HausaTv:
2025-12-14@00:38:50 GMT

An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya

Published: 15th, April 2025 GMT

Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.

Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai  harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.

Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.

Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.

Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna  kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara

Daga Usman Muhammad Zaria

Shugaban kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bukaci ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar  tabbatar da ganin cewa kananan hukumonin jihar 27 sun wallafa cikakken kundin kasafin kudadensu cikin zangon farko na sabuwar shekara.

Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa, ya bayyana haka ne lokacin tantance kiyasin kasafin kudin sabuwar shekara na ma’aikatar kananan hukumomi.

Ya kuma yi kira ga ma’aikatar da ta duba batun rashin biyan albashi ga wasu daga cikin nadaddun kansiloli, kasancewar yanzu haka akwai nadaddun kansiloli 21 da ba sa samun albashin su.

Ya kara da cewar, kwamitin ya samu koke kan tsallake albashin wasu ma’aikatan kananan hukumomi sakamakon aikin tantance ma’aikata na IPPS  ta yadda wasu ma’aikatan sun yi ritaya ba tare sun karbi albashin da aka tsallake su ba.

A nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar kananan hikumomin Jihar, Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa, ya bada tabbacin yin duk abinda ya kamata domin magance wadannan batutuwa.

Ya ce ma’aikatar ta yi kiyasin kashe naira miliyan dubu 13 domin gudanar da manyan ayyuka da harkokin yau da kullum a shekarar 2026.

Hannun Giwa, ya kuma bayyana cewar daga cikin manyan ayyuka akwai gyaran ofisoshin shiyya na jami’an duba kananan hukumomi guda 7.

Yana mai cewar za’a kuma kammala aikin ginin sabbin ofisoshi dake kananan hukumomin Babura da Kafin Hausa.

Kazalika, Kwamishinan ya ce za’a sayi motocin aiki da babura ga jami’an duba kananan hukimomi da mataimakansu, tare da kudaden gudanarwa domin ziyarar aiki a lungu da sakon kananan hukumomin jihar 27.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Ma’aikatar Ilimi ta Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 18 a 2026
  • Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC