Aminiya:
2025-08-02@19:29:58 GMT

Zulum zai mayar da ’yan gudun hijira 5,000 Bama

Published: 2nd, August 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce gwamnatinsa na shirin mayar da mutum 5,000 gida daga sansanin ‘yan gudun hijira kafin wucewar damina domin su samu damar yin noma.

Mutanen za su fito ne daga garuruwan Goniri, Bula Kuriye, Mayanti, Abbaram, da Darajamal.

Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja

Gwamnan, ya bayyana hakan ne lokacin da ya kai wa Mai Martaba Shehun Bama, Dakta Umar ibn Kyari Umar El-Kanemi, ziyara a fadarsa da ke Bama.

Ya ce an riga an kammala gina matsuguni 1,000 a Darajamal, sannan kuma aikin gina wasu a sauran garuruwan hudu.

“Mun ƙudiri aniyar dawo da ‘yan gudun hijira gida. A Mayanti, Goniri, Bula Kuriye da Abbaram muna gina gidaje, na Darajamal kuma an riga an gama,” in ji Gwamnan.

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta kewaye yankunan da rami domin inganta tsaro.

Zulum, ya jaddada muhimmancin noma a rayuwar al’umma.

“Muna so mutanen da za a dawo da su gida su samu damar yin noma, saboda noma shi ne abin dogaron rayuwa a Borno,” in ji shi.

Ya ce zai gana da shugabannin JTF da Civilian JTF domin tsara yadda za a kare lafiyar manoma da gonaki.

Haka kuma, Zulum ya shaida wa Shehun Bama cewa gwamnatinsa ta ƙara tsaurara tsaro a garin Nguro Soye, domin samun damar yin noma.

“Daga dawowa daga Gwoza, na tsaya a sansanin sojoji da ke kusa da Banki, inda muka tattauna yadda za a tsaurara tsaro a Nguro Soye. Na bai wa sojoji da Civilian JTF kayan aiki kuma na yi alƙawarin biyan ‘yan sa-kai da ke sintiri alawus ɗin watanni shida da suka wuce,” in ji Gwamnan.

A nasa ɓangaren, Mai Martaba Shehun Bama ya yaba wa Zulum bisa ƙoƙarinsa na kyautata tsaro da jin daɗin jama’a.

“Ina yi wa gwamna godiya saboda dawo da mutanen Darajamal gida. Muna fatan sauran mutane ma za su dawo gida cikin kwanciyar hankali,” in ji Shehun.

Shehun, ya kuma roƙi gwamnatin da ta ƙara tallafa wa Civilian JTF domin kare manoma da gonaki a lokacin damina.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan gudun hijira

এছাড়াও পড়ুন:

Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta

Limamin da ya jagoranci sallar Juma’ar birnin Tehran ya bayyana cewa: Iran za ta  mayar da birnin Tel Aviv kufai idan ta maimaita wautar ta

Limamin da ya jagoranci sallar Juma’a a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran, Ayatullah Ahmad Khatami, ya gargadi shugabannin yahudawan sahayoniyya kan illar duk wani keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma, yana mai jaddada cewa: Idan aka sake yin wani wauta, to Iran za ta kaddamar da wani mummunan martani da zai mayar da Tel Aviv garin fatalwa.”

A hudubar sallarsa ta Juma’a a a yau, Ayatullah Khatami ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ita ce ta yi nasara a yakin wuce gona da iri da aka shafe kwanaki 12 ana yi, yayin da yahudawan sahayoniyya suka kasance mafiya hasara.

Limamin ya yaba da irin jarumtar da al’ummar Iran suka nuna a yakin da aka yi a baya-bayan nan, inda ya tunatar da shahadar manyan kwamandojin soji da masana kimiyyar nukiliya. Ya mai nanata cewa: Iran ba zata rushe ba, kuma ba za a taba yin nasara kanta ba, da yardan Allah, amma za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka da alfahari duk da irin makircin da ake kullawa kanta.

Ayatullah Khatami ya kara da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta tabbatar da karfinta a lokacin da ta kai hari kan sansanonin Amurka irin su Ain al-Assad da Udeid da makamai masu linzami, inda ta kasance kasa daya tilo tun bayan yakin duniya na biyu da ta kai wa Amurka hari sau biyu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Slovenia Da Haramta Tura Makamai Zuwa Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 1, 2025 Kasar Spain Ta Bayyana Abin Da Ke Faruwa A Gaza A Matsayin Abin Kunya Ga Bil’Adama August 1, 2025 Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu August 1, 2025 Mali da Rasha sun tattauna kan hadin gwiwar makamashi August 1, 2025 Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka August 1, 2025 Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli August 1, 2025 Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata August 1, 2025 Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan August 1, 2025 Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar August 1, 2025 Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
  • ‘Yan Sudan dama na komawa gida bayan gudun hijira na tsawon shekaru a Masar
  • Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana
  • Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta
  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga