An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya
Published: 15th, April 2025 GMT
Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.
Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.
Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.
Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.
Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
Dubban mutane sun taru a Jihar Bauchi, don halartar jana’izar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya rasu a ranar Alhamis a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa.
Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ayyana ranar Juma’a a matsayin ranar hutu domin ba jama’a damar halartar jana’izar malamin.
Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka CAF Tayi Watsi Da Alƙalan Wasan Nijeriya a Kofin Afrika Na 2025Ɗalibansa da sauran Musulmi daga Bauchi da maƙwabtan jihohi sun isa da wuri domin halartar jana’izar.
Huumomi sun tsaurara matakai a jihar don tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali.
Maulud Dahiru Bauchi, wanda ya yi magana a madadin iyalan marigayin, ya ce za a yi jana’izar malamin da misalin ƙarfe 3 na rana bisa wasiyyar malamin.
Ya ƙara da cewa Sheikh Sharif Saleh ne zai jagoranci jana’izar.
Jama’a da dama sun halarta, ciki har da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, gwamnoni, sarakuna, ’yan kasuwa, attajirai da sauransu.
Iyalan mamacin sun ce dandazon mutanen da suka halarci jana’izar, ya nuna tasirin da Sheikh Dahiru ya yi wajen yaɗa addini da tarbiyya tsawon rayuwarsa.