Shirin ACRESAL Zai Samar Da Injinan Ban Ruwa Masu Amfani Da Hasken Rana A Jigawa
Published: 3rd, August 2025 GMT
A kokarin da Gwamnatin Jihar Jigawa ke yi na kara habbaka harkokin noma, shirin ACRESAL yace sami amincewar gwamnatin na siyo injinan ban ruwa masu amfani da hasken rana guda 3,000 domin tallafawa manoma.
Shugaban Shirin na Jihar, Malam Yahaya Kafin Gana ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.
Yana mai cewar, samar da injinan ban ruwa masu amfani da hasken rana ga manoman na da nasaba da bunkasa aikin gona a jihar Jigawa.
A cewar sa, shirin ACRESAL na jihar ya sami sahalewar gyaran karin wasu cibiyoyin renon itatuwa guda 3 a sassan jihar.
Malam Yahaya Uba Kafin Gana ya kara da cewar, cibiyoyin renon itatuwan da za’a gyara sune na garuruwan Birnin Kudu da Kafin Hausa da kuma na Gadar Kazaure.
Yana mai nuni da cewar baya ga gyaran cibiyoyin, har Ila yau za’a kuma a samar musu da rijiyoyin samar ruwan sha masu amfani da hasken rana.
Kafin Gana, yace nan bada jimawa ba za su sake zakulo wasu cibiyoyin renon itatuwa guda 5 domin mayar da su irin na zamani.
Yace shirin ya kuma siyo karin Injinan yasar kogi guda 2 domin mara baya ga guda 2 da ake dasu a ma’aikatar kare muhalli ta jihar Jigawan.
Kazalika, ya ce shirin zai samar da hasken wutar lantarki mai amfani da hasken rana a garuruwan Matamu da Safa da Galaucimi da Hannun Giwa da Kwazalewa da Tozarya dake kananan hukumomin Birniwa da Birnin Kudu da Miga da Kafin Hausa da Kazaure har ma da Sule Tankarkar.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa amfani da hasken rana
এছাড়াও পড়ুন:
Sai an samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu za mu ajiye makamai — Hamas
Ƙungiyar Hamas ta sake jadadda matakinta na cewa ba za ta taɓa ajiye makami ba, har sai lokacin da duniya ta amince da samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu a yankin Gabas ta Tsakiya, wani abu da zai sake mayar da yarjejeniyar zaman lafiya da ake ƙoƙarin ƙullawa baya.
A halin da ake ciki yanzu haka ana wata tattaunawa wadda ba ta kai tsaye ba tsakanin Isra’ila da Hamas don ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki 60, da kuma sakin mutanen da ke riƙe a hannun ɓangarorin biyu.
A Talatar da ta gabata ne ƙasahen Qatar da Masar suka sanar da matakin ƙasashen Saudi Arabiya da Faransa na goyon bayan samar da ƙasar Falasdinu, don tabbatar da dawamammen zaman lafiya a gabas ta tsakiya.
To amma ƙasashen sun ce hakan za ta yiwu ne kawai idan har Hamas ta amince da ajiye makamai ga mahukuntan Faladinu da ke Ramallah.
A wata sanarwa da Hamas ɗin ta fitar ta ce bazata taɓa ajiye makamai ba, har sai ta tabbatar da samun ƴancin kan Falasɗinawa, da kuma ayyana birnin Ƙudus a matsayin babban birni.
Wannan ba shi ne karon farko da Hamas ke bayyana hakan a matsayin hanya ɗaya tilo ta ajiye makami ba, yayin da ita kuma Isra’ila ke cewa zata yi kowacce irin tattaunawa da Hamas ne bayan sun amince da ajiye makami.
A makon da ya gabata Firaministan Isra’ila Benjamin Natenyahu ya ce ba shakka samar da ƴantacciyar ƙasar Falasɗinu, shimfida hanya ne na rusa Isra’ila don haka ba zai taɓa aminta da hakan ba, kuma dole ne sha’anin tsaron yankunan Falasɗinu ya kasance ƙarƙashin ikon ƙasar sa.
Da yake caccakar matakin ƙasashen Birtaniya, Canada da kuma Faransa na goyon bayan samar da ƙasar Falasɗinu biyo bayan halin da Isra’ila ta jefa al’ummar Gaza, ya ce wannan abu ne da Hamas ta janyo.