Aminiya:
2025-11-02@12:29:44 GMT

Sai an samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu za mu ajiye makamai — Hamas

Published: 3rd, August 2025 GMT

Ƙungiyar Hamas ta sake jadadda matakinta na cewa ba za ta taɓa ajiye makami ba, har sai lokacin da duniya ta amince da samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu a yankin Gabas ta Tsakiya, wani abu da zai sake mayar da yarjejeniyar zaman lafiya da ake ƙoƙarin ƙullawa baya.

A halin da ake ciki yanzu haka ana wata tattaunawa wadda ba ta kai tsaye ba tsakanin Isra’ila da Hamas don ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki 60, da kuma sakin mutanen da ke riƙe a hannun ɓangarorin biyu.

A Talatar da ta gabata ne ƙasahen Qatar da Masar suka sanar da matakin ƙasashen Saudi Arabiya da Faransa na goyon bayan samar da ƙasar Falasdinu, don tabbatar da dawamammen zaman lafiya a gabas ta tsakiya.

To amma ƙasashen sun ce hakan za ta yiwu ne kawai idan har Hamas ta amince da ajiye makamai ga mahukuntan Faladinu da ke Ramallah.

A wata sanarwa da Hamas ɗin ta fitar ta ce bazata taɓa ajiye makamai ba, har sai ta tabbatar da samun ƴancin kan Falasɗinawa, da kuma ayyana birnin Ƙudus a matsayin babban birni.

Wannan ba shi ne karon farko da Hamas ke bayyana hakan a matsayin hanya ɗaya tilo ta ajiye makami ba, yayin da ita kuma Isra’ila ke cewa zata yi kowacce irin tattaunawa da Hamas ne bayan sun amince da ajiye makami.

A makon da ya gabata Firaministan Isra’ila Benjamin Natenyahu ya ce ba shakka samar da ƴantacciyar ƙasar Falasɗinu, shimfida hanya ne na rusa Isra’ila don haka ba zai taɓa aminta da hakan ba, kuma dole ne sha’anin tsaron yankunan Falasɗinu ya kasance ƙarƙashin ikon ƙasar sa.

Da yake caccakar matakin ƙasashen Birtaniya, Canada da kuma Faransa na goyon bayan samar da ƙasar Falasɗinu biyo bayan halin da Isra’ila ta jefa al’ummar Gaza, ya ce wannan abu ne da Hamas ta janyo.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila ƙasar Falasɗinu

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

“Amurka ba za ta tsaya kawai tana kallo ba yayin da irin waɗannan ta’addancin ke faruwa a Nijeriya da sauran ƙasashe.

“Mun shirya, muna da ƙarfi da niyyar kare Kiristoci a faɗin duniya,” in ji Trump.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano October 31, 2025 Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai