An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
Published: 2nd, August 2025 GMT
“Saurayin nata ne ya kashe marigayiyar a ranar Talata kuma ya kulle ta a cikin dakinsa, maƙwabta ne suka ja hankalin daliban a lokacin da suka fahimci wani wari daga dakin.
“Har yanzu ba mu san dalilin da ya sa saurayin ya kashe ta ba, dalibar tana sana’ar POS a yankin, amma tun ranar Talata, ta ɓace kuma babu wanda ya san inda take sai jiya, lokacin da maƙwabta suka ji wani wari daga dakin saurayinta.
“Shi yaron, bayan sun kashe ta, ya tafi da cinikin da yi a wajen sana’ar ta ta POS.
“Lokaci ya yi da gwamnatin jihar za ta yi wani abu game da kashe-kashen da ƴan asalin garin suke yi wa dalibanmu, idan ba a yi wani abu ba, hakan na iya haifar da mummunan rikici a wannan al’umma.
“Idan za ku iya tunawa a makonnin da suka gabata, an kuma sace dalibanmu biyu tare da kashe su, don haka dole a yi wani abu.”
A halin da ake ciki, daliban, a yayin zanga-zangar, sun rera waƙoƙin haɗin kai daban-daban, dauke da kwalaye da rubuce-rubuce irin su, ‘A Akungba Akoko, ka ce kada a kashe dalibai’, ‘A daina kashe mu, daliban AAUA,’ ƴa kamata gwamnatin jihar ta sa baki wajen kashe daliban AAUA,’ da dai sauransu.
da take mayar da martani game da sabon kashe-kashen da aka yi a cikin al’ummar jami’ar, kwamitin haɗin gwiwa na ƙungiyar daliban Nijeriya ta ƙasa, ta yi Allah-wadai da wannan danyen aikin tare da yin kira ga jami’an tsaro da su gurfanar da wanda ya aikata laifin.
“ƙungiyar daliban Nijeriya ta ƙasa, Joint Campus Council, Ondo Aɗis ta yi matuƙar kaɗuwa tare da nuna alhinin ta dangane da yawaitar kashe-kashen da ake yi wa daliban Jami’ar Adekunle Ajasin, Akungba Akoko, Jihar Ondo.
Tuntubi kakakin rundunar ƴansandan jihar, Ayanlade Olayinka, ya tabbatar da kisan.
Ayanlade ya ce saurayin marigayin ya gudu daga cikin al’umma kuma nan ba da jimawa ba jami’an ƴansanda za su kamo shi.
Ya ce an kama mutane uku da ake zargin ana yi musu tambayoyi kan kisan da aka yi a jami’ar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno
Dakarun Operation Haɗin Kai da ke Arewa maso Gabas, sun ɗakile wani sabon hari da mayaƙan Boko Haram suka kai a Jihar Borno.
Sun kai harin ne yankunan Konduga, Bama da Gwoza.
Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000’Yan ta’addan sun yi yunƙurin tarwatsa gadar da ke kan hanyar Marte zuwa Dikwa ta hanyar dasa bama-bamai.
Amma sojoji sun gano abubuwan fashewa guda 17 da suka dasa a ƙarƙashin gadar kuma suka cire su.
A yayin daƙile harin, sojoji sun kashe ’yan ta’addan Boko Haram guda tara, sannan sun ƙwato bindigogi ciki har da AK-47 da bindigar PKT.
Kakakin rundunar sojin a Maiduguri, Kyaftin Reuben Kovangiya, ya ce dakarun na ci gaba da kai farmaki da sanya ido kan ayyukan ‘yan ta’addan a yankin.
Ya ce wannan nasarar na nuna cewa sojoji sun ƙudiri aniyar hana ’yan Boko Haram da ISWAP aikata ta’addanci.
Rundunar sojin ta roƙi jama’a da su ci gaba da bayar da haɗin kai ta hanyar bayar da rahoton motsin duk wani mutum da suke zargi yana da alaƙa da ’yan ta’adda ga jami’an tsaro.