Aminiya:
2025-11-16@18:53:05 GMT

Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina

Published: 13th, April 2025 GMT

Yin garkuwa da mutane domin don karbar kudin fansa ya zama ruwan dare a Jihar Katsina har ta kai ga ana shiga cikin manyan birane ana daukar manyan mutane ko makusantansu.

Daga manyan sojoji zuwa sarakuna da malaman addini da ’yan siyasa da attajirai da ma dalibai, babu wanda ya tsira daga wannan matsalar ta’addanci.

Gwarzon gasar Al-Kur’ani

A yayin da ake shirye-shiryen daukar azumin watan Ramadana ne ’yan bindiga suka yi garkuwa da Gwarzon Gasar Al-Kur’ani na Kasa da aka kammala a Jihar Kebbi, Abdulsalami Rabi’u Fasakari a hanyarsa ta komawa gida tare da ’yan uwansa bayan Gawmna Dikko Radda ya karbi bakuncinsa tare da karrama shi.

Sai bayan makonni biyu, a yayin da ake gab da daukar azumin ne kuma danginsa suka sanar cewa sun kubuta daga hannun ’yan bindiga ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

Mahaifinsa, Alaramman, Malam Rabiu Zakariya Faskari, ya bayyana cewa suna tsare a hannun ’yan bindiga a Katsina har sai da wani babban dan bindiga mai suna Yellow daga Zamfara ya zo ya karbe su da karfi,

“Muna ta addu’a har ranar Juma’a da aka zo aka ce mu fito mu tafi. Yaransa suka ɗauke mu suka kai mu wani gari, daga nan muka yi tafiyar awa huɗu kafin muka samu mota.”

Malam Rabiu, ya ce da suka hau babur sai direban ya shaida musu cewa an kashe Yellow

Sheikh Ahmed Suleiman

Irin haka ya yi kama da abin da ya faru a watan Maris na shekarar 2019 inda ’yan bindiga suka yi wa ayari malaman addinin Musulunci da ke dawowa daga taron addini daga Jihar Kebbi kwanton bauna a yankin Sheme da ke Jihar Katsina, inda suka yi garkuwa da fitaccen makarancin Al-Kur’ani nan, Sheikh Ahmed Muhammad Sulaiman, da wasu malamai hudu. Sai da malaman suka shafe kwanaki 12 cur a hannun ’yan ta’addan kafin su sako su.

Janar Maharazu Tsiga

Idan ba a manta ba, kafin sace su Alaramma Abdulsalamu ne ’yan bindiga suka kutsa gidan LaftanarJanar Maharazu Tsiga (ritaya) tsohon Shugaban Hukumar Kula da Masu yi wa Kasa Hidima (NYSC) da karfin tuwo suka yi awon gaba da shi, sai da ya shafe sama da kwanaki hamsin a hannunsu kafin a sake shi tare da sauran mutane 18 da aka sace su tare a mahaifarsa da ke Tsiga a Jihar Katsina.

Ko a karshen makon da ya gabata, sai da ’yan bindiga suka yi garkuwa da kusan mutum 60, yawancinsu mata da kananan yara a kauyukan kananan hukumomin Dandume da Funtua, inda suka kashe wasu mutum shida.

Yayan Gwamna Dikko Radda

Wani daga cikin manyan mutane da aka yi garkuwa da shi da aka yi a baya-bayan nan ta girgiza Jihar Katsina shi ne, yayan Gwamna Umaru Dikko Radda wanda kuma shi ne Maigarin Radda, Alhaji Kabir Umar Radda, sai da aka biya kudin fansa kafin a karbo shi daga hannun ’yan bindiga.

A duk lokacin da Gwamna Radda zai yi magana a kan batun tsaro ya kan kawo misali da abin da ya faru ga wannan dan uwa nasa.

Surukar tsohon Gwamna Masari

Kwatsam sai aka ji labarin an sace sararkuwar tsohon gwamna Masari Hajiya Hauwa a lokacin kuma yana kan mulki.

Satar dattijuwar ta bayar da mamaki domin kuwa a yayin da ake zargin barayin daji ne suka sace ta, sai aka gano cewa wasu matasa ne karkashin wani da ake yi wa lakabi da Yalo suka dauke ta a gidanta da ke can wajen sabon titin Kwado a garin Katsina suka hannanta ta ga wasu Fulani da ake zargi da satar shanu da aikata kisan haka-kawa da kuma garkuwa da mutane.

Daga bisani dai an yi nasarar karbo ta, daga bisani aka kama matasan da suka sace ta da farko. Nan ma an samu bayanai masu karo da juna inda wasu ke cewa sai da aka biya kudin fansa, wasu kuma na cewa lallashi ne ya sa aka sako ta.

Duk wadannan abubuwa sun faru ne bayan gwamnatin Masari ta nemi sasanci da wadannan ’yan bindigar.

Magajin Garin Daura

A cikin watan azumin shekarar 2022 ne kuma aka wayi gari da labarin sace Magajin garin Daura, Alhaji Musa Umar, wanda suruki ne ga hadimin Shugaban Kasa Buhari.

Wasu mutane ne a cikin mota suka zo suka yi awon gaba da wannan basarake, kamar kamar dai yadda aka sace surukar Masari.

Buhari dan asalin garin Daura ne kuma can yake zuwa hutun sallah, kuma abin ya faru ne a ’yan makonni kafin ya tafi hutun sallah a masarautar ta Daura.

Sai dai hukumomi sun ce babu ko sisin da aka biya wajen kubutar da shi domin Rundurar ’Yan Sanda masu Yaki da Ayyukan Ta’addanci karkashi jagorancin Abba Kyari ne suka ceto shi a garin Kano a gidan da aka tsare shi tare da kama masu garkuwar.

Hakimai da Dagattai

Hatta da masu gari ba su tsira ba, sai dai wasu sukan samu kubuta ko nan take ko kuma a ana tafiya da su kafin a kai su maboyar ’yan ta’addan.

Amma a lokacin da barayin daji suka je za su yi garkuwa da Hakimin ’Yantumaki, Marigayi Alhaji Abubakar Attiku Maidabino, ya ki yarda ya ba da kai bori ya hau, nan take suka bude masa wuta a cikin dakin da ya buya, suka kashe shi.

Sai kuma Maigarin Wurma, wanda kamar yadda muka samu labari, ba a fita da shi daga cikin garin ba wani daga cikin barayin ya nuna mashi wani zaure ya ce, ya shige ciki.

Dan uwan Dahiru Mangal

Kazalika, akwai wani da ke matsayin da ga hamshakin dan kasuwar nan Alhaji Dahiru Mangal wanda ake zargin dangantakarsa da attajirin tasa masu garkuwar suka dauke shi.

Mahaifiyar mai Gidajen Man Shema

Hakazalika ’yan bindaiga sun yi garkuwa da mahaifiyar wani dan kasuwar da ke garin Dutsinma, mai suna Alhaji Mamman Nagogo wanda shi ke da gidajen man Shema.

Ita ma wannan dattijiuwa sai da danginta suka biya kudin fansa kafin ta shaki iskar ’yanci daga hannun bata-garin.

Mahaifiyar Rarara

Shi ma fitaccen mawakin siyasa, Dauda Adamu Kahutu, wanda aka fi sani da Rarara mahaifiyarsa ta shiga hannun masu garkuwa da mutane, inda ta shafe kwanaki da dama kafin jami’an tsaro su kubutar da ita.

Shugaban NURTW

Shugaban Kungiyar Direbobi ta Kasa (NURTW) reshen Jihar Katsina Alhaji Musa Garba ’Yandoma shi ma ya shiga hannun masu garkuwar kafin daga bisani a kubutar da shi.

Daliban Kankara

Sace daliban a Makarantar Sakandaren Kankara na daya daga cikin garkuwa da mutanen da zai yi wuya a manta da su, kasancewar a lokacin shi ne irinsa na farko da aka yi a Jihar Katsina, mahaifar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.

Kasurgumin dan bindiga Auwalun Daudawa wanda shi ma ya bakunci lahira ne ya jagoranci sace daliban a shekarar 2021 ya rarraba yaran zuwa wurare ciki kuwa har da yankin Karamar Hukumar Danmusa mai makwabtaka da Kankara, ya tsere da mafi yawansu zuwa dajin Zamfara.

Sai da aka kai ruwa rana tare da samun rahotanni masu karo da juna kafin fitowar yara, domin kwa har kungiyar Boko Haram sai da ta yi ikirarin ita ke da alhakin sace su.

A waje guda kuma, gwamnatin jihar ta yi ikirarin cewa ba ta biya kudin fansarsu ba, amma ta samu hadin kai da taimakon gwamnatin Jihar Zamfara a karkashin jagorancin Gwamna Bello Mohammed Mutawalle da sojojin Nijeriya, wadanda daga bisani suka ceto su.

Amma wasu rahoton sun ce sai da aka biya milyoyin kudin da masu garkuwar suka nema kafin sako ayran.

Shi kansa Auwalun Daudawa a wata hira da Jaridar Aminiya ta yi da shi, ya bayyana cewa sai da aka ba shi kudin fansa, amma dai ba su kai yawan abin da ya nema ba.

Kisan gillar ’yan bindiga

Sa’anan akwai wasu manyan hare-hare biyu da ’yan ta’addar suka kai a wasu yankunan jihar wadanda har gobe ake tunawa da su. Na farko shi ne, wanda Adamu Aleru, dan bindigar nan da ’yan sanda suka sanya tukuicin wasu miliyoyin kudi ga duk wanda ya yi sanadin kamo shi, ya jagoranci yaransa a kan babura kimanin 150 suka kai a garin Kadisau na Karamar Hukumar Faskari.

A wannan harin kusan kowane babur dauke yake da mutane uku kowannesu da bindiga, kamar yadda wani wanda aka kai harin da shi ya shaida wa manema labarai a hedikwatar ’yan sanda bayan an kama shi a wancan lokacin, a shekarar 2020.

Ya bayyana cewa dalilin kai harin shi ne, saboda jami’an tsaro sun kama dan Alerun a wani harin da suka kai.

Hari na biyu shi ne, wanda aka kai a garin Tsauwa inda ’yan bindigar suka kone daukacin garin sai da duk abin da ke cikinsa (mutum ko dabba) ya zama gawayi, in banda ’yan kalilan da suka tsallake rijiya da baya.

A harin ne aka tsinci gawar mace da ciki amma ta zama gawayi, wata kuma da goyo ta lullube wasu yaran, amma dukkansu sun kone kurmus sun zama gawayi, lamarin da ya sa jami’an tsaro da ’yan jarida zubar da hawaye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: daliban kankara garkuwa da mutane Jihar Katsina Maharazu Tsiga garkuwa da mutane yan bindiga suka biya kudin fansa a Jihar Katsina yi garkuwa da masu garkuwar masu garkuwa da aka biya

এছাড়াও পড়ুন:

MDD: Mutane 100,000 Ne Su Ka Fice Daga Birnin Al-Fasher Na Kasar Sudan

Hukumar dake kula da ‘yan hijira ta MDD ta ce; Da akwai fiye da mutane 100,000 da su ka fice daga birnin Al-Fasher makwanni biyu kadai bayan da da kungiyar RSF ta shimfidaikonta a cikinsa.

Mai magana da yawun hukumar ‘yan hijirar ta MDD, Yujing Biyun … ta kuma ce abu ne mai yiyuwa a halin yanzu adadin wadanda su k fice daga cikinbirnin sun fi haka,domin da akwai wadanda su ka makale akan hanya suna ci gaba da tafiya, wasu kuma suna cikin birnin suna son ficewa.

Mutanen da suke ficewa suna son isa yankunan da suke da nisa sosai kamar kilo mita 50 daga gundumar Darfur. Wasu kuma suna tafiyar dubban kilo mita daga yankin baki daya.

Sai dai kuma hukumar ‘yan hijirar ta ce,nisan da masu ficewa daga Al-Fasher suke yi, yana kara jefa su cikin hatsari saboda rashin abinci da ruwan sha aka hanya.

A yayin kutsen da rundunar RSF ta yi a cikin birnin na Al-Fasher ta aikata laifukan yaki da su ka hada kisan kiyashi, cin zarafi da wawason dukiyar mutanen birnin.

Hukumar yan hijirar ta MDD ta kuma ce, a fadin kasar Sudan da akwai mutanen da sun kai miliyan 30 da suke da bukatuwa da agaji na gaggawa.

A jiya Juma’a ne dai hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD ta amince da kafa kwamitin da zai bincika laifukan da aka yi a Darfur,musamma a birnin Al-Fasher.

A ranar 26 ga watan Oktoba ne dai mayakan rundunar kai daukin gaggawa ta RSF su ka kutsa cikin birnin na Al-Fsher, da shi ne cibiyar mulkin ta Darfur ta,, tare da cin zarafin mutanen dake ciki, bayan killace sun a watanni 18.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Yace Iran Ba za Ta Taba Mika Wuya Ga Duk Wata Barazana Ba November 15, 2025 Kasashen Latin Amurka Sun Shirya Tsaf Don Mayar Da Martani Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Kan Venuzuwela November 15, 2025 Rasha Tace Bata Da Shirin Kai wa Kungiyar Nato Hari Amma Za ta Mayar Da Martani Kan Duk Wata Barazana November 15, 2025 Shugaban Iran Da Prime Ministan Iraqi Sun Tattaunawa Kan Batun Zabe Da Kuma Alakar Dake Tsakaninsu. November 15, 2025 M D D Ta yi Tir Da Harin Da Yahudawa Yan Share Wuri Zauna Suka Kai A Masallaci A Yammacin kogin Jodan November 15, 2025 Mali ta Dakatar da Tashoshin Talabijin na Faransa TF1 da LCI November 15, 2025 Gaza: Amurka na matsin lamba ga kwamitin tsaro don amincewa da shirin Trump November 15, 2025 AU da MDD, sun karfafa dabarun tabbatar da zaman lafiya da tsaro November 15, 2025 Iran ta bukaci duniya ta gaggauta daukar mataki a Sudan November 15, 2025 EU ta nemi Isra’ila ta dauki mataki kan tashin hankali a Yammacin Kogin Jordan November 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya
  • Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi
  • Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
  • MDD: Mutane 100,000 Ne Su Ka Fice Daga Birnin Al-Fasher Na Kasar Sudan
  • Babu Janar ɗin da ISWAP ta kama a Borno — Sojoji
  • Mayaƙan ISWAP sun sace Janar sun kashe sojoji a Borno
  • Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yanga 16 sun sace mutane 42 a Neja
  • Bebejin Katsina, Alhaji Nuhu Yashe ya rasu
  • Nijeriya ta doke Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya