HausaTv:
2025-12-08@16:56:57 GMT

An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya

Published: 15th, April 2025 GMT

Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.

Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai  harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.

Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.

Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.

Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna  kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada

Rahotannin da suke fitowa daga  DRC sun ce fadan ya barke ne dai bayan kwanaki kadan da gwamatin DRC da ta Rwanda su ka amince da tabbatar da zaman lafiya.

A can gabashin kasar an ga dubban mutane maza, mata, da kananan yara suka dauke da kayayyakinsu a lokacin da suke ficewa daga kauyukna da suke gundunar Kivu ta kudu,saboda kaucewa sabon fadan da ya barke a tsakanin sojojin kasar da na ‘yan tawayen kungiyar M23.

A jiya Asabar ne sabon fadan ya barke saboda bama-baman da ake amfani da su wajen kai hare-haren a tsakanin bangarorin biyu da suke fada da juna.

Wani mutum da yake gudu daga garin Luvungi ya fada wa cibiyar watsa labaru ta “Afirka Today” cewa; Kungiyar M23 da kuma sojojin Congo suna ta jefa bama-bamai akan garuruwan Luvungi, Mulumbulwa da Gabriel.”

Haka nan kuma ya ce; A cikin kwanaki biyu da su ka gabata fadan ya haddasa kashe mutane da dama. Kuma an kashe makwabtansa, shi ya sa ya yanke shawarar ficewa.

Wasu daga cikin yankunan da fadan ya shafa da akwai garuruwan Katogota da Kamanyola da yankunan da suke zagaye da su.

Barkwar sabon fadan dai ya zo ne kwana daya bayan da aka yi tsammanin zaman lafiya zai dawo saboda yadda gwamnatin kasar ta DRC da kuma Rwanda su ka bayyana amincewa da shimfida zaman lafiya a yankin.

Albarkatun ma’adanai da Allah ya huwacewa kasar DRC, musamman a gabashinta, da yadda manyan kamfanonin waje da kasashen makwabtaka suke da kwadayin ne yake jawawa kasar yake-yake,tun da ta sami ‘yanci daga kasar Belgium.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurumin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi December 6, 2025   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika December 6, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi December 6, 2025 Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabo Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi
  •  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada
  • Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Dorinar Ruwa ta Yi Ajalin Mutane Biyu, ta Raunata Shida a Gombe
  • Dorinar ruwa ta kashe mutum 2, ta jikkata 6 a Gombe