An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya
Published: 15th, April 2025 GMT
Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.
Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.
Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.
Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.
Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
Daga Bello Wakili
Najeriya ta ƙarfafa ƙoƙarinta na kawar da cutar HIV nan da shekarar 2030, inda Uwargidar Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kira ga ’yan Najeriya, shugabanni da jami’an lafiya su haɗa hannu wajen cimma wannan manufa.
Yayin jawabi a bikin ranar Yaki da Cutar AIDS ta Duniya ta 2025 da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu ta jaddada cewa za a iya kawar da cutar HIV a Najeriya idan aka ci gaba da yin aiki cikin tsari, haɗin kai da kuma samun tallafi.
Ta ce duk da cewa an samu cigaba a fannoni na rigakafi, magani da kulawa, ana buƙatar ci gaba da dagewa domin tabbatar da cewa kowane ɗan Najeriya na samun kariya.
Ta yi nuni da muhimmancin yaki da wariya, hantara da nuna bambanci, abubuwan da har yanzu ke hana mutane neman taimako.
Ta kuma jaddada aikin da ake yi a matakin ƙasa na dakile yaduwar cutar daga uwa zuwa jariri, faɗaɗa magungunan yara masu dauke da HIV, da dorewar shirye-shiryen al’amuran da suka shafi cutar ta HIV a cikin gida.
Uwargidar Shugaban Ƙasar ta yabawa Shirin Ƙasa na Yaƙi da Cutar AIDS da STDs saboda ci gaban da aka samu, tare da tallafin Global Fund.
Oluremi Tinubu ta lura cewa ko da yake masu tallafawa daga waje na taka muhimmiyar rawa, gwamnatin tarayya ta amince da dala miliyan 200 domin ƙarfafa shirye-shiryen HIV, tarin fuka da zazzabin cizon sauro.
Ta kuma yaba wa cigaban da Hukumar Kula da Cutar HIV ta Kasa (NACA) ke samu wajen haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi domin tabbatar da dogon tsari da ɗorewar shirin ƙasa na dakile cutar ta HIV.