Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja
Published: 2nd, August 2025 GMT
Wani mutum ya rasu, yayin da wasu biyu suka jikkata sakamakon rikici da ya ɓarke tsakanin mazauna ƙauyen Kuchibiyi da jami’an ’yan sanda a Ƙaramar Hukumar Bwari da ke Babban Birnin Tarayya, Abuja.
Wani mazaunin ƙauyen, Samuel Dangana, ya shaida wa wakilinmu ta waya cewa rikicin ya samo asali ne yayin da wasu da ake zargin masu ƙwacen fili ne suka zo ƙauyen tare da ‘yan sanda daga ofishin Byazhin, suna ƙoƙarin ƙwace wani fili a ƙauyen.
Dangana, ya ce lokacin da mazauna ƙauyen suka gan su, sai suka taru suka toshe hanya don hana su zuwa wajen filin.
Ya ce mutanen ƙauyen suna riƙe sanduna da duwatsu, inda suka fuskanci jami’an tsaro.
Daga nan ’yan sandan suka fara harba barkonon tsohuwa da harsasai.
“Ɗaya daga cikinmu an harbe shi ya mutu, biyu kuma sun jikkata,” in ji Dangana.
Ya ƙara da cewa an garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa wani asibiti da ke garin Bwari domin kula da su.
Ƙwamishinan da ke wakiltar mazaɓar Byazhin/Kuchibiyi, Hon. Dogara J. Ahmed, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce an shaida masa cewa mutum ɗaya ya rasu, yayin da wasu biyu kuma sun samu rauni.
“Yanzu haka na iso ƙauyen domin samun cikakken bayani,” in ji shi.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar, SP Josephine Adeh, ta ce an kama wasu mutane kan rikicin fili a ƙauyen Kuchibiyi.
Ta ce DPO na Byazhin da na Kubwa sun garzaya wajen domin kwantar da tarzoma, kuma lamarin ya lafa.
Ta tabbatar da cewa an kama mutane kuma suna ci gaba da bincike, amma ba ta ce komai ba kan wanda aka ce ya rasu ko waɗanda suka jikkata ba.
Sai dai ta bayyana cewa Kwamishinan ’yan sandan Abuja, CP Ajao Saka Adewale, ya soki yadda matasan ƙauyen suka kai wa jami’an tsaro hari.
Ya yi gargaɗin cewa rundunar ba za ta lamunci hakan ba, kuma za ta ɗauki matakin doka kan duk wanda ya aikata hakan.
’Yan sanda sun ce za su yi ƙarin bayani a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Arangama Ƙauye
এছাড়াও পড়ুন:
Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
Adadin mutanen da suka yi shahada sakamakon kisan kiyashin da ‘yan sahayoniyya suke yi a Gaza ya doshi 65,000
Adadin mutanen da suka yi shahada sakamakon yakin da yahudawan sahayoniyya suka kakaba wa Falasdinawa a yankin Zirin Gaza ya karu zuwa shahidai 64,871 da kuma jikkatan wasu 164,610 tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekarar 2023.
Bisa kididdigar baya-bayan nan da ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta fitar a zirin Gaza a ranar Lahadin da ta gabata, mutane 12,321 ne suka yi shahada yayin da wasu 52,569 suka samu raunuka tun bayan da gwamnatin mamayar Isra’ila ta sake komawa yaki kan Falasdinawa a ranar 18 ga watan Maris.
A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, Falasdinawa 68 ne suka yi shahada tare da jikkatan wasu 68 da aka isa da su zuwa asibitocin Gaza.
Haka nan wasu Falasdinawa 10 sun yi shahada wasu 18 kuma suka jikkata da aka kai su asibitoci, lamarin da ya kawo adadin wadanda hare-haren ta’addancin ya rutsa da su a cikin bala’in neman tallafin abinci suka haura zuwa shahidai 2,494 da kuma wasu fiye da 18,135 da suka samu raunuka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci