Aminiya:
2025-09-18@00:36:01 GMT

Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja

Published: 2nd, August 2025 GMT

Ce-ce-ku-ce ya ɓarke a Jihar Neja, bayan da Gwamna Mohammed Umaru Bago, ya bayar da umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM da ke Minna, Babban Birnin Jihar.

Ya kuma umarci ’yan sanda da Kwamishinan Tsaron Cikin Gidan jihar su rufe tashar, tare da soke lasisinta.

Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa HOTUNA: Yadda aka yi Jana’izar Sarkin Gudi na Yobe bayan rasuwarsa a Abuja

Ya kuma bayar da umarnin bincikar mai gidan rediyon, kan zarginsa da tayar da hankalin jama’a da kuma adawa da gwamnati.

“Tashar na yaɗa kalaman tunzuri,” in ji mai magana da yawun gwamnan, Bologi Ibrahim.

“Gwamna ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki a kan gidan rediyon da kuma mamallakinsa.”

Sai dai shugabannin gidan rediyon sun ƙaryata zargin.

Daraktan harkokin Badeggi FM, Abubakar Shuaib, ya ce an zalunce su ne ba tare da wata hujja ba.

“Abin da ya dace shi ne a kai wa Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talabijin ta Ƙasa (NBC) ƙorafi, tun da ita ce ke sanya idanu kan shirye-shiryenmu kullum.

“Ba za mu taɓa aikata wani abu da zai tayar da zaune tsaye a jihar ba. Aikinmu dai shi ne mu riƙa sa ido kan shugabanni, ba mu da wani buri na cin zarafin kowa,” in ji shi.

Wannan ba shi ne karon farko da ‘yan jarida ke fuskantar matsin lamba a ƙarƙashin mulkin Gwamna Bago ba.

A shekarar 2023, wani ɗan jarida daga tashar Voice of America, Mustapha Nasiru Batsari, ya ce wani Kwamishina ya zage shi tare da ƙoƙarin ƙwace masa na’urar naɗar bayanai a fadar gwamnatin jihar.

A shekarar 2025 ma, Gwamnatin Jihar ta tsare wani ɗan jarida, Yakubu Mustapha Bina, na tsawon sa’o’i, tare da ƙwace wayoyinsa saboda ya wallafa wani rahoto da ya soki gwamnati.

Umarnin da gwamnan ya bayar ya fusata jama’a da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Ƙungiyar Amnesty International ta bayyana matakin a matsayin cin zarafi da rashin bin doka.

“Zargin gidan rediyo da laifin da gwamnati ke yi shi ne ƙoƙarin kauce wa gaskiya. Gwamna ba shi da hurumin rufe tashar bisa doka. Wannan wani yunƙuri ne na murƙushe ’yancin ’yan jarida da danne muryar jama’a,” in ji Amnesty International.

Muhammad Alfa Muhammad, shugaban ƙungiyar Accountability Ambassadors da ke Minna, shi ma ya soki matakin.

“Rufe gidan rediyo ba tare da bin matakan doka ba babban hatsari ne. Idan akwai wata matsala da gidan rediyon, to ya kamata a miƙa ƙorafi ga NBC. Duk wani mataki da ya saɓa da haka zalunci ne,” in ji shi.

Mutane da dama da ƙungiyoyin fararen hula, da ma ’yan jam’iyyar APC da ke goyon bayan gwamnatun sun nuna damuwa matakin.

Wasu na ganin wannan mataki na iya hana sauran ’yan jarida yin aikinsu saboda tsoro.

Yahaya Adam Idrees, wanda aboki ne ga Gwamnan Jihar Neja, ya bayyana ra’ayinsa a shafin Facebook.

“Dokar ƙasa ta Najeriya ta bai wa kowa ’yancin faɗin albarkacin baki. Ya kamata a sake nazarin wannan doka. Hana kafafen watsa labarai aiki ba abin da ya dace ba ne,” in ji shi.

Wasu mutane sun buƙaci a buɗe gidan rediyon na Badeggi FM nan take, tare da kira ga gwamnatin da ta daina amfani da ƙarfi wajen hana kafafen watsa labarai masu zaman kansu yin aikinsu.

Sun ce aikin ’yan jarida muhimmi abun ne a kowace dimokuraɗiyya kuma dole ne a kare shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamna Umaru Bago

এছাড়াও পড়ুন:

Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Gwamnan Jihar Neja, Umar Mohammed Bago, ya janyo ce-ce-ku-ce a fadin Najeriya bayan da ya sake jaddada cewa duk wani malamin addini da ke shirin yin wa’azi dole ne ya gabatar da rubutaccen wa’azinsa domin tantancewa kafin ya gabatar da shi ga jama’a.

A cewar gwamnatin jihar, wannan mataki na da nufin daƙile kalaman ƙiyayya, tsattsauran ra’ayi da barazanar tsaro da ke tasowa daga wa’azin da ba a tantance ba.

Da yake jawabi a shirin Politics on Sunday na gidan talabijin na TVC, Gwamna Bago ya musanta zargin cewa dokar ta hana wa’azi gaba ɗaya, yana mai cewa matakin na da nufin tabbatar da zaman lafiya da hana tayar da fitina.

Gwamnan ya ce:

“Ban hana wa’azi ba. Duk wanda zai yi wa’azi a ranar Juma’a, ya kawo rubutaccen wa’azinsa domin tantancewa. Wannan ba sabon abu ba ne. A Saudiyya ma haka ake yi. Ba za a bar malami ya yi wa’azi da ke cin mutuncin jama’a ko gwamnati ba, yana mai cewa ba da damar yin wa’azi ba yana nufin a yi amfani da damar wajen tayar da hankali.”

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnati na aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro kamar DSS, ’yan Sanda, Sibil Difens da sojoji domin sa ido kan wa’azin da ka iya tayar da hankali.

Matakin ya fara jawo ce-ce-ku-ce ne bayan da Darakta Janar na Hukumar Kula da Harkokin Addini ta Jihar Neja, Umar Farooq, ya sanar da cewa duk wani malami dole ne ya nemi lasisin wa’azi cikin watanni biyu ko ya fuskanci hukunci.

“Abin da ake bukata shi ne su zo ofishinmu, su cike fom, sannan su fuskanci kwamitin tantancewa kafin su fara wa’azi,” in ji Farooq.

Wannan sanarwa ta haifar da martani iri-iri daga shugabannin addini da ƙungiyoyin fararen hula, inda da dama ke nuna fargabar cewa dokar za ta iya zama hanyar danne ’yancin faɗin albarkacin baki.

Babban Limamin Jami’ar Fasaha ta Minna, Sheikh Bashir Yankuzo, ya bayyana ra’ayi mai sassauci, yana mai cewa duk da cewa gwamnati na da haƙƙin daƙile kalaman ƙiyayya, ba za ta hana wa’azi na gaskiya ba.

Sheikh Yankuzo ya ce:

“Wa’azi umarni ne daga Allah, kuma gwamnati ba ta biya kowa albashi don yin wa’azi. Amma idan akwai masu tayar da hankali ko amfani da kalaman batanci, to gwamnati na da ikon dakile hakan don tabbatar da zaman lafiya.”

Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Jihar Neja ta bakin Sakataren ta, Raphael Opawoye, ta ce ba a sanar da su hukuncin ba.

“CAN ba ta da masaniya kan dokar. Za mu fitar da sanarwa idan an sanar da mu a hukumance,” in ji Opawoye.

Sai dai wani malamin addinin Musulunci, Ustaz Uthman Siraja, ya soki dokar kwata-kwata, yana mai cewa ta take ‘yancin addini da ibada.

Ya bayyana cewa:

“Hana wa’azi cin zarafin ’yancin addini ne. Mafi alheri shi ne gwamnati ta gayyato malamin da ya tayar da hankali ta hukunta shi, ba wai a tantance wa’azi gaba ɗaya ba.”

Gwamna Bago ya kare dokar da cewa matakin tsaro ne na rigakafi, musamman ganin tarihin jihar na fuskantar hare-haren ’yan bindiga, rikicin addini da tsattsauran ra’ayi.

Yayin da wa’adin cike fom da samun lasisi ke ƙara matsowa, idanu sun karkata zuwa Jihar Neja don ganin ko dokar za ta kawo zaman lafiya ko kuma ta ƙara dagula al’amura tsakanin gwamnati da al’ummar addini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja