Yemen Ta Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami Na “Falasdinu 2”
Published: 3rd, May 2025 GMT
Sojojin kasar ta Yemen sun sanar da kai wa yankin Yafa hari da makami mai linzami da ya fi sauti sauri mai suna ” Falasdinu 2″, tare da tabbatar da cewa, ya fada inda aka harba shi.
A yau Asabar ne dai sojojin na Yemen su ka kai wa HKI harin da makami mai linzami mai tsananin sauri bisa abinda su ka kira da cewa; Mayar da martani ne akan ci gaba da yakin da yakin da ‘yan sahayoniya suke ci gaba da kai wa Gaza, da kuma jefa yankin cikin yunwa.
Kakakin sojan kasar Yemen, janar Yahya Sari, ya bayyana cewa; Makami mai linzamin da aka yi amfani da shi sunashi; “Falasdinu 2” kuma ya isa inda aka harba shi.
Janar Yahya Sari ya kuma ce: Dukkanin al’ummar musulmi ne suke da alhakin yin shiru akan abinda yake faruwa a Gaza, da kuma kin taimaka musu, sannan kuma ya ce: Ko ba dade-ko bajima, samamakon yin shiru akan wuce gona da irin ‘yan sahayoniya zai isa cikin sauran kasashe.”
Janar Sari ya kuma ce; Gaza, tana kare dukkanin al’umma ne a wannan lokacin, domin taimaka mata shi ne ya fi dacewa da a tsumayi lokacin da sharri zai isa gidan kowa.”
Da safiyar yau Asabar ne dai jiniyar gargadi ta kada a yankuna da yawa na HKI da su ka hada yankin Kudus, Tel Aviv da kuma ” “Dead Sea” bayan da aka harbo makami mai linzami daga kasar ta Yemen.
Makamin na dazu dai ne karo na uku da sojojin Yemen su ka harba a cikin sa’o’i 24.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun IRGC Na JMI Sun Kaddamar Da Sabon Kwale-Kwale Mai Cilla Makamai Masu Linzami
Rear Admiral Alireza Tangsiri babban kwamandan sojojin ruwa na dakarun IRGC ya bayyana haka ne a jiya a bikin ranar “Tekun farisa’ ta kasa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kwale-kwalen mai sauran kilomita Knots 116 na ruwa wanda yayi dai-dai da kilomita 215 / a ko wace sa’a yana da kayan aikin cilla makamai masu linzami.
Kwamandan ya kara da cewa, wannan yana daga cikin shirin JMI na karfafa tsoron kasar, kuma sako ne ga makiya su san da haka, sannan sakon zaman lafiya ga makobta da abokai.
An sanya ranar da turawan Portigal suka fice daga tekun farisa da mashigar ruwa ta Hurmus shekaru 1622 da suka gabata, a matsayin ranar tekunfarisa ta kasa.
A lokacinda yake karin bayani kan wannan kwale-kwalen Tangsiri ya cewa sun gina wannan karamin jirgin mai cilla makamai masu linzami, a lokacinda yake gudun saurin kilimita 215 ne don kyautata tsaron taken farisa, da kuma nuna karfin JMI na tabbatar da zaman lafiya a dukkan yanken tekun na farisa.
Yace Iran bata son samuwar sojojin kasashen waje, musamman Amurka dawasu kasashne turai a yankin, don ba abinda samuwarsu suke haddasawa a yankin sai rashin tsaro da zaman lafiya a cikinsu.