Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
Published: 29th, July 2025 GMT
Akalla mutane 7 ne aka ceto, bayan kifewar kwale-kwale a wani kogi da ke Zangon Maje, ƙaramar hukumar Taura, ta jihar Jigawa ranar Litinin.
Shugaban ƙaramar hukumar Taura, Dr Shuaibu Hambali ne ya bayyana hakan ga Rediyon Najeriya a Dutse, babban birnin jihar.
A cewarsa, lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, lokacin da wasu manoma ke dawowa daga gonakinsu a ƙauyen Zangon Maje, inda suka hau kwale-kwalen.
Ya ce, jami’an bada agajin gaggawa na yankin sun samu nasarar ceto mutane 7 a kokarin da suka yi na ceto wadanda lamarin ya shafa.
Ya ƙara da cewa, masu ceton sun gano gawar mutum guda a yankin Yalleman da ke ƙaramar hukumar Kaugama.
Dr Shuaibu ya bayyana cewa, sauran mutane 9 da ke cikin jirgin har yanzu ba a same su ba a lokacin da ake bayar da wannan rahoto.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, ba a fitar da sunayen waɗanda abin ya shafa ba, amma lamarin ya jefa al’ummar yankin cikin jimami da baƙin ciki.
Shugaban ƙaramar hukumar ya bayyana cewa, za a raba rigunan kariya (life jacket) ga fasinjoji a nan gaba kadan domin kiyaye sake afkuwar lamarin nan gaba.
Ya kuma gargadi matuka kwale-kwale da su kiyaye ƙa’idojin tsaro da kaucewa cunkoson fasinjoji, musamman da yamma a lokacin damina, inda ruwa ke ƙaruwa a kowane lokaci.
Dr Hambali, wanda ya isa wurin da abin ya faru, ya jajanta wa iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Wasu daga cikin mazauna yankin da Rediyon Najeriya ta tattauna da su, sun nemi gwamnatin ta gaggauta ɗaukar matakan da suka dace, tare da inganta hanyoyin sufuri ta ruwa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Taura ƙaramar hukumar kwale kwale
এছাড়াও পড়ুন:
An gano gwawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
An gano gwawar mutum 15 a yayin da ake ci gaba neman wasu uku bayan hastarin kwalekwale da ya auku a yankin Ƙaramar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja.
Kwalekwalen ya kife ne a yayin da yake ɗauke da mutum 43 da buhuna 60 na shansherar shinkafa da shanu uku da tumaki biyu a ranar Asabar.
Kifewar kwalekwalen ta auku ne a sakamakon karonsa da wani kututture bayan ya ɗauki fasinjojin daga yankin Guni zai kai su kasuwar mako-mako da ke yankin Zumba da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro.
Manajan Hukumar Albarkatun Koguna ta Ƙasa (NIWA), mai kula da yankin, Akapo Adeboye, ya ce an gano gwawar mutum 15, amma ana ci gaba neman wasu mutum uku, ko da yake cewa an yi nasarar ceto mutum 26 da ke sanye da rigunan kariya da ransu, bayan aukuwar hatsarin.
HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INECAdebayo ya bayyana cewa, “Mutanen sun taso ne daga ƙauyen Shayita za su tafi Kasuwar Kwata da ke Zumba tare da kayansu na miliyoyin kuɗaɗe a ranar Asabar 26 ga watan Yuli, 2025.
“Jami’an NIWA sun gudanar da aikin ceto, amma an samu asarar rayuka 18, an ceto wasu 26, kuma aka ci gaba da aiki da kuma ƙoƙarin kamo mai kwalekwalen.”
Shaidu sun ce hastarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na ranar Asabar, kuma yawancin fasinjojin mata ne da ƙananan yara, kuma jami’an Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) sun tabbatar da hakan.
Sarkin Ruwan Zumba, Umar Isah, ya ce mutum 15 ne suka rasu, an ceto 25, amma an yi asarar shanu uku da buhu 60 na shansherar shinkafa.
“A cikin mutum 15 da suka rasu har da ƙananan yara uku mata da gano gawarwakinsu,” in ji shi.
Amma Darakta Janar na Hukumar NSEMA, Abdullahi Baba Arah, ya ce gawa 13 aka gano kuma an yi jana’izarsu a ranar Lahadi.
Arah, wanda ya tabbatar da asarar wasu mutane da dabbobi da kayan abinci a hatsarin, ya ce gawarwakin sun haɗa da mata takwas da maza uku da kuma yara biyu.