Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka
Published: 31st, March 2025 GMT
Har yanzu dai kisan wasu matafiya ’yan Arewa da aka yi a garin Uromi da ke Ƙaramar Hukumar Arewa maso Gabashin Esan na ci gaba da tayar da ƙura a faɗin Nijeriya.
A bayan nan ne wasu hotunan bidiyo da aka yaɗa a shafukan sada zumunta suka nuna wasu mutane ɗauke da makamai suna far wa matafiyan da suka taso daga Kudanci zuwa Arewacin Nijeriya.
Hotunan bidiyon sun nuna yadda aka yi wa waɗanda abin ya shafa jina-jina sannan aka cinna musu wuta suka ƙone ƙurmus.
Za mu tura tawaga ƙauyen Torankawa —Gwamnatin KanoGwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa zai tura tawaga ta musamman zuwa ƙauyen Torankawa domin jajanta wa iyalan mafarautan da aka kashe a Jihar Edo.
Hakan dai na ƙunshe ne cikin saƙonsa na barka da sallah kamar yadda mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a jiya Lahadi.
Wasu majiyoyi daga fadar Gwamnatin Kano ta ce ana kuma sa ran karɓar baƙuncin Gwamnan Edo domin jajanta wa gwamnatin da kuma iyalan waɗanda lamarin ya shafa.
Al’ummar Edo a Kano sun yi Allah wadai da lamarinƘungiyar mazauna Edo da ke Jihar Kano ta yi tir da faruwar lamarin, tana mai neman da a bi wa waɗanda lamarin ya shafa haƙƙinsu.
Wata sanarwa da mai magana da yawun ƙungiyar , Mista Philip Tomon ya fitar, ya jajanta wa iyalan mafarautan da aka yi wa kisan gillar yana mai kiran mahukunta da su tabbatar an yi adalci a lamarin.
Ƙungiyar Mafarauta ta jingine zanga-zangaA wata sanarwa da Sakataren Ƙungiyar Mafarautan Kano, Usman Mu’azu Abdullahi Yakasai ya fitar, ya ce sun jingine zanga-zangar da suka shirya gudanarwa.
Sai dai sakataren wanda aka fi sani da Alaska duk da tana cikin alhini ta jingine zanga-zangar ce bayan tuntuɓe-tuntuɓen da ta yi, inda ta miƙa wa Gwamnatin Kano ƙorafi a hukumance na neman yi wa waɗanda aka kashe adalci.
Alaska ya ce ƙungiyar ta gamsu da irin matakan da ake ɗauka wajen tunkarar lamarin, kuma tana fatan doka za ta yi aiki yadda ya kamata.
Gwmanan Edo a Najeriya, Monday Okpebholo, ya dakatar da Kwamandan Rundunar Samar da Tsaro a jihar Friday Ibadin, biyo bayan kisan da aka yi wa mafarauta 16 ƴan asalin yankin arewacin kasar a alhamis da ta gabata.
SWannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Umar Musa Ikhilor ya fitar mai cewa an ɗauki matakin ne la’akari da bayanan da ke ƙunshe a rahoton binciken farko da aka gudanar dangane da wannan lamari, wanda ya yi matuƙar girgiza jama’a a Najeriya.
‘’ Lura da abubuwan da suka faru a ranar ta 27 ga watan Maris na 2025 a garin Uromi na ƙaramar hukumar Esan, inda aka samu asarar rayukan wasu matafiya, Mai Girma gwamna Monday Okpebholo, ya bayar da umurnin dakatar CP mai ritaye Friday Ibadin, Kwamandan Rundunar Samar da Tsaro ta jihar daga matsayinsa,’’ a cewar sanawar.
An rusa duk ƙungiyoyin ’yan bangar da ba su da rajistaHar ila yau, sanarwar da Sakataren Gwamnatin jihar ta Edo ya fitar ta ƙara da cewa an rusa ilahirin ƙungiyoyin ’yan banga da ba su da rajista a jihar, biyo bayan wannan kisa.
Sanarwar ta ci gaba da cewa ’yan bangar da suka aikata wannan ta’asa, suna aiki ne ƙarƙashin inuwar wata ƙungiya da ba ta da rajista, saboda haka ya zaman wajibi a ɗauki wannan mataki don tabbatar da samar da yanayi na tsaro a jihar.
Mahukuntan Edo na tattaunawa da takwarorinsu na Kano kan lamarinYanzu haka ana ci gaba da bincike dangane da wannan lamari, kuma tuni aka kama mutane 14 da ake zargi, yayin da ake farauta wasu mutane da dana da suka arce kamar dai yadda Babban Sufeton ’yan sandan Nijeriya ya bayar da umarni.
Gwamnatin Edo ta ce tana ci gaba da tattaunawa da dangin marigayan, da kuma mahukuntan jihar Kano, lura da cewa mafi yawan ’yan asalin jihar ne, tare da ɗaukar alƙawarin cewa za a tabbatar da adalci ta hanyar hukunta waɗanda aka sama da laifi.
Bayanan da suka fito fili bayan faruwar wannan lamari, sun tabbatar da cewa mafarautan sun fito ne daga Fatakwal da ke Jihar Ribas a hanyarsu ta zuwa Kano domin yin bukukuwan sallah a cikin iyalansu.
Ya zama dole a hukunta masu laifi a lamarin — CANƘungiyar Kiristoci a Najeriya (CAN) ta yi tir da Allah wadai dangane da kisan da aka yi wa mafarauta 16 a lokacin da suke ratsa jihar Edo a hanyarsu ta komawa a arewacin ƙasar.
A sanarwar da ta fitar ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar Archbishop Daniel Okoh a ranar Lahadi, da farko CAN ta isar da saƙon nuna alhini zuwa ga ƴan uwa da aminan waɗanda suka rasa rayukansu, daga nan kuma ta yi kira ga mahukunta da su ɗauki matakan da suka wajaba domin tabbatar da cewa ana aiki da doka da kuma cusa wa jama’a ra’ayin yarda da tsarin shari’a na ƙasar.
Daga nan sai sanarwar ta ce ‘’alhaki ya rataya a wuyan gwamnati domin tabbatar da cewa an gudanar da bincike da nufin hukunta waɗanda ke da hannu a wannan lamari da za a iya bayyana shi a matsayin mummunan cin zarafin bil Adama’’.
Har ila Ƙungiyar ta Kiristocin Najeriya ta isar da saƙon taya murna ga al’ummar Musulmi dangane da bukukuwan sallar da suke yi bayan sun kammala azumin watan Ramadan.
Ƙungiyar Amnesty International mai fafatikar kare haƙƙin ɗan Adam ta ce dole binciken da za a yi, ya zama sanadiyar hukunta waɗanda suke da hannu a kisa tare da ƙona matafiya ’yan arewa da aka yi a garin Uromi da ke Jihar Edo.
Shugaban ƙungiyar a Nijeriya, Isa Sanusi ne ya bayyana haka, inda, “dole hukumomin Najeriya su tabbatar an gudanar da bincike a bayyane, sannan kuma binciken ya zama silar adalci ga waɗanda aka kashe da iyalansu.
“Ya kamata a riƙa bayyana yadda binciken ke gudana tun daga farko har zuwa lokacin yanke hukunci.”
Amnesty ta ce abin da ya faru Uromi na nuna yadda ake ƙara samun ƙungiyar ’yan sa-kai na garuruwan da suke kusa da manyan hanyoyi suke tare hanyoyin suna aikata ba daidai ba.
“Yadda aka daɗe ana irin waɗannan kashe-kashen na nuna akwai gazawar gwamnati wajen kare rayukan al’ummarta.”
Isa Sanusi ya ƙara da cewa Amnesty ta yi Allah wadai da kisan, sannan ya sake nanata kiransu ga gwamnatin Najeriya da ta ɗauki matakin da ya dace.
Dole a kawo ƙarshen kisan gillar da ake yi wa ’yan ArewaƘungiyar dattawan arewa ta magantu kan kisan matafiya ƴan yankin arewa da aka yi a garin Uromi da ke jihar Edo, inda ta ce yankin arewa ya daɗe yana haƙuri da cin kashin da ake yi masa, amma kuma an kusa ƙure su.
Ƙungiyar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da kakakinta, Farfesa Abubakar Jika Jiddere ya fitar.
Sanarwar ta ce, “dattawan arewa sun damu matuƙa da kisan dabbanci da rashin tausayi da aka yi wasu mafarauta ƴan arewa da suke hanyarsu ta komawa gida arewa domin bikin sallah. Muna Allah wadai da wannan aika-aikar.
“Mun daɗe muna haƙuri da irin wannan cin kashin da ake mana a kudancin Nijeriya. Dole a kawo ƙarshensa haka,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa dole a kama waɗanda suka aikata laifin, sannan a musu hukunci a bayyane.
“Sannan dole a biya diyyar waɗanda aka kashe kamar yadda yake a addinance, sannan dole gwamnatin Edo ta fito ta bayar da haƙuri.”
Dattawan sun kuma buƙaci gwamnatin tarayya da ta Edo ta cika waɗannan buƙatun nan da kwana da 14, “idan kuma ba a ga wani mataki ba zuwa lokacin, dattawan arewa za su yi amfani da duk matakan da suka dace wajen bin haƙƙin ƴaƴanta da aka kashe.”
A bi mana haƙƙi — ’Yan uwaWakilan Aminiya sun ziyarci ƙauyen Torankawa da ke Ƙaramar Hukumar Bunkure a Jihar Kano, inda suka zanta da wasu daga cikin iyalan mafarautan da aka kashe.
Wasu daga cikin iyalan mafarautan kuma mazauna ne a ƙauyukan ƙananan hukumomin Garko, Kibiya da Rano da ke Jihar Kanon.
Tun dai bayan samun labarin faruwar lamarin ne mazauna ƙauyen Torankawa da aka sansu da sana’ar farauta suka shiga cikin alhinin da suka ce ba su taɓa faɗawa makamancinsa ba.
Shida daga cikin mafarautan da aka kashe da wani ɗaya da ya tsallake rijiya da baya sun fito ne daga ƙauyen.
Daga cikin mamatan akwai Abdulkadir Umar, wanda ya rasu ya bar mata biyu da mahaifiyarsa.
Sai kuma Zahraddeen Tanko wanda ya bar mata ɗaya da ’ya’ya huɗu da kuma Haruna Hamidan wanda shi ma ya rasu ya bar mata ɗaya da ’ya’ya huɗu.
Akwai kuma Usaini Musa wanda ya rasu ya bar mata biyu da ’ya’ya biyu da Abdullahi Harisu wanda ya yi aure watanni huɗu da suka gabata da kuma Ya’u Umaru da Abubakar Ado da ba su kai ga yin auren ba ma.
Duk ’yan uwan mamatan da Aminiya ta zanta da su sun bayyana alhini — wasunsu cikin hawaye suna roƙon mahukunta da su bi musu haƙƙinsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Edo Jihar Kano mafarauta Monday Okpebolo mafarautan da aka ƙauyen Torankawa iyalan mafarautan wata sanarwa da Allah wadai da wannan lamari a garin Uromi waɗanda aka da aka yi wa da ke jihar da ke Jihar ya bar mata tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
A tsayin wadannan shekarun, Nijeriya ta fuskanci kalubale da dama da suka hada da fafutukar tabbatar da mulkin dimokuradiyya, siyasar yanki, rikita- rikitar addini da kabilanci da kuma gagarumar matsalar tsaro daga Kudu zuwa Arewa.
Mafi yawan al’ummar Nijeriya na bayyana shekaru 26 na mulkin dimokuradiyya a matsayin shekarun gurbataccen mulki, shekarun mulkin danniya da zalunci, cin hanci da rashawa, tabarbarewar tsaro, rugujewar tattalin arziki kana shekaru 26 na satar danyen mai, rashin wutar lantarki, koma baya a sha’anin ilimi, aikin gona da rashin ayyukan yi tare da hauhawar farashin mai da tsadar rayuwa.
Akasin murnar wannan ranar, kungiyoyi a Arewa da Kudu, jam’iyyun siyasa, kungiyoyin farar hula da na matasa da dalibai sun bayyana ‘yan siyasa a matsayin matsalar da ta dabaibaye kasar nan ba wai tsarin aikin gwamnati ba.
A mabambantan bayan su kungiyar dattawan Arewa ta ACF, kungiyar Yarbawa ta Afenifere da Ohanaeze ta Inyamurai sun bayyana amfani, nasarori, illa da matsalolin mulkin dimokuradiyya.
Kungiyar dattawan Arewa ta ce matukar ‘yan siyasa ba su watsar da tsattsauran ra’ayin su na rikau, talakawa ba za su mori romon mulkin dimokuradiyya ba. Ita kuwa kungiyar Yarbawa ta bayyana kima da tasirin mulkin dimokuradiyya ga kasa da ‘yan kasa, sai dai duk da kasawarsa a wasu bangarori ta ce shine tsari mafi inganci ga ‘yan Nijeriya.
Sai dai kungiyar Inyamurai ta bayyana cewar babu wata mafita ta samar da ci-gaba a Nijeriya illa canza fasalin kasa domin a baiwa kowane yanki damar bunkasa tattalin arzikin sa.
Haka ma kungiyoyi da dama sun koka ga gwamnati a kan ta gaggauta shawo kan matsalolin tsadar rayuwa, rage farashin mai da bunkasa tattalin arziki wadanda suka zama silar jefa al’umma a cikin kunci musamman a dalilin cire tallafin man fetur da wasu tsare-tsaren gwamnati masu tsauri.
A cewarsu maimakon shagalin buki, kamata ya yi a yi zaman jajantawa juna kan gurbatacciyar hanyar da shugabannin kasar mabambanta suka hau na rashin ci-gaba akasin ingantacciyar hanyar da shugabannin baya wadanda suka jagoranci samarwa kasar ‘yanci suka dora ta a kai.
Da yawan mutane sun yi tunanin daga shekarar 1999 zuwa yau matsalolin da ake fuskanta za su kau amma sai a ka ga akasin hakan. Abubuwan da ke ciwa jama’a tuwo a kwarya musamman sha’anin samar da hasken wutar lantarki har yanzu ba a shawo kan matsalar ba duk da irin makuddan kudaden da a ka narkar wadanda a ke ganin bai kamata a ce har yanzu babu tsayayyiyar wutar lantarki a Nijeriya.
A ra’ayin wasu gwamnatoci a mataki-mataki sun taka rawar gani. Idan da a ce babu mulkin dimokuradiyya da ba za a samu ‘yancin fadar albarkacin baki ba wanda shi kansa ci-gaba ne.
Haka ma a cewar su idan aka kalli kauyukan kasar nan a kananan hukumomi 774 zuwa yau an samu ci-gaba domin a can baya ba haka suke ba. Sai dai tabbas ci-gaban ba yadda a ka zata ba ne. Watakila gwamnatocin ba su samu kudade yadda ya kamata ba, wasu kuma na kukan matsalar daga hannun shugabanni take.
Mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a tsayin wadannan shekaru mulki ne da ke cike da rudu da kwamacalar siyasa daban-daban. A wanann rahoton za mu gabatar da muhimman abubuwan da dama da suka faru a kowace gwamnatin dimokuradiyya daga Obasanjo, ‘Yar’Adua, Jonathan, Buhari zuwa Tinubu da ke jan zaren mulki a yau.
Abubuwan Tunawa A Gwamnatin Obasanjo (1999-2007)
A jiya da yau a kan tuna da Gwamnatin Obasanjo a 1999-2007 ta hanyar kafa Hukumomin Yaki da Almundana da Kudaden Al’umma (EFCC) da (ICPC) tare da karfafawa Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata domin yaki da cin hanci da rashawa. Gurbatattun ‘yan siyasa da mutane da dama sun shiga hannu tare da gurfana a kotu zuwa daurewa a kurkuku a wancan lokacin.
Wasu daga cikin nasarorin da za a iya cewa gwamnatin Obasanjo ta samarwa al’ummarta akwai rattaba hannun shigowa da kamfunan sadarwa wanda ya zama silar samar da wayoyin hannu na GSM wanda daga lokacin zuwa yau kusan babu wani gida a Nijeriya da ba a mallakin wayar tafi-da-gidanka ba.
Gwamnatin Obasanjo wadda aka samu tabarbarewar tsaro da rikita- riikitar kabilanci a mulkinsa haka ma a mulkin sa an shaidi yawaitar faduwar jiragen sama ciki har da jirgin ADC wanda ya dauki rayuwar Sarkin Musulmi Muhammadu Maccido da muhimman mutane a 2006.
Gwamnatin Obasanjo ta yi matukar kokarin samarwa Nijeriya afuwar bashin zunzurutun kudi har dala Biliyan 18 daga Paris da London wanda ya jima yana ciwa kasar nan tuwo a kwarya.
Bugu da kari a zamanin mulkin Obasanjo ne siyasar ko- a- mutu- ko- a- yi-rai ta samu gindin zama ta yadda aka rika sarawa ko babu gaba ga duk wani ko wadanda suka yi kokarin shiga gona ko huruminsa. Obasanjo a 2007 a kokarin sharewa marigayi ‘Yar’Adua hanyar zama shugaban kasa, ya jagoranci gudanar da kazamin zabe mafi muni a Nijeriya wanda ke cike da aika-aika da murdiyar zabe.
Haka ma Obasanjo ya so yi wa mulkin dimokuradiyya fyade a yayin neman zarcewa saman mulki a wa’adi na uku lamarin da ‘yan Nijeriya suka sa kafa suka shure tare da Allah-wadai kan kokarin yin karan tsaye ga kundin tsarin mulkin kasa, abin da ya kawo karshen bukatarsa wadda hakarsa ta kasa cimma ruwa.
Umaru ‘Yar’Adua (2007-2010)
Umaru Musa ‘Yar’Adua shine shugaban Nijeriya daga Mayu 2007 zuwa 5 ga Mayu 2010 a lokacin da ya yi bankwana da duniya yana a saman mulki.
‘Yar’Adua ne shugaban kasa na farko a tarihi da ya fara bayyana kadarorin da ya mallaka a bayyane tun kafin ya shiga ofis. Haka ma a fili ya fito ya bayyanawa duniya cewar zaben da ya kawo shi saman mulki cike yake da ta’addanci, murdiya da sabawa dokokin zabe.
Haka ma gwamnatin Matawallen na Katsina ta taka rawar gani wajen rage farashin man fetur daga farashin da yake akai zuwa naira 65 a kowace lita. Dukkanin gwamnatocin baya kara farashin mai suke yi, ita kuwa ta ‘Yar’Adua saukar da farashin ta yi. Kazalika takaitacciyar gwamnatin ‘Yar’Adua wadda ba ta yi tsawon rai ba ta cancanci a yaba mata wajen kawo gyara ga dokokin zabe.
Baya ga wannan a mulkinsa ba za a manta da yadda ya sa kafa ya sabawa tsarin mulki wajen rashin hannuntawa mataimakinsa Jonathan ragamar mulki ba a yayin da ya bar kasa zuwa duba lafiyarsa a Saudi Arabiya. Sai dai ‘yan Nijeriya masu kishi da hangen nesa sun tashi tsaye suka jagoranci gyara babbar matsalar tare da tabbatar da zaman Jonathan a matsayin mukaddashin shugaban kasa.
Haka ma gwamnatin ‘Yar’Adua ta samu nasarar kawo karshen ta’addancin tsagerun yankin Neja-Delta da ke talauta kasa ta hanyar yi masu afuwa suka ajiye mukamai tare da tallafa masu a shirin musamman wanda a lokacin ya kawo karshen ta’addanci a yankin mai albarkar man fetur.
Goodluck Jonathan (2010-2015)
A zamanin gwamnatin Jonathan ‘yan ta’addan Boko-Haram sun ci karensu ba babbaka ta yadda al’ummar kasa suka rika bacci da ido daya a gwamnatin Jonathan wanda shine shugaban kasa na farko da ya fito daga yankin Kudu-Maso-Kudu.
Sace ‘yan matan Chibok 100 da mayakan Boko-Haram suka yi awon gaba da su a makarantar mata a Jihar Borno a Afrilu 2014 lamari ne da ya yi matukar jan hankalin al’ummar ciki da wajen kasar nan.
Jonathan ya zama shugaban kasa na farko a tarihi kasar nan da ya sha kasa a zabe yana kan gadon mulki. Fitowa fili da ya yi ya karbi faduwa zabe tare da taya Muhammadu Buhari murna ya daga darajarsa da samar masa kima da dattako tare da tabbatar da karfin mulkin dimokuradiyya.
Muhammadu Buhari (2015- 2023)
Muhammadu Buhari wanda ya zama shugaban kasa a 2015 bayan ya sha kaye a zabukan 2003, 2007 da 2011, ya sake lashe zaben 2019 da gagarumar nasara.
Gwamnatin Buhari wadda ta yi kaurin suna wajen yekuwar yaki da cin hanci da rashawa, ta fadi kasa warwas ta hanyar kasa magance yawaitar cin hanci a fannoni da dama lamarin da jama’a ke ganin batun yaki da cin hanci suna ne kawai a gwamnatin Buhari domin kuwa a yayin da ake gurfanar da magoya bayan PDP a kotu, takwarorinsu na APC suna ci-gaba da cin karensu ba babbbaka a matsayin shafaffu da mai.
Bugu da kari gwamnatin Buhari ta kasance ta farko a dimokuradiyyar kasar nan da ta rika kawar da kai ga mutunta kundin tsarin mulkin kasa ta hanyar katsalandan ga sashen shari’a da rashin mutunta umurnin kotuna.
Misali kotuna daya bayan daya har guda tara sun bayar da belin Sambo Dasuki rsohon mashawarci na musamman kan sha’anin tsaro a gwamnatin Jonathan amma kuma gwamnatin Buhari ta kasa sakinsa a daurin da ta yi masa a kusan shekaru hudu kan badakalar kudin makamai.
A karkashin mulkin dimokuradiyya a zamanin Buhari al’ummar Nijeriya sun fuskanci yawaitar kisan gilla, garkuwa da mutane da ta’addancin Fulani fiye da kowane lokaci gabaninsa wanda bakidaya al’umma musamman a yankin Arewa suke cikin zullumi da fargaba. Haka ma Buhari zai ci-gaba da zama a cikin tarihi a matsayin shugaban kasa da ya kwashe kwanaki 217 wajen duba lafiyarsa a wajen kasar nan.
Bola Tinubu 2023-
A shekaru biyu na mulkin Bola Ahmad Tinubu al’ummar kasa na kuka da kokawa da tsare- tsare da manufofin gwamnatinsa masu tsauri ta yadda da yawa ke kewa da kwadayin mulkin PDP wanda rayuwa ke da sauki a mulkin ta.
Cire tallafin man fetur da Tinubu ya yi a jawabinsa na karbar mulki a 2023 shine babban abin da ya dauki hankalin jama’a tare da girgiza su musamman bisa ga radadi da kuncin da matakin ya jefa kasa da ‘yan kasa a ciki wanda ya haddasa tsada da karancin man fetur a lokaci daya.
Ya zuwa yanzu al’umma na cike da kunci a dalilin hauhawar farashin dukkanin abubuwan da rai ke bukata ta yadda abubuwa da dama musamman abinci ke gagarar talaka.
Duk da cewar farashin abinci yana tashi sama a fadin kasa a tsayin shekaru, amma yanayin a wannan lokacin ya ta’azzara ne sosai a bisa ga illar shiraruwan gwamnati musamman cire tallafin man fetur, faduwar darajar naira da sauransu.
Karuwar Talauci
Al’ummar Nijeriya da ke fama da talauci a zamanin gwamnafin da ta gabata sun kara talaucewa sosai a cikin shekaru biyu na mulkin Tinubu ta yadda a yau suke zumudin zuwan lokacin zabe.
Tsananin talaucin da al’umma ke fama da shi a yanzu, ya sa mafi yawan jama’a kasancewa cikin kuka da kokawa da yadda mulkin Tinubu ya zo masu wanda a baya suke fatar samun saukin al’amurra bayan karewar gwamnatin da ta gabata, amma sai gashi talaucin da ake fama da shi a yanzu ya fi na baya tsanani.
Matsalolin Tsaro
Duk da matakan da gwamnati ke dauka na kokarin samar da ingantaccen tsaro har zuwa yanzu ‘yan ta’adda na ci-gaba da cin karensu ba babbaka ta yadda suke hanawa al’umma bacci da idanu biyu wanda kasawa ce karara ga gwamnati a shekaru 26 na mulkin dimokuradiyya amma a kullum tsaron kasa kara tabarbarewa yake yi.
A yayin jin ra’ayin mabanbantan al’ummar kasa daga Arewa har Kudu kan amfani da alfanun da suka amfana da shi na romon mulkin dimokuradiyya, da yawa daga ciki sun bayyana shekaru 26 na dimokuradiyya a Nijeriya a matsayin shekarun gurbatacciyar dimokuradiyya, mulkin fatara da talauci, mulkin rikice-rikice da tashe-tashen hankula.
Bugu da kari jama’a sun fassara 26 a matsayin shekarun cin hanci da rashawa, shekarun sata da wawashe kudaden al’umma, kazalika shekarun karawa masu karfi karfi da kuma ci- da gumin talaka.
A kan wannan karara a yayin da wasu ke bayyana mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a matsayin wata hular baka ce wasu kuwa cewa suke yi Shekaru 26 Na Mulkin Dimokuradiyya A Nijeriya: Da Dadi, Ba Badi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp