HausaTv:
2025-12-05@23:52:01 GMT

An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya

Published: 15th, April 2025 GMT

Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.

Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai  harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.

Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.

Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.

Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna  kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa

Jirgin Fadar Shugaban Kasa da Gwamnatin Najeriya ta saka a kasuwa da nufin sayarwa ya kasa samun mai saye kusan watanni biyar bayan ɗora shi a dandalin sayar da jiragen sama na duniya.

A sakamakon haka, tuni ma kamfanin dillancin da ke kula da sayar da jirgin samfurin Boeing 737-700 Business Jet ya janye jerin sayar da shi daga shafinsa.

’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe

Jaridar Punch ta rawaito cewa jirgin da a baya aka saka a shafin kamfanin, yanzu an cire shi daga kai.

A cikin wata amsa ga sakon imel, Laurie Barringer wanda shi ne Manajan Binciken Kasuwa na JetHQ, ya tabbatar da cewa kamfanin ya cire jirgin daga jerin sayarwa, inda ya ce a nemi karin bayani daga Gwamnatin Najeriya.

“Mun gode da sakonku. Ba mu da jerin Boeing yanzu a shafinmu. Sai dai ku tuntubi Gwamnatin Najeriya don samun bayani kan abin da ya faru da jirgin. Na gode da lokacinku — Laurie Barringer, Manajan Binciken Kasuwanci, JetHQ,” in ji sakon.

Hadimin Mai Ba da Shawara kan Tsaron Ƙasa, Ismail Garba, ya yi alƙawarin bayar da amsa amma bai yi hakan ba har bayan kwanaki da dama.

Mataimakin Manajan Binciken Kasuwa na JetHQ, Marinell Nuevo, ya tabbatar da cewa jirgin “yana nan a kasuwa” amma ya tura karin tambayoyi zuwa Barringer.

Daga baya Barringer ya bayyana cewa kamfanin ba zai bayyana wasu bayanai fiye da kasancewar jirgin a kasuwa ba, yana mai cewa irin wannan bayani na sirri ne.

“Ba ma bayar da irin wadannan bayanan ga kowa sai ga mamallakin jirgin kai tsaye. Ana ɗaukar wannan bayani a matsayin sirri. Ina fatan za ku fahimta. Abin kawai da za mu iya bayarwa shi ne cewa jirgin yana nan a kasuwa,” in ji Barringer.

Kafin a cire shi daga jerin sayarwa, bayanai sun nuna cewa an yi wa jirgin gyare-gyare a watan Yuli 2024, ciki har da gyaran kujerun ajin farko, sauya kafet na cikin jirgi da sauran kananan gyare-gyare.

A cewar aircraftcostcalculator.com, jirgin Boeing 737 BBJ da aka taɓa amfani da shi darajarsa a kasuwa ta kai kusan $56m, kwatankwacin Naira sama da Naira biliyan 82.

An sayi jirgin a shekarar 2005 a kan $43m a zamanin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, kuma ya kasance wani jerin jiragen Fadar Shugaban Ƙasa.

A watan Yuli 2025, gwamnatin Tinubu ta sanar da shirin sayar da jirgin a matsayin wani ɓangare na dabarar rage kashe kuɗi da daidaita yawan jiragen, a yayin da jama’a ke ƙara sa ido kan yadda gwamnati ke kashe kuɗade.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dorinar ruwa ta kashe mutum 2, ta jikkata 6 a Gombe
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina