An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
Published: 12th, April 2025 GMT
Jami’an tsaro sun samu nasarar kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake kira Gwaska Ɗan Ƙarami da wasu mayaƙa 100 a Jihar Katsina.
Kwamishinan Harkokin Cikin Gida na Jihar Katsina, Dokta Nasir Mu’azu ya bayyana matakin a matsayin wata gagarumar nasara a yaƙi da ’yan bindiga ake yi a jihar.
An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba — Ganduje“Abin farin ciki ne ga jihar, domin wannan nasara ta taimaka wajen wargaza ayyukan ’yan bindigar da ke addabar garuruwa da ƙauyukan da ke ƙananan hukumomin Faskari da Kankara da Bakori da Malumfashi da kuma Kafur,” in ji Kwamishinan.
Ya bayyana cewa runduna ta 17 ta sojin Nijeriya tare da ɓangaren sojin saman ƙasar ne suka ƙaddamar da hare-haren a ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2025 a dabar ɓarayin daji a Mununu Bakai da Zango da Jeka Arera da Malali, da kuma Ruwan Godiya duka a cikin ƙananan hukumomin Kankara da Faskari.
Haɗin gwiwar jami’an tsaron ƙasar ne suka ƙaddamar da harin a ranar Juma’a wanda ya yi sanadin kisan Gwaska — wanda ya kasance mataimakin shahararren ɗan bindiga Malan, shugaban ISWAP a yankin Arewa Maso Yamma.
“Hare-haren da suka yi daidai kan ɓarayin, bisa bayanan sirrin da aka samu, sun yi silar kashe wani wanda ake nema ruwa-a-jallo da aka fi sani da Gwaska, wanda mataimaki ne ga wani shugaban ’yan bindiga mai alaƙa da ISWAP,” in ji shi.
“Bayanan sirri sun tabbatar da cewa kwanan nan ne Gwaska ya yi ƙaura daga Ƙaramar Hukumar Danmusa zuwa dajin Munumu.
Rahotonni sun ce sojojin sun lalata maɓoyar ’yan bindigar da dama a sassan jihar a lokacin harin, tare da ƙwato da kuma lalata wasu manyan bindigogi masu jigida da waɗanda aka ƙera a cikin gida.
Harin na zuwa ne bayan da a farkon mako ’yan bindigar suka yi garkuwa da mutum 43 mazauna ƙauyukan Maigora da ke yankin Ƙaramar Hukumar Dandume.
Kazalika, dakarun tsaro sun ƙaddamar da wani aiki da sanyin safiyar ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2025, a hanyar da ɓarayin daji ke bi a Dutsen Wori gefen hanyar Dandume zuwa Kandamba, da ke wajen garin Dandume a kan iyaka da ƙananan hukumomin Faskari da Sabuwa.
Aikin da aka aiwatar da misalin ƙarfe 3:45 na dare ya yi silar kashe ɓarayi shida ciki har da shugabansu, yayin da sauran ɓarayin suka tsere da raunukan bindiga.
Bayanai sun nuna cewa dakarun sun ƙwace mashina bakwai yayin da saura huɗu suka tsere cikin daji.
An bi sawun ɓarayin ne daga dabarsu da ke Maigora/Doroyi cikin Ƙaramar Hukumar Faskari.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Katsina yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
An gano gawar wani malamin makarantar Islamiyya kuma mahaifin ’ya’ya bakwai, Malam Awwal Yakubu, a cikin wani kango da ke rukunin gidaje na Talba a birnin Minna, na Jihar Neja.
Malam Awwal, yana da makarantar Islamiyya a unguwar Barikin-Saleh, an neme shi sama ko ƙasa tun ranar Alhamis ɗin da ta gabata.
’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar BeninAn gano gawarsa ne da safiyar ranar Lahadi.
Rahotanni sun nuna cewa an ƙone al’aurarsa, sannan an samu kwalin ashana a gefen gawarsa.
Shugaban al’ummar yankin, Malam Mahmud Dalhatu Iya, ya shaida wa Aminiya cewa iyalan mamacin sun riga sun gano gawar kuma an riga an binne shi.
Ya ce, “An sanar da ni cewa an ga wata gawa ta lalace a wani gini da ba a kammala ba a cikin rukunin gidajenmu.
“Mun kai wa ’yan sanda rahoto. Muna nan lokacin da wani ya zo ya ce shi abokin mamacin ne, ya kuma ya ɓace tun ranar Alhamis. An yi wa gawar sutura don yi mata jana’iza a lokacin da nake magana da ku.”
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce, “A yau, 7 ga watan Disamba 2025, da misalin ƙarfe 10 na safe, an samu rahoto cewa an ga gawa a bayan rukunin gidaje na Talba da ke kan titin Kpakungu.
“Jami’an ’yan sandan Kpakungu sun je wajen kuma sun gano gawar ta lalace cikin wani gini da ba a kammala ba.
“Daga bisani iyalansa suka tabbatar da cewa Auwal Yakubu ne, mai shekaru 45, mazaunin wannan yanki.”
Ya ƙara da cewa, “Ana zargin cewa an jefar gawar ne a wajen, domin an ruwaito ya ɓace tun a ranar 4 ga watan Disamba kafin a gano shi da safiyar yau.
“An kai gawar asibiti, kuma an fara bincike don gano musabbabin rasuwarsa.”