HausaTv:
2025-12-02@17:40:09 GMT

An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya

Published: 15th, April 2025 GMT

Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.

Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai  harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.

Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.

Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.

Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna  kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026

Daga Usman Muhammad Zaria 

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ya zuwa yanzu ta mayar da sama da naira miliyan 50 ga maniyyatan jihar na shekarar 2026, biyo bayan rage kudin kujerar aikin Hajji da Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar.

Daraktan Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, an mayar da kudaden ga maniyyatan da suka riga suka biya kudin kujerunsu ga hukumar kafin a rage farashin.

Ahmed Labbo ya ce NAHCON ta sake fasalin kudin Hajj na Yankin Arewa wanda yanzu ya kai sama da naira miliyan 7 da dubu 600 yana mai jaddada cewa mayar da kudin umarni ne daga Hukumar Alhazai ta Kasa, sakamakon gagarumin ragin da aka yi wa kujerar Hajjin shekarar 2026.

Ya jinjina wa jami’an hukumar na yankuna bisa kwazon tattara takardun  zuwa Hajj da bayanan maniyyata cikin sauri.

Yayin da yake magana kan shirye-shiryen aikin Hajjin 2026, Labbo ya bayyana cewa hukumar na aiki ba dare ba rana domin tabbatar da ingantattun tsare-tsare ga tawagar jihar a ƙasar Saudiyya.

Ya kuma yi kira ga maniyyata su tabbatar sun biya kudin kujerunsu kafin ko a ranar 24 ga Disamba, 2025.

Ahmed Labbo ya bayyana godiya ga Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da jajircewarsa ga hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa
  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano