Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Published: 3rd, August 2025 GMT
Auwalu Labarina, wanda ke cikin matasa jarumai da tauraruwarsu ke haskawa a Masana’antar Kannywood, ya fito a manyan fina-finai da dama da suka hada da darasi, Kwana Casa’in, Gidan Sarauta da kuma shirin nan na Labarina, ya kuma samu kyautuka da dama da suka danganci wannan sana’a tasa ta fim a lokuta daban-daban.
da yake amsa tambaya a kan me yasa ya fi mayar da hankali wajen ɗora bidiyo, musamman na jarumai mata a Masana’antar Kannywood a shafukansa na sada zumunta, musamman kuma ‘Facebook’? Sai Baba Sadiƙ ya ce; ba komai ba ne ya jawo haka illa tsarin biyan kuɗi (Monetization) da kamfanin ‘Facebook’ ya fito da shi, domin yanzu na zage damtse ina neman kuɗi, ba tare da wasa ba, kafin yanzu ina ɗora bidiyon shawarwarin da za su taimaki al’ummarmu, amma kuma su mutanen da ke kallo sai na ga kamar ba su da ra’ayin ire-iren wadannan abubuwa da nake ɗorawa a shafin nawa.
Bayan daukar tsawon lokaci ina yin wadannan bidiyoyi na shawarwari, sai na yanke shawarar yin watsi da shi na koma ɗora bidiyoyina tare da abokan aikina ƴan fim, musamman idan muka haɗu a lokeshan na daukar fim, daga wannan lokaci ne sai na ga yawan ‘likes’ da ‘comments’ ɗin da mutane suke yi a shafi nawa ya ƙaru sosai, sannan adadin mutanen da ke ziyartar shafin shi ma ya ƙaru, sai kuma ga shi ina samun dalar Amurka fiye da 300 a duk lokacin da na ɗora ire-iren wadannan bidiyoyi nawa a shafin, sai kawai na ci gaba da yin hakan.
daga wancan lokacin da na fara ɗora bidiyoyi nawa tare da jarumai mata ƴan fim da sauran sanannun mata, na kan samu aƙalla Naira Miliyan biyar zuwa 10 a duk wata daga abin da ‘Facebook’ ke biya na, don haka yanzu na gane cewa; talauci ne matsalata a lokacin baya, kuma Alhamdulillahi yanzu na fara samun sauƙin wannan matsala a halin yanzu da hanyoyin samu suka ƙara buɗe min, in ji shi.
daga ƙarshe, Baba Sadiƙ ya ce; kamata ya yi a ce matasa su mayar da hankali wajen abubuwan da za su taimake su a rayuwarsu, ba su tsaya suna faɗin aibin wani ko yaba burgewar wani ba, yanzu matasa da dama su kan ɓata lokacin su wajen aibata wani idan ya yi kuskure, ko kuma yabon wanda bai ma san suna yi ba, ba komai ne ke jawo irin haka ba; illa rashin aiki da mafi yawancin matasa ke fama da shi, a maimakon ka tsaya cewa; Rarara ya sai sabuwar mota ko kuma Hadiza Gabon ta yi ‘Slimming’ gara ka je ka nemi abin da za ka rufa wa kanka asiri, kamar yadda ya shawarci matasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Kannywood
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
Mai kuɗin Afrika kuma Shugaban Matatar Mai ta Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya zargi wasu manyan masu harkar mai da shirya maƙarƙashiya domin kashe matatarsa.
Ɗangote ya yi zargin cewa miyagun ’yan kasuwan suna ƙoƙarin kashe matatar mansa mai darajar dala biliyan 20, kamar yadda aka kashe masana’antar tufafi ta ƙasar.
Ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Legas yayin bikin cika shekara ɗaya da fara samar da fetur a matatar, inda ya ce tafiyar ta kasance cike da ƙalubale tun daga farko.
“A gaskiya tafiyar shekara ɗaya da ta wuce ta yi mana matuƙar wuya. Mun zo mu sauya tsarin kasuwancin man ƙasa. Amma wasu na ganin mun raba su da hanayar cin abinci bakinsu,” in ji shi.
’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati BaYa ci gaba da cewa, “Amma abin da muka yi shi ne mun sa Najeriya da nahiyar Afirka gaba ɗaya su yi alfahari.”
Ɗangote ya ce matatar ta riga ta fitar da lita biliyan 1.8 na man fetur zuwa ƙasashen waje cikin watanni uku da suka gabata, sannan tana da isasshen ƙarfi wajen cika buƙatar cikin gida.
Ya ce tun daga fara aikin matatar a watan Satumbar 2024, dogayen layukan man fetur da suka fi shekaru 50 ana fama da su a Najeriya sun zama tarihi.
Ɗangote ya ƙara da cewa farashin fetur ya sauka daga kusan Naira 1,100 zuwa N841 a wasu jihohi, kuma da zarar sabbin motocin gas (CNG) masu dakon mai sun fara aiki a duk faɗin ƙasar, rage farashin zai fi tasiri.
Ya kuma bayyana cewa sabbin motocin CNG 4,000 za su samar da aƙalla ayyukan yi 24,000, ciki har da direbobi, makanikai da sauran ma’aikata.
“Ba mu kore kowa daga aiki ba, sai dai muna ƙara samar da ayyuka,” in ji shi.
Ɗangote ya zargi masu harkar mai da haɗa kai da ’yan kasuwa na cikin gida da na waje da ƙoƙarin hana nasarar matatar.
“Yadda aka hallaka masana’antar yadi, haka suke ƙoƙarin kashe matatar mu,” in ji shi.
A kan zargin cewa bai wadatar da ƙasa da fetur ba, sai ya mayar da martani da cewa: “Idan ba mu da ƙarfin samar da mai, me ya sa muke fitarwa zuwa ƙasashen waje?”
Ya kuma yi ba’a ga Ƙungiyar Ma’aikatan Mai (NUPENG) wadda ta ce rage farashin fetur na matatar Dangote “kyautar Girka ce.” Dangote ya ce: “Ko da kuwa kyautar Girka ce, ai kyauta ce, za ta kuma ci gaba da kasancewa.”
Ya jaddada cewa abin da Najeriya ke buƙata yanzu shi ne kare masana’antunta, domin ci-gaban tattalin arziki da kuma rage dogaro da shigo da kaya daga waje.