Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi
Published: 3rd, August 2025 GMT
Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da naɗa Hon. Ismaila Ahmed Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi, bayan rasuwar Alhaji Isa Bunuwa Madugu Ibn Kaji.
Sabon Sarkin na Gudi, Ismaila Ahmed Gadaka, ya shahara da ƙwarewa a fannoni da dama.
Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin NajeriyaYa taɓa zama ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Fika/Fune daga 2011 zuwa 2019, kuma kafin nan ya yi aiki a matsayin Kwamishina a Jihar Yobe daga 2007 zuwa 2010.
Gadaka, ƙwararren ma’aikacin banki ne, inda ya yi aiki da bankuna irin su UBA da Standard Trust Bank, inda ya kai matsayin Manajan Kasuwanci.
Kafin naɗa shi Sarki, ya riƙe sarautar Yariman Gudi, a masarautar.
Yanzu haka, yana shugabantar hukumar gudanarwar Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Yawuri, a Jihar Kebbi, da kuma Kwamitin Kula da Ayyukan Gwamnatin a Ƙananan hukumomin Jihar Yobe tun daga 2024.
Gwamna Buni, ya bayyana cewa yana da tabbacin sabon Sarkin zai kula da martabar masarautar Gudi, ya kuma tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan al’umma.
Ya kuma aike da saƙon ta’aziyyarsa ga masarautar Gudi da iyalan marigayi Sarkin, tare da taya sabon Sarkin murna bisa wannan sarauta da ya samu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Masarautar Gudi Sabon Sarki sabon Sarkin
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp