Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Inganta Kwazon Kananan Hukumomin Jihar
Published: 2nd, August 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta jaddada kudurin ta na bada managartan shawarwari da za su yi wa kananan hukumomin jihar jagoranci wajen gudanar da ayyukan su kamar yadda yakamata.
Shugaban Kwamatin Kananan Hukumomi na Majalisar, Alhaji Aminu Zakari, ya bada wannan tabbacin lokacin rangadin kwamatin majalisar a sakatariyar karamar hukumar Birniwa.
Alhaji Aminu Zakari Wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa, yace ziyarar Kwamatin na daga nauyin da aka dorawa bangaren majalisa wajen bibiyar yadda Gwamnati ta ke aiwatar da manufofi da shirye shirye domin tabbatar da shugabanci nagari.
Alhaji Aminu Zakari yace haka kuma Kwamatin yana la’akari da batun zamantakewar jama’ar da tattalin arziki a matsayin ma’aunin ci gaban rayuwa da koma bayana domin baiwa bangaren zartaswa shawarwari dan bullo da manufofi da shirye shiryen da za su dace da bukatun Jama’a.
Yace , ziyarar na bada damar ganawa da bangaren zartaswa da na kansiloli da ma’aikata domin tabbatar da tsarin aiki tare ta hanyar kyakkyawar fahimtar juna.
A daya bangaren kuma, kananan kwamitocin da Babban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawan ya kafa, sun sami nasarar tantance ayyukan raya kasa da karamar hukumar Birniwa ta gudanar a sassan yankin daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu.
Karamin Kwamati na daya, bisa jagorancin wakilin mazabar Alhaji Muhammad Abubakar Sa’id ya duba aikin Masallacin kamsissalawati na Kakori, da gyaran masallacin juma’a na Malandi, da sanya fitilu masu amfani da hasken rana a Taljari da shaguna da rumfuna a kasuwar Birniwa da wasu muhimman wurare da suka hada da gyaran gidajen karamar hukumar da gyaran kotun shari’a a Birniwa.
Karamin Kwamati na biyu bisa jagorancin wakilin mazabar Guri, Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari, ya duba aikin gina shago guda biyar a bakin Babban titin garin Birniwa da shaguna da rumfuna da cikon kasa a garin Kupsa da masallacin kamsissalawati a kauyen Garuba.
Kazalika, ziyarar Kwamatin ta duba batun daukar malaman duba gari 22 da Gina ajujuwa a makarantun ‘Yayan fulani.
Tunda farko, shugaban karamar hukumar Birniwa, Malam Shehu Baba Birniwa, ya bayyana aniyarsa ta aiki da shawarwarin Kwamatin domin cigaban karamar hukumar sa.
Malam Shehu Baba ya ce tun daga kama mulkinsa ya bar kofar sa a bude da nufin cusa dabi’ar aiki tare da masu ruwa da tsaki a matsayin turba mai sauki wajen gudanar da mulkin karamar hukumar.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Birniwa Jigawa karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye dokar ta-baci a Jihar Rivers daga ƙarfe 12 na daren 17 ga watan Satumban 2025.
Shugaban Ƙasar, a wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce dokar ta-bacin da ta dakatar da Gwamna, Mataimakiyarsa, da ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida ta cimma manufarta na dawo da zaman lafiya a jihar.
Tinubu ya bayyana cewa ya yi amfani da Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 ne a watan Maris na 2025 sakamakon durƙushewar mulki a Jihar Rivers.
A cewarsa, rashin jituwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Majalisar Dokokin Jihar, da kuma lalata muhimman kadarorin gwamnati sun jefa jihar cikin rikici.
“Lamarin ya kai ga Babbar Kotun Ƙoli ta bayyana a ɗaya daga cikin hukuncinta cewa babu gwamnati a Jihar Rivers.” In ji Shugaban Ƙasa.
Ya gode wa Majalisar Ƙasa bisa amincewa da wannan sanarwa, tare da yabawa Sarakuna da jama’ar jihar bisa haɗin kan da suka bayar.
Tinubu ya kuma yaba wa masu adawa da suka kalubalanci wannan mataki a kotu, yana cewa wannan shi ma wani ɓangare ne na dimokuraɗiyya.
Da yake magana kan sabuwar fahimta tsakanin manyan ‘yan siyasa a jihar, Shugaban Ƙasa ya ce babu dalilin ƙara tsawaita dokar ta-bacin.
Ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara, da Mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, da Shugaban Majalisar Dokoki Martins Amaewhule da dukkan mambobin majalisar jihar za su koma bakin aiki daga 18 ga Satumban 2025.
Tinubu ya yi kira ga shugabannin siyasa a faɗin Najeriya da su ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai domin isar da fa’idodin dimokuraɗiyya ga al’umma.
Daga Bello Wakili