Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
Published: 12th, April 2025 GMT
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi watsi da damuwar da ake nunawa kan ziyarar da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya kai wa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, inda ya ce APC ba ta girgiza ba, kuma ta mayar da hankali ne kan karfafa madafunta.
A cikin wani bidiyo, a lokacin da yake yi wa manema labarai jawabi jim kadan bayan ya jagoranci masu ruwa da tsaki na APC zuwa ganawa da Buhari a gidansa, Ganduje ya ce sun ziyarci Buhari ne don sanar da shi irin nasarorin ci da jam’iyyar ta samu tun bayan barinsa mulki da kuma tabbatar da kudirinsu na tabbatar da ci-gaban ayyukansa.
“Ba mu ba damu ko kadan. Mun zo ne don girmama tsohon shugaban kasa kuma mu sanar da shi nasarorin da babbar jam’iyyarmu ta samu tun bayan saukarsa daga mulki. Mun tabbatar masa da cewa za mu ci gaba da sanar da shi ina aka kwana akai-akai game da halin da ake ciki,” in ji Ganduje.
Game da ziyarar Atiku ga Buhari, wadda ake gani a matsayin yiwuwar haɗewarsu a siyasa, Ganduje ya yi watsi da ita a matsayin mara muhimmanci.
“Wannan ziyarar ba ta dame mu ba. Ƙoƙari ne maimaita tarihi amma abin da suke nema ba zai yiwu ba. Abin da suke kokarin ginawa ba shi da tushe. Wasu ɓangarorin ba za su taɓa iya haɗuwa ba,” in ji shi.
Ko da yake ya ki yin ƙarin bayani, Amma ya yi nuni da cewa a shirye APC take don dakile duk wani yunkurin ’yan adawa, ko da yake bai yi ƙarin bayani ba.
Ganduje ya ce, “Ba za mu bayyana shirinmu ba, amma mun riga mun shirya musu. Nasarorin da Shugaba Tinubu ya samu yana ƙara karfafa jam’iyyar,” in ji shi.
Ganduje ya kuma jaddada burin APC na karɓe fiye da jihohi 21 da take mulki a halin yanzu, yana mai bayyana ƙwarin gwiwa cewa jam’iyyar za ta samu karin jihohi ta hanyar sauya sheka ko zaɓe mai zuwa.
“Wasu gwamnoni za su iya dawowa cikinmu, ko kuma mu kayar da su a zaɓe. Ko ma mene ne dai, muna faɗaɗa mulkinmu. Muna gamsu da inda muke, amma ba za mu tsaya a iya nan ba.”
Da yake tsokaci kan sauya shekar da wasu kusoshin APC suka yi a kwanan nan da kuma rikicin cikin gida na jam’iyyar, Ganduje ya tabbatar da cewa tafiyarsu ba ta da wani tasiri mai yawa.
“Manyan mutane daga wasu jam’iyyu suna dawowa APC. ’Yan ƙalilan da suka tafi kuma babu wata illa ta a-zo-a-gani da za sai yi,” in ji shi.
Dangane da sukar da ake yi kan zargin gwmanatin Tinubu da nuna bangaranci a rabon muƙamai, Ganduje ya dage cewa ana raba mukamai daidai kuma jam’iyyar na tattara bayanai don tabbatar da adalci.
Ya ce, “Muna tara alƙaluman nadin mukamai don nuna cewa babu nuna bambanci a nadin mukaman shugaban kasa,” in ji shi.
Kalaman Ganduje na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da cukumurdar siyasa gabanin babban zaben 2027, inda jam’iyyun masu mulki da na adawa ke neman karfafa kawance da kuma sake dabaru.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: adawa Buhari tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
KissoshinRayuwa : Sirar Imam Al-Hassan(a) 156
156-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littana wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Murtadha Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawa, na maulana jalaluddeen Rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.
////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Hassan Al-Mujtaba(a) dan Fatimah diyar manzon All..(s) da muke kawo muku. Mun yi maganar yadda, yadda Mu’awiya dan abusufyan ya kidemi bayan bayan ya sami labarin cewa an yiwa Imam Hassan bai’a a matsayin Khalifan musulmi a kufa, sannan ya kira taron mashawartansa suka zauna suka kuma fidda wassu al-amura guda biyu don fuskantar Imam Al-Hassan(a). Kuma sune, aika jasusu mai aiko masu labarai sirri daga kasar Iraki, musamman a biranen Kufa da Basra wadanda suka kasance manya-manyan garuruwan a lokacin a kasar Iraki.
Sannan na biyu kuma suna son sayan wasu manya-manyan shugabannin Iraki wadanda suke taimakawa Imam Alhassan (a) don su barshi shikadai, hakan zai tilasta masa ya mika kai ga mu’awiya dan Abusufyan.
Sannan ba tare da bata lokaci ba suka aika mutanen biyu zuwa kasar Iraki, daya a Basra da kuma a Kufa babban birnin daular musulunci karkashin Imam Hassan (a).
A lokacin da wadan nan ma’aikata biyu suka je inda aka turasu suka fara ayyukansu na leken asiri, sai asirinsu ya tonu, Imam Hassan (a) ya tura shurdatul Khamis suka bazu a cikin kufa har sai da suka zakulo jasusun Ma’awiya a cikin birnin suka kawoshi a gaban Imam Alhassan (a) wanda ya bada Umurni a kashe sai aka kashe shi.
Haka ya faru a Basra ma, inda Abdullahi dan Abbas ® ya sa aka nemo shi aka kuma kama shi aka kawo shi a gabansa ya bada umurni aka kasheshi.
Daga sai Imam Hasan (a) ya rubutawa Mu’awiya wasika, inda a ciki ya aibata shi da cusa dan leken asiri a cikin kufa da Basar, sannan yayi masa barazana da yaki. Sannan ya fada masa cewa ya ji labarin ya nuna jin dadi da shahadar mahaifinsa Imam Ali (a).
Mu’awiya ya tsorata ya kuma mayar masa da amsa kan cewa bai ji dadin kasan mahaifinsa ba, amma yaki ya yi magana kan dan leken asirin da ya aika. Haka ma Ibnu Abbas ya rubutawa Mu’awiya wasika yana aibata shi da cusa dan leken asiri a cikin mutanen Basra. Shi ma mu’awiya ya mayar masa da amsa inda ya bayyana masa cewa Imam Alhassan (a) ya rubuta masa wasika irin tasa, yana aibata shi. Amma bai bayyanawa Ibn Abba kan cewa Imam Al-Hassan (a) yayi masa barazana da yaki.
Bayan haka sai Ibn Abbas ya rubutawa Imam Alhassan wasika inda a cikin yake bashi shawara yake kuma kodaitar da shi kan yakar Mu’awiya da kuma wasu dabarbaru da ya bashi. Ga nassin wasikar kamar yadda take.
:Bayan haka, Lalle musulmi sun mayar maka shugabancinsu bayan Aliyu (a), to zage dantse don yaki, ka yi jihadi da makiyinka, ka kusanto da mutanenka, wadanda suke da raunin Imani ka sayi addininsu don kare kanka daga cutar da kai. Ka kuma dora mutane daga manya-manyan gidaje da daukaka don sai danginsu su bika sannan kan jama’a ta hadu, …..
Ka yi koyi da abinda abinda ya zo daga wajen shuwagabanni adilai, suna cewa karya bata halatta sai a yaki… kuma ka san cewa abinda ya sa mutane suka kauracewa mahaifinka suka koma wajen Mu’awiya shi ne shi mai son daidaita rabo a tsakanin, sai wannan yayi masu nauyi.
Kuma ka san cewa kana yakar wanda ya yaki All..da manzonsa(a) a farkonmusulunci ne, har sai da al-amarin All..ya bayyana ya kuma sami rinjaye. A lokacinda aka kadaita Allah aka shafe shirka addini ya daukaka, sai suka bayyana cewa su masu Imani ne a gaban mutane, suka karanta Alkur’ani suna masu istahza’I da ayoyinsa, suka tsaida sallah suna cikin kasala, suna aikata sauran farillu ba da sonsu ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 155 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 154 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 153 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 152 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 151 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 150 October 19, 2025 Wata Kotun A Murka Ta Haramtawa HKI Kafa Na’urorin Leken Asiri A Wayoyi Masu WattsApp October 19, 2025 Sojojin Najeriya: Rahotanni Dangane Da Juyin Mulki Wa Shugaba Tinubu Ba Gaskiya Bane October 19, 2025 Hamas Ta Gabatar Da Sunayen Kwararrun Da Zasu Gudanar Da Harkokin Gaza October 19, 2025 Doha: Pakistan da Afghanistan sun amince da tsagaita bude wuta a tsakaninsu October 19, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci