Aminiya:
2025-09-18@00:43:38 GMT

Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai 

Published: 3rd, August 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ce idan Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC suka sake lashe zaɓe a 2027, hakan zai lalata makomar ’yan Najeriya.

El-Rufai, ya faɗi haka ne a Jihar Sakkwato yayin wani gangamin wayar da kan jama’a da jam’iyyar adawa ta ADC, ta shirya.

Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba

Ya ce yana goyon bayan wannan haɗaka, kuma zai taimaka wajen ganin ’yan Najeriya sun sauke APC daga kan mulki.

“Idan muka bar wannan gwamnati ta ci gaba da mulki zuwa karo na biyu, ragowar abin da ya rage na haɗin kai da amincewa tsakanin ‘yan Najeriya zai lalace.

“Ƙasar na iya fuskantar barazana,” in ji shi.

“Wannan dai ta zama gwagwarmaya don ceto rayuwarmu.”

El-Rufai, ya ce dawowarsa siyasa ba don wata riba ko matsayi ba ne, sai don yana ganin gwamnatin yanzu ta gaza.

“Ba don ƙashin kaina nake wannan ba. Na dawo siyasa ne domin na yi wa al’umma hidima. Idan gwamnati ba ta cika alƙawari ba, dole ne na fito na faɗi gaskiya kuma na ɗauki mataki,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa haɗakar ADC an kafa ta ne domin yaƙar manufofin APC.

Ya ce gangamin da aka yi a Sakkwato shi ne farkon matakin neman goyon bayan jama’a a faɗin ƙasar nan.

El-Rufai, wanda ya ɗaya ne daga cikin waɗanda suka kafa jam’iyyar APC, ya fice daga jam’iyyar a watan Maris, 2025.

Ya koma jam’iyyar SDP, saboda rashin jin daɗin yadda ake tafiyar da mulki a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan siyasa Sakkwato jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa