Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfado Da Filin Jirgin Sama Na Kano
Published: 12th, November 2025 GMT
Shugaban Hukumar Gudanarwa Filayen Jiragen Sama ta Kasa (FAAN), Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya sake tabbatar da kudirin Gwamnatin Tarayya na dawo da tsohon martabar Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano.
Dakta Ganduje ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar duba aiki da ya kai filin jirgin a Kano.
Ya jagoranci wata tawaga mai ƙarfi ta jami’an FAAN domin tantance halin da filin jirgin yake ciki yanzu, ciki har da ayyukan da ake gudanarwa da kuma waɗanda aka bari da nufin samar da cikakken tsari na zamani da dorewar ci gaba.
Ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin tsofaffin filayen jiragen sama masu tarihi a Najeriya da yankin Yammacin Afirka, wanda a da yake ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin tashi da saukar jirage da ke haɗa Najeriya da sauran sassan duniya.
“Mun zo ne mu gani da idonmu, tsoffin ayyuka da sababbi, domin mu tsara sabuwar hanya ta farfado da wannan fili tare da dawo da matsayinsa cikin fitattun filayen jiragen sama na yankin,” in ji Ganduje.
Ya jaddada cewa hukumar FAAN za ta tabbatar da inganta jin daɗin fasinjoji, kiyaye ƙa’idodin tsaro, da kuma haɓaka ingancin aiki bisa ka’idodin ƙasa da ƙasa.
Dakta Ganduje ya tabbatar da cewa abubuwan da tawagar ta gano a yayin ziyarar za su zama ginshiƙi wajen tsara sabuwar manuniya ta dabarun sake farfado da filin domin ya zama abin koyi a harkar gudanar da filayen jiragen sama da kuma abin ƙarfafa tattalin arzikin Arewa.
Tawagar ta ziyarci sassa daban-daban na filin jirgin, ciki har da zauren sauka da tashin fasinjoji, hanyar tashi da saukar jirage, da kuma rukunin jigilar kaya, domin gano wuraren da ake bukatar gaggawar gyara.
ABDULLAHI JALALUDDEEN, Kano.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba
Shugabannin jam’iyyar APC a matakin unguwanni 35 da sakatarorinsu a faɗin Jihar Kuros Riba, sun nemi a tsige shugaban jam’iyyar na jihar, Mista Alphonsus Eba, bisa zargin badaƙala da kuɗaɗen jam’iyya da kuma nuna son kai wajen gudanar da harkokin jam’iyyar.
Wannan buƙatar ta fito ne a cikin wata sanarwa da shugabanni da sakatarorin jam’iyyar suka rattaba wa hannu bayan taron da suka gudanar a garin Kalaba, babban birnin jihar, a ranar Talata.
Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a BornoShugabannin sun bayyana cewa idan ba a ɗauki mataki kan shugaban ba, akwai yiwuwar rikicin cikin gida ya durƙushe jam’iyyar a jihar.
Da yake jawabi bayan taron, shugaban ƙungiyar shugabannin, Cif Kelvin Njong, ya shaida wa Aminiya cewa sun gamsu cewa shugaban jam’iyyar na jihar yana amfani da dukiyar jam’iyya yadda yake so ba tare da tuntubar kowa ba.
“Muna zargin shugaban jam’iyyar da wadaƙa da kuɗaɗen jam’iyya. Ba ya bin tsarin jam’iyya kuma ba ya jin shawarar kowa. Wannan ne dalilin da ya sa muke son a sauke shi domin a samu shugabanci nagari,” in ji shi.
Sun kuma zargi shugaban jam’iyyar da nuna bambanci da son kai ga wasu ’ya’yan jam’iyyar, lamarin da suka ce ya saɓa wa wasu sassa na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC da aka sabunta a watan Maris na 2022.
Haka kuma, shugabannin sun yi zargin cewa Alphonsus Eba ya ƙi raba kuɗaɗen da aka samu daga sayar da fom ga ‘yan takara a zaɓen 2023 yadda ya kamata, musamman ga shugabannin jam’iyyar a ƙananan hukumomi da mazabu.
“Akwai shugabanni da sakatarori har mutum 5,778 a matakai daban-daban, amma an ce naira miliyan 9.2 kawai aka raba daga cikin miliyoyin da aka tara.
“Shugabannin jiha su kaɗai ne aka bai wa naira miliyan 40. Wannan rashin adalci ne kuma ya saba da tsarin jam’iyya,” in ji su.
Sun kuma buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan yadda shugaban ya riƙa kashe kuɗaɗen jam’iyya da sunan ayyuka, tare da buƙatar a tabbatar da raba kaso 70 cikin 100 na kuɗaɗen jam’iyya ga ƙananan hukumomi, mazabu, da gundumomi.
Ɗaya daga cikin shugabannin jam’iyyar a ƙaramar hukumar Bekwarra, Kwamared Odama Thomas Odama, ya ce: “Abin da muke cewa gaskiya ne, ba bita-da-ƙulli muke yi masa ba. Shugaban ya ci amana kuma hakan ya jawo ɓacin ran ’ya’yan jam’iyyar.”
Shi ma sakataren ƙungiyar shugabannin jam’iyyar APC a matakin ƙananan hukumomi, William Book, ya jaddada cewa duk zarge-zargen da aka ambata gaskiya ne.
“Ba zargin na shaci faɗi muke yi masa ba, akwai hujjoji da takardu da ke tabbatar da abin da muke faɗi,” in ji shi.