiyya da kirkire-kirkire ta 2025 tare da Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) da hadin gwiwar CACSA shaida ne na wannan ci gaban sauyin.

Idan aka aiwatar da wadannan yarjejeniyoyin hadin gwiwar yadda ya kamata, wannan hadin gwiwa mai zurfi zai iya taimakawa Afirka wajen hanzarta gyara da ci gaban masana’antunta da komawa cikin zamani. Har ila yau, hakan zai sanya Sin da Afirka a matsayin abokan tarayya wajen tsara sabon tsarin ci gaban duniya mai bangarori daban-daban.

 

 

 

 

 

 

 

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce December 11, 2025 Ra'ayi Riga Ya Kamata Amurka Ta Daina Sa Hannu Cikin Harkokin Najeriya December 4, 2025 Ra'ayi Riga Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi December 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Waiwaye Adon Tafiya: Manyan Nasarorin Da Aka Cimma A Dangantakar Kasashen Afirka Da Sin A 2025
  • Kotu Ta Umarci EFCC Ta Biya Wani Ƴan Kasuwar Kano Miliyan 5, Ta Nemi Afuwar Su
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu