HausaTv:
2025-07-12@09:10:11 GMT

Sabon Shugaban Kasar Gabon Ya Bayyana Shiransa Na Kawo Sauyi Mai Kyau A kasar

Published: 15th, April 2025 GMT

Bayan da hukumar zaben kasar Gabon ta tabbatar da nasarar da Brice Oligui yayi a zaben shugaban kasa na karshen makon da ya gabata, shugaban ya gabatar da jawabinsa na farko ga mutanen kasar, inda ya bayyana masu kan cewa, babu jin dadi sai tare da wahala.

Shafin tanar gizo na labarai ‘Africa News” ya nakalto shugaban yana cewa muhimman al-amuran da zai sa a gaban a shugabancin kasar sun hada da sauya tsarin tattalin arzikin kasar daga dogaro da man fetur zuwa harkokin kasuwanci,  har’ila yau zai yaki cin hanci da rashawa.

Brice ya ce, ya zo ne a matsayin mai gina kasa, kuma yana son taimakon su don samun nasara a wannan gagarum,in aikin.

A ranar lahadin da ta gabata ce hukumar zaben kasar Gabaon ta bada sakamakon zaben shugaban kasa wanda aka gudanar a ranar Asabar wanda ya nuna cewa masu zabe a kasar sun zabi Brice a matsayin shugaban kasa tare da samun kasha 90.4% na yawan kuri’un da aka kada, kuma yawan mutanen da suka fito kara kuri’un ya kai kasha 74%.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu

Hukumar hana fasa ƙwauri ta Najeriya (Kwastam), ta ce ta kama wata mota da ke ɗauke da wata kontena maƙare da mazaƙutar jakai a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Hukumar ta Kwastam ta sanar da kama motar ne a ranar Alhamis.

Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos

An gano waɗanda suka yi safarar ne da ake zargin suna shirin fitar da shi zuwa ƙasashen waje ba bisa ƙa’ida ba.

An samu nasarar ne a ranar Juma’a 5 ga watan Yuni, 2025, da misalin ƙarfe 9 na dare, bayan wani haɗin gwiwa da jami’an ofishin kula da namun daji na musamman da na hukumar Kwastam suka gudanar.

Kwaturola Janar na Hukumar kwastam, Mista Adewale Adeniyi ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja ranar Alhamis.

Maimagana da yawun hukumar ta Kwastam, Abdullahi Aliyu Maiwada wanda ya wakilci Kwanturola Janar na Kwastam ya bayyana cewa, nasarar kama masu aikata hakan na cikin ƙoƙarin da ake yi na daƙile kasuwancin dabbobin dawa ta ɓarauniyar hanya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi
  • 2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
  • Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025
  • Malaman Jihar Jigawa Sun Karrama Shugaban Hukumar Alhazai Ta Jihar
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Shugaban Yahudawan Iran Ya Tuhumi Isra’ila Da Fakewa A Karkashin Addini
  • Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha
  • An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN