Zulum zai mayar da ’yan gudun hijira 5,000 Bama
Published: 2nd, August 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce gwamnatinsa na shirin mayar da mutum 5,000 gida daga sansanin ‘yan gudun hijira kafin wucewar damina domin su samu damar yin noma.
Mutanen za su fito ne daga garuruwan Goniri, Bula Kuriye, Mayanti, Abbaram, da Darajamal.
Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a NejaGwamnan, ya bayyana hakan ne lokacin da ya kai wa Mai Martaba Shehun Bama, Dakta Umar ibn Kyari Umar El-Kanemi, ziyara a fadarsa da ke Bama.
Ya ce an riga an kammala gina matsuguni 1,000 a Darajamal, sannan kuma aikin gina wasu a sauran garuruwan hudu.
“Mun ƙudiri aniyar dawo da ‘yan gudun hijira gida. A Mayanti, Goniri, Bula Kuriye da Abbaram muna gina gidaje, na Darajamal kuma an riga an gama,” in ji Gwamnan.
Ya ƙara da cewa gwamnati za ta kewaye yankunan da rami domin inganta tsaro.
Zulum, ya jaddada muhimmancin noma a rayuwar al’umma.
“Muna so mutanen da za a dawo da su gida su samu damar yin noma, saboda noma shi ne abin dogaron rayuwa a Borno,” in ji shi.
Ya ce zai gana da shugabannin JTF da Civilian JTF domin tsara yadda za a kare lafiyar manoma da gonaki.
Haka kuma, Zulum ya shaida wa Shehun Bama cewa gwamnatinsa ta ƙara tsaurara tsaro a garin Nguro Soye, domin samun damar yin noma.
“Daga dawowa daga Gwoza, na tsaya a sansanin sojoji da ke kusa da Banki, inda muka tattauna yadda za a tsaurara tsaro a Nguro Soye. Na bai wa sojoji da Civilian JTF kayan aiki kuma na yi alƙawarin biyan ‘yan sa-kai da ke sintiri alawus ɗin watanni shida da suka wuce,” in ji Gwamnan.
A nasa ɓangaren, Mai Martaba Shehun Bama ya yaba wa Zulum bisa ƙoƙarinsa na kyautata tsaro da jin daɗin jama’a.
“Ina yi wa gwamna godiya saboda dawo da mutanen Darajamal gida. Muna fatan sauran mutane ma za su dawo gida cikin kwanciyar hankali,” in ji Shehun.
Shehun, ya kuma roƙi gwamnatin da ta ƙara tallafa wa Civilian JTF domin kare manoma da gonaki a lokacin damina.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan gudun hijira
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya
Fadar Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa nan da wasu kwanaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gana da takwaransa na Amurka, Donald Trump, domin tattaunawa kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya.
Mai ba wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, ne ya tabbatar da hakan a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.
Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin SudanA cewar Daniel Bwala, shugabannin biyu — Tinubu da Trump — sun yi tarayya da juna kan fahimta ta haɗin kai wajen yaƙi da ta’addanci da duk wata barazana ga bil’adama.
“A bayan nan Shugaba Trump ya taimaka wajen ba da izinin sayar wa Nijeriya makamai, kuma Shugaba Tinubu ya yi amfani da damar yadda ya kamata wajen yaƙi da ta’addanci, kuma muna da sakamakon da za mu iya nunawa,” in ji Bwala.
Ya ƙara da cewa duk wani saɓanin fahimta kan ko ‘yan ta’adda a Nijeriya na kai hari ne ga Kiristoci kaɗai ko kuma mabiyan addinai daban-daban, “za a tattauna kuma a warware su” a yayin ganawar shugabannin biyu, wadda za ta gudana “ko dai a Fadar Shugaban Kasa ta Abuja, ko a Fadar White House da ke Washington.”
Sanarwar ta zo ne bayan barazanar Shugaba Trump ta kai farmaki a Nijeriya, inda ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta fara tsara yadda za a kai hari kan ƙasar, saboda abin da ya kira “kisan gillar da ake yi wa Kiristoci” a Nijeriya.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, Trump ya ce Amurka “a shirye take ta turo sojojinta da manyan makamai zuwa Nijeriya don kare Kiristoci,” yana mai cewa idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma “mai yiwuwa ta shiga ƙasar don kawar da ‘yan ta’adda masu zafin kishin Musulunci.”
Barazanar Trump ta jawo cece-kuce bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya, ba tare da ya bayyana takamaiman inda ya samo waɗannan alƙaluman ba.
Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Tinubu ya jaddada cewa Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai kiyaye dimokuraɗiyya, wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.