Leadership News Hausa:
2025-09-18@00:43:05 GMT

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Published: 3rd, August 2025 GMT

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Magana ta gaskiya matsala daya ce zuwa biyu ko uku, na farko akwai laifin iyaye, na biyu akwai laifin samari da suke zuwa su yi auren, na uku kuma akwai laifin amaryar wacce ita ce take zaman auren.

Bari na fara da maganar farko, dalilin da ya sa na ce laifin iyaye ne shi ne; duk mutumin da ya zo zai auri ƴarka, idan kana da ƴa ta isa aure, ya kamata ka zaunar da shi ka tambaye shi; mene ne ma auren, kuma me yasa yake son ya auri ƴar taka? da yawan samarin da suke yin aure, ba su san ma mene ne auren ba.

An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya anyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Alal haƙiƙanin gaskiya, sha’awa ce kawai take tunzura su; a tunanin samari jima’i kawai shi ne aure, wannan shi yake kawo mace-macen aure ka ga namiji ya saki mace cikin sauƙi. ɗomin idan don sha’awa ka yi, da zarar ka gusar da sha’awarka za ka ji to, ai ba ka da kuma wata buƙata a wajenta.

ɗon haka, yana da kyau ka tambayi wanda ya zo neman auren ƴarka cewa; mene ne ma auren? a nan za ka gane ko yana da addini ko kuma ba shi da shi, ya san mene ne ma auren ko bai sani ba, shin ya san aure sunnah ce ta Ma’aiki ko ma bai sani ba?

Ba fa jima’i ne kawai aure ba, wani sha’awa ce, ruɗu ne kawai tana da kyau, ta iya kwalliya da dai sauransu, shikenan da an yi auren kuma ya ga ta zo ta yi wanka ta yi kaza, ya ga ta tashi daga barci, ya zo ya same ta ba wanka, sai ya ga kamar ba waccan ba ce, to ya kamata ya san ma mene ne auren tukunna.

Ba laifi ba ne, kuma ba abin kunya ba ne, ka sanar da shi kai da shi, domin burinka idan ya auri ƴarka su zauna har abadan da’iman mutu-ka-raba, ba kawai a yi rawar ƙafa ba. Ah! kawai shikkenan yarinyar nan duk ƙannenta sun yi aure ga wani ya fito kawai sai a ce turo iyayenka, saboda me, waye shi, mene ne matakin iliminsa, me ya sani, me ya sani dangane da auren?

Sannan ku zaunar da ƴarku, ku sanar da ita mene ne aure, da kike ta rawar ƙafa za ki auri wane, me ya sa kike sonsa? ɗon haka, ga abin da addini ya shara’anta, ga abin da ya kamata ki yi idan kina son ki zauna lafiya, ga kuma yadda ya kamata ki yi.

Neman kai kake da ƴarka? lokacin da ka yi aure ka haife ta har ta yi laulayi aka goya ta, ta tashi ta fara rarrafe, ka raine ta, makaranta safe, rana da kuma dare, ka kai ta ka dauko ta, duk ba ka yi neman kai da ita ba sai da aka zo dan taƙi na ƴan shekaru kawai da wani yake so, kake son ya aure ta sai ka yi ta gaggawa?

ɗuk mace a duniya Allah ya rubuta mata mijinta, amma dolenmu sai mun tsaya mun miƙa wa Allah lamarinmu, ba lallai sai maikuɗi za ki aura ki zauna lafiya ba, Hajiya ki nemi mai rufin asiri, wanda za ku zauna lafiya ya rufa miki asiri ya ga mutuncin iyayenki, ya kare ki, ya kare mutuncinki, ya kuma kare addininki.

Sannan su ma na dawo kan su samarin masu yin aure, sha’awa ce take sa wa da yawa muke yin aure, ko kuma tana burge ni, ko abokina ya auri wata kyakkyawa fara ƙal ni ma ƙal zan aura a ce shege wane ya auri wance, “Kai! ka ga matar wane?”, wa ya aike ka Alaji duk ga abin da Annabin tsira ya karanto ka kalli wannan suffofin shin tana daga ciki?

Amma ba ma bi, muna dauka ne kawai mai kyau ce, ta iya wanka, ta iya girki, “kai! ka ga idan ta yi wanka, ai idan na auri wannan ai na kece a cikin abokanai”, wa ya fada maka? ba wannan ba ne Alaji.

Alaji ka yi aure kai kwanciyar hankali, ka bi abin da addini ya ce da abin da ma’aiki (SAW) ya fada, ga irin tsarin duk ya zayyano mana siffofi.

Idan za ka auri mace, kar ka yi mata ƙarya, ku yi gaskiya da gaskiya, kuma ka sanar da ita ga irin zaman da kake so ku yi tun kuna waje, yadda idan ta shiga ma ba za ta ga ka yi mata ƙarya ba, Alaji wallahi idan ka yi ƙarya ma ba za ka ga daidai a gidanka ba, ka yi iya bakin ikonka kar ka kwaikwayi rayuwar wani ka yi iya irin taka wacce ba ta kaucewa al’ada da addininmu na musulunci ba.

Idan muna so a rage zawarawa da mace-macen aure, to kafin auren sai mu riƙa kiyayewa da sanin me ya kamata mu yi.

Wassalamu Alaikum.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Zawarawa

এছাড়াও পড়ুন:

NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025

Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO), ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare (SSCE) na shekarar 2025.

Daga cikin ɗaliban da suka zana jarabawar guda 818,492, kashi 60.26 sun ci aƙalla darusa biyar da suka haɗa da Lissafi da Turanci.

Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Shugaban NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya ce ɗalibai 1,367,210 suka yi rajistar jarabawar; maza 685,514 da kuma mata 681,696.

Amma daga cikinsu, ɗalibai 1,358,339 ne suka zana jarabawar.

Ya ce ɗalibai 1,144,496, wanda ya kai adadin kashi 84.26, sun samu darusa biyar ba tare da cin Lissafi da Turanci ba.

Sai dai an dakatar da sakin sakamakon makarantu takwas a Ƙaramar Hukumar Lamorde ta Jihar Adamawa saboda rikicin ƙabilanci da ya auku tsakanin 7 zuwa 25 ga watan Yuli, 2025.

Rikicin ya yi sanadin wanda ya hana zana jarabawar darusa 13 da takardu 29.

Hukumar na tattaunawa da gwamnati don sake bai wa ɗaliban damar rubuta jarabawar.

NECO ta kuma bayyana cewa an samu makarantu 38 daga jihohi 13 ds laifin aikatar satar amsa yayin zana jarabawa.

Za a gayyace su zuwa babban ofishin NECO kafin ɗaukar mataki a kansu.

Haka kuma, hukumar ta dakatar da mutum tara da ke aikin sanya ido sake kula da jarabawa saboda gazawarsu wajen hana satar amsa.

Mutanen da aka dakatar, uku sun fito daga Jihar Ribas, uku daga Babban Birnin Tarayya, da kuma mutum ɗai-ɗai daga Jihohin Neja, Kano da Osun.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya