HausaTv:
2025-11-14@20:03:14 GMT

Sabon Shugaban Kasar Gabon Ya Bayyana Shiransa Na Kawo Sauyi Mai Kyau A kasar

Published: 15th, April 2025 GMT

Bayan da hukumar zaben kasar Gabon ta tabbatar da nasarar da Brice Oligui yayi a zaben shugaban kasa na karshen makon da ya gabata, shugaban ya gabatar da jawabinsa na farko ga mutanen kasar, inda ya bayyana masu kan cewa, babu jin dadi sai tare da wahala.

Shafin tanar gizo na labarai ‘Africa News” ya nakalto shugaban yana cewa muhimman al-amuran da zai sa a gaban a shugabancin kasar sun hada da sauya tsarin tattalin arzikin kasar daga dogaro da man fetur zuwa harkokin kasuwanci,  har’ila yau zai yaki cin hanci da rashawa.

Brice ya ce, ya zo ne a matsayin mai gina kasa, kuma yana son taimakon su don samun nasara a wannan gagarum,in aikin.

A ranar lahadin da ta gabata ce hukumar zaben kasar Gabaon ta bada sakamakon zaben shugaban kasa wanda aka gudanar a ranar Asabar wanda ya nuna cewa masu zabe a kasar sun zabi Brice a matsayin shugaban kasa tare da samun kasha 90.4% na yawan kuri’un da aka kada, kuma yawan mutanen da suka fito kara kuri’un ya kai kasha 74%.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake nada Birgediya-Janar Mohammed Buba Marwa (mai ritaya) a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) na tsawon shekaru biyar masu zuwa.

Bayo Onanuga, Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labaru, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Juma’a.

An kama ’yan Najeriya 3 a Kenya kan zargin aikata damfara Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030

An fara nada Marwa a watan Janairu 2021 ta hannun

Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari ne ya fara naɗa Buba Marwa a muƙamin a watan Janairun 2021, bayan ya jagoranci Kwamitin Shugaban Kasa na Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi daga shekarar 2018 zuwa Disamba 2020.

Sabon nadin na nufin tsohon hafsan soja dan asalin jihar Adamawa zai ci gaba da rike mukamin har zuwa shekarar 2031.

Marwa, wanda ya taba zama gwamnan soja na jihohin Legas da Borno, ya kammala karatu a Makarantar Soja ta Najeriya da kuma Kwalejin Tsaro ta Najeriya (NDA).

Bayan ya zama cikakken soja a shekarar 1973, Marwa ya yi aiki a matsayin babban jami’in 23 Armoured Brigade, ya kasance babban dogari ga tsohon Babban Hafsan Soja, Laftanar-Janar Theophilus Danjuma, sannan ya yi aiki a matsayin Magatakardar Kwalejin Tsaro ta Najeriya.

Haka kuma ya yi aiki a matsayin Mataimakin Mashawarci kan Tsaro a Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Washington DC, daga baya kuma ya zama Mashawarci kan Tsaro a Ofishin Jakadan Najeriya na Dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.

Zaman Marwa a NDLEA ya yi fice wajen kama masu fataucin miyagun kwayoyi, inda aka cafke sama da mutane 73,000 da ke harkar fatauci da kuma kwace fiye da tan miliyan 15 na miyagun kwayoyi iri-iri.

A karkashin jagorancinsa, hukumar ta kaddamar da gangamin yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a faɗin Najeriya.

Shugaba Tinubu ya ce: “Sake nadinka alamar amincewa ce da kokarinka na kawar da kasar nan daga annobar fatauci da shan miyagun kwayoyi. Ina rokonka kada ka yi kasa a gwiwa wajen bin diddigin ’yan kasuwar miyagun kwayoyi da ke neman lalata al’ummarmu, musamman matasa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA
  • Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka
  • Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya  ( IEA)  Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji
  • Shugaban Karamar Hukumar Nasarawa Ya Yi Kira Ga Jama’a Su Yi Rijista Kuma Su Karɓi Katin Zaɓe
  • Iraki: Hukumar Zabe Ta Fara Sanar Da Sakamakon Farko Na Babban Zaben Da Aka Gudanar
  • Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
  • Gabon: An Daure Mata Da ‘Dan  Tsohon Shugaban Kasa Bongo Shekaru 20 A Gidan Yari
  • An Bayyana Ranar Karshe Ta Biyan Kudin Aikin Hajji Mai Zuwa