HausaTv:
2025-07-05@22:14:19 GMT

An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya

Published: 15th, April 2025 GMT

Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.

Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai  harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.

Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.

Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.

Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna  kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce wahalhalu sun yi yawa a Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, wanda har ya sa mutane suka fara fatan dawowar tsohon Shugaba Muhammadu Buhari.

Yayin da yake magana a birnin Abuja, Amaechi ya ce Najeriya ta taɓarɓare matuƙa, inda ya ce sauyin gwamnati ne kawai zai magance matsaloli.

Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota

“Farashi kayayyaki ya tashi sosai. Mutane ba za su iya siyan abinci ba. Babu kuɗi. Komai ya lalace,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa rayuwa ta yi tsanani har mutane sun fara tunawa da zamanin Buhari da muradin dawowarsa kan mulki.

“Yanzu mutane na so Buhari ya dawo. A Najeriya, kowace sabuwar gwamnati tana ƙara muni fiye da ta baya. Wannan shi ne dalilin da ya sa mutane ke ci gaba da tunanin gwamnatin da ta gabata,” in ji shi.

Amaechi ya bayyana cewa ya fice daga jam’iyyar APC a daren ranar Talata, inda yanzu ya koma jam’iyyar haɗaka ta ADC.

Ya ce tuni ya daina shiga harkokin jam’iyyar APC tun da daɗewa.

“Na fice daga APC jiya da daddare. Ban halarci taro ko guda ɗaha ba. Na taɓa gargaɗinsu, kuma na rubuta musu kada su sake gayyatata. Ba za ka zauna cikin ƙungiyar da yawancinsu suke satar dukiya ba, kai kuma ka yi shiru,” in ji shi.

Da aka tambaye shi me ya sa yake sukar gwamnatin da ya taɓa yi wa aiki, Amaechi ya ce matsalar Najeriya ba kawai shugabanci ba ne, sai an gyara tsarin gaba ɗaya.

Ya ce akwai bukatar fara shiri, ba kawai kafa jam’iyya ba, wanda zai haɗa ‘yan Najeriya su ƙwato ƙasarsu da hannunsu.

Amaechi ya kuma ce bai taɓa ganin Tinubu a matsayin mutum wanda ya cancanci ya mulki Najeriya ba.

“Na taɓa cewa Tinubu ba shi da ɗabi’u shugabanci. Har yanzu ra’ayina kenan,” in ji shi.

Ya soki yadda gwamnati ke tafiyar da tattalin arziƙi, musamman faɗuwar darajar Naira.

“Lokacin Buhari, dala tana kusa da Naira 460 ko Naira 500. Yanzu ta kai Naira 1580. Wannan ya fi kashi 100,” in ji shi.

Da aka tambaye shi ko wannan matsala ta Naira wata dabara ce ta gwamnati, Amaechi musanta hakan.

Ya ce, “Ko dabara ce ko akasin haka, duk wata gwamnati da ba ta damu da rayuwar mutane ba, ba za a ce dabara ce mai kyau ba.”

Tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, shi ma ya fice daga jam’iyyar APC, inda ya bu sahun Amaechi wajen komawa jam’iyyar ADC.

Ficewarsu da wasu manyan jiga-jigan siyasa na nuni da juyin juya hali kafin babban zaɓen 2027, yayin da jam’iyyar ADC ke neman zama sabuwar babbar jam’iyyar adawa a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matashi ya kashe mahaifinsa da sanda a Jihar Bauchi
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
  • SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta?
  • Lakurawa sun kashe mutane 15 a Sakkwato
  • Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta