HausaTv:
2025-04-26@04:53:51 GMT

An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya

Published: 15th, April 2025 GMT

Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.

Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai  harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.

Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.

Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.

Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna  kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Musanta Zargin Nethalands Na Cewa Tana Da Hannun A Kokarin Kisa A Kasar

Ofishin jakadancin kasar Iran a kasar Netherlands ta yi watsi da zargin da gwamnatin kasar takewa JMI na kokarin aiwatar da kashe-kashe har guda biyu a shekarar da ta gabata.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran tace Ofishin jakadancin Iran da ke Netherlands  ta fidda wannan sanarwan ne a jiya Alhamis. Ta kuma kara da cewa, kasar Iran wacce ta fi ko wace kasa a duniya fama da yan ta’adda, ba za ta yi kokarin kasashe wani a wani wuri ba.

Sanarwan ta bayyana cewa wannan al-amarin siyasace ta tsakanin jami’an siyasa na kasar ta Netherlands  don neman amincewar masu kuri’a.

Kafin haka dai wata cibiyar ayyukan tsaro ta kasar Netherlands  mai suna AIVD ta bada rahotomta na shekara shekara kan abinda ya shafi ayyukan ta’addancin inda ta ammabi kasar Iran a ciki.

Har’ila yau wannan rahoton yasa ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Netherlands  ta kira jakadan JMI a kasar zuwa ma’aikatar harkokin wajen kasar don gabatar da korafinta.

Gwamnatocin kasashen Turai musamman kasar Faransa tana gudanar da taron yan adawa da JMI a kasashensu, wadanda kuma sune suka kashe Iraniyawa da dama a farko-farkon nasarar juyin juya halin musulunci a kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe
  • Jigawa Ta Bude Sabon Babi: Maniyyata Za Su San Masaukansu Tun Daga Gida Najeriya
  • Iran Ta Musanta Zargin Nethalands Na Cewa Tana Da Hannun A Kokarin Kisa A Kasar
  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • ’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa 
  • Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 47 A Birnin El-Fasher Fadar Mulkin Darfur Ta Arewa
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi Da Dabbobi 4 A Wani Hari A Filato