HausaTv:
2025-08-07@06:43:54 GMT

 Yemen Ta Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami  Na  “Falasdinu 2”

Published: 3rd, May 2025 GMT

Sojojin kasar ta Yemen sun sanar da kai wa yankin  Yafa hari da makami mai linzami da ya fi sauti sauri mai suna ” Falasdinu 2″, tare da tabbatar da cewa, ya fada inda aka harba shi.

A yau Asabar ne dai sojojin na Yemen su ka kai wa HKI harin da makami mai linzami mai tsananin sauri bisa abinda su ka kira da cewa; Mayar da martani ne akan ci gaba da yakin da yakin da ‘yan sahayoniya suke ci gaba da kai wa Gaza, da kuma jefa yankin cikin yunwa.

Kakakin sojan kasar Yemen, janar Yahya Sari, ya bayyana cewa; Makami mai linzamin da aka yi amfani da shi sunashi; “Falasdinu 2” kuma ya isa inda aka harba shi.

Janar Yahya Sari ya kuma ce: Dukkanin al’ummar musulmi ne suke da alhakin yin shiru akan abinda yake faruwa a Gaza, da kuma kin taimaka musu, sannan kuma ya ce: Ko ba dade-ko bajima, samamakon  yin shiru akan wuce gona da irin ‘yan sahayoniya zai isa cikin sauran kasashe.”

Janar Sari ya kuma ce; Gaza, tana kare dukkanin al’umma ne a wannan lokacin, domin taimaka mata shi ne ya fi dacewa da a tsumayi lokacin da sharri zai isa gidan kowa.”

Da safiyar yau Asabar ne dai  jiniyar gargadi ta kada a yankuna da yawa na HKI da su ka hada yankin Kudus, Tel Aviv da kuma ” “Dead Sea” bayan da aka harbo makami mai linzami daga kasar ta Yemen.

Makamin na dazu dai ne karo na uku da sojojin Yemen su ka harba a cikin sa’o’i 24.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar sojin kasar Sin (PLA) ta yi sintiri a yankin tekun kudancin Sin daga ranar 3 zuwa 4 ga wata.

Kakakin rundunar PLA ta kudancin kasar Tian Junli ya bayyana a yau Litinin cewa, kasar Sin ta dauki matakin ne biyo bayan matakan Philippines na sanya kasashen dake wajen yankin cikin abun da ta kira da sintirin hadin gwiwa, wanda ke neman lalata zaman lafiya da kwanciyar hankalin yankin.

A cewarsa, dakarun rundunar ta kudancin kasar za su ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana da kare ikon kasar kan yankunanta da muradunta na teku ba tare da yin kasa a gwiwa ba, yana mai cewa za a dakile duk wani matakin soja dake nemen tada hankali da rikici a yankin. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • “Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa
  • Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
  • Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus
  • Kotun Ta Umurci Gwamnatin Neja Ta Janye Hukuncin Da Ta Dauka Akan Gidan Rediyon Badeggi
  • Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Yankin Jaffa Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI Bayan Da Yemen Ta Cilla Sabbin Makamai
  • Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
  • Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa