Leadership News Hausa:
2025-09-17@23:21:11 GMT

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

Published: 2nd, August 2025 GMT

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

“Saurayin nata ne ya kashe marigayiyar a ranar Talata kuma ya kulle ta a cikin dakinsa, maƙwabta ne suka ja hankalin daliban a lokacin da suka fahimci wani wari daga dakin.

“Har yanzu ba mu san dalilin da ya sa saurayin ya kashe ta ba, dalibar tana sana’ar POS a yankin, amma tun ranar Talata, ta ɓace kuma babu wanda ya san inda take sai jiya, lokacin da maƙwabta suka ji wani wari daga dakin saurayinta.

“Shi yaron, bayan sun kashe ta, ya tafi da cinikin da yi a wajen sana’ar ta ta POS.

“Lokaci ya yi da gwamnatin jihar za ta yi wani abu game da kashe-kashen da ƴan asalin garin suke yi wa dalibanmu, idan ba a yi wani abu ba, hakan na iya haifar da mummunan rikici a wannan al’umma.

“Idan za ku iya tunawa a makonnin da suka gabata, an kuma sace dalibanmu biyu tare da kashe su, don haka dole a yi wani abu.”

A halin da ake ciki, daliban, a yayin zanga-zangar, sun rera waƙoƙin haɗin kai daban-daban, dauke da kwalaye da rubuce-rubuce irin su, ‘A Akungba Akoko, ka ce kada a kashe dalibai’, ‘A daina kashe mu, daliban AAUA,’ ƴa kamata gwamnatin jihar ta sa baki wajen kashe daliban AAUA,’ da dai sauransu.

da take mayar da martani game da sabon kashe-kashen da aka yi a cikin al’ummar jami’ar, kwamitin haɗin gwiwa na ƙungiyar daliban Nijeriya ta ƙasa, ta yi Allah-wadai da wannan danyen aikin tare da yin kira ga jami’an tsaro da su gurfanar da wanda ya aikata laifin.

“ƙungiyar daliban Nijeriya ta ƙasa, Joint Campus Council, Ondo Aɗis ta yi matuƙar kaɗuwa tare da nuna alhinin ta dangane da yawaitar kashe-kashen da ake yi wa daliban Jami’ar Adekunle Ajasin, Akungba Akoko, Jihar Ondo.

Tuntubi kakakin rundunar ƴansandan jihar, Ayanlade Olayinka, ya tabbatar da kisan.

Ayanlade ya ce saurayin marigayin ya gudu daga cikin al’umma kuma nan ba da jimawa ba jami’an ƴansanda za su kamo shi.

Ya ce an kama mutane uku da ake zargin ana yi musu tambayoyi kan kisan da aka yi a jami’ar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno

Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.

Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala

A cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.

“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).

“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.

Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin