Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
Published: 12th, April 2025 GMT
Sojojin kasar Yemen sun yi amfani da jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan cibiyoyin makamai na HKI wadanda suka Yaffa (tel aviv) saboda daukar fansa kan kashe-kashen da take yi a Gaza.
Tashar talabijin Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran YAF na kasar Yemen yana fadar haka a jiya Jumma’a, ya kara da cewa sojojin yahudawan sun kai hare-hare kan unguwar Shaja’iyya inda suka kashe Falasdinawa da dama.
Ya zuwa yanzu tun fara yakin tufanul Aksa, a cikin watan Octoban shekara ta 2023, falasdinawa kimani 51,000 sannan wasu 115,688 a gaza. Ta kuma rusa kimani kasha 90% na gine-ginen Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Zanga-Zangar Miliyoyi A Yemen Ta Jaddada Alkawari Ga Shahidai Da Ci Gaba Da Goyon Bayan Al’ummar Falasdinu
Zanga-zangar miliyoyin mutane a birnin Sana’a na sabunta alkawarin da aka yi wa shahidai tare da tabbatar da shirin tallafawa Falasdinu
Babban birnin kasar Yemen, Sana’a, ya halarci wani tattaki na miliyoyin mutane a yau Juma’a mai taken “Shekaru biyu na bayar da gudummawa… da aminci ga jinin shahidai”, tare da tabbatar da gwagwarmaya na goyon bayan al’ummar Falastinu tare da sabunta alkawarin bin tafarkin shahidai da azama.
Daruruwan jama’a a dandalin Al-Sabeen a lokacin tattakin bayar da amana ya kunshi zurfafa fahimtar al’amuran al’umma. Sun yi nuni da cewa al’ummar Yemen duk da killacewar wuce gona da iri, amma suna nan a fagagen alfahari da daukaka, da tsayin daka kan tafarkinsu na imani da jihadi.
Daruruwan mutane daga cikin miliyoyin ne suka daga tutocin kasar Yemen da na Falasdinu, da kuma hotunan Shahidan gwagwarmaya misalign Manjo Janar Mohammed Al-Ghamari da shugabannin shahidan da suka hau kan hanyar Qudus. Sun kuma rera taken da ke tabbatar da shirye-shiryensu na tunkarar makiya yahudawan sahayoniyya idan har suka dawo da kai farmaki kan Gaza da al’ummar Falastinu ta hanyar karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta.
Sun nuna alfahari da girmamawa ga irin gagarumin sadaukarwar da aka bayar na goyon bayan al’ummar Falastinu da ‘yan uwansu a Gaza tun bayan kaddamar da harin “Ambaliyar Al-Aqsa” da kuma girmama shahidan da suka tashi tsaye wajen kare kasarsu da martabarsu da mutuncinsu da kuma tsarkakar Musulunci.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yemen Ta Sanar Da Nadin Sabon Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Kasar October 17, 2025 Iran Tayi kira Da A Warware Rikici Tsakanin Afghnistan Da Pakistan Ta Hanyar Diplomasiya October 17, 2025 Hizbullah: Amurka ِDa Isra’ila Ba za Su Iya Yin Nasarar Akanmu ba. October 17, 2025 Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin sabon Shugaban INEC October 17, 2025 Shugaban Kasar Sudan Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar October 17, 2025 Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahada Sanadiyyar Hrin Wuce Gona Da Iri Na HKI October 17, 2025 WSJ: Amurka Tana Tara Rundunonin Yaki A Zagayen Kasar Venezuela October 17, 2025 Shugabannin Kasashen Amurka Da Rasha Za Su Hadu A Kasar Hungary October 17, 2025 Larijani ya isar da sakon Ayatullah Khamenei ga Putin a ziyarar da ya kai Rasha October 17, 2025 Madagaska : Ranar Juma’a za’a rantsar da Kanar Randrianirina October 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci