Aminiya:
2025-08-02@16:26:35 GMT

Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja

Published: 2nd, August 2025 GMT

Ce-ce-ku-ce ya ɓarke a Jihar Neja, bayan da Gwamna Mohammed Umaru Bago, ya bayar da umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM da ke Minna, Babban Birnin Jihar.

Ya kuma umarci ’yan sanda da Kwamishinan Tsaron Cikin Gidan jihar su rufe tashar, tare da soke lasisinta.

Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa HOTUNA: Yadda aka yi Jana’izar Sarkin Gudi na Yobe bayan rasuwarsa a Abuja

Ya kuma bayar da umarnin bincikar mai gidan rediyon, kan zarginsa da tayar da hankalin jama’a da kuma adawa da gwamnati.

“Tashar na yaɗa kalaman tunzuri,” in ji mai magana da yawun gwamnan, Bologi Ibrahim.

“Gwamna ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki a kan gidan rediyon da kuma mamallakinsa.”

Sai dai shugabannin gidan rediyon sun ƙaryata zargin.

Daraktan harkokin Badeggi FM, Abubakar Shuaib, ya ce an zalunce su ne ba tare da wata hujja ba.

“Abin da ya dace shi ne a kai wa Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talabijin ta Ƙasa (NBC) ƙorafi, tun da ita ce ke sanya idanu kan shirye-shiryenmu kullum.

“Ba za mu taɓa aikata wani abu da zai tayar da zaune tsaye a jihar ba. Aikinmu dai shi ne mu riƙa sa ido kan shugabanni, ba mu da wani buri na cin zarafin kowa,” in ji shi.

Wannan ba shi ne karon farko da ‘yan jarida ke fuskantar matsin lamba a ƙarƙashin mulkin Gwamna Bago ba.

A shekarar 2023, wani ɗan jarida daga tashar Voice of America, Mustapha Nasiru Batsari, ya ce wani Kwamishina ya zage shi tare da ƙoƙarin ƙwace masa na’urar naɗar bayanai a fadar gwamnatin jihar.

A shekarar 2025 ma, Gwamnatin Jihar ta tsare wani ɗan jarida, Yakubu Mustapha Bina, na tsawon sa’o’i, tare da ƙwace wayoyinsa saboda ya wallafa wani rahoto da ya soki gwamnati.

Umarnin da gwamnan ya bayar ya fusata jama’a da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Ƙungiyar Amnesty International ta bayyana matakin a matsayin cin zarafi da rashin bin doka.

“Zargin gidan rediyo da laifin da gwamnati ke yi shi ne ƙoƙarin kauce wa gaskiya. Gwamna ba shi da hurumin rufe tashar bisa doka. Wannan wani yunƙuri ne na murƙushe ’yancin ’yan jarida da danne muryar jama’a,” in ji Amnesty International.

Muhammad Alfa Muhammad, shugaban ƙungiyar Accountability Ambassadors da ke Minna, shi ma ya soki matakin.

“Rufe gidan rediyo ba tare da bin matakan doka ba babban hatsari ne. Idan akwai wata matsala da gidan rediyon, to ya kamata a miƙa ƙorafi ga NBC. Duk wani mataki da ya saɓa da haka zalunci ne,” in ji shi.

Mutane da dama da ƙungiyoyin fararen hula, da ma ’yan jam’iyyar APC da ke goyon bayan gwamnatun sun nuna damuwa matakin.

Wasu na ganin wannan mataki na iya hana sauran ’yan jarida yin aikinsu saboda tsoro.

Yahaya Adam Idrees, wanda aboki ne ga Gwamnan Jihar Neja, ya bayyana ra’ayinsa a shafin Facebook.

“Dokar ƙasa ta Najeriya ta bai wa kowa ’yancin faɗin albarkacin baki. Ya kamata a sake nazarin wannan doka. Hana kafafen watsa labarai aiki ba abin da ya dace ba ne,” in ji shi.

Wasu mutane sun buƙaci a buɗe gidan rediyon na Badeggi FM nan take, tare da kira ga gwamnatin da ta daina amfani da ƙarfi wajen hana kafafen watsa labarai masu zaman kansu yin aikinsu.

Sun ce aikin ’yan jarida muhimmi abun ne a kowace dimokuraɗiyya kuma dole ne a kare shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamna Umaru Bago

এছাড়াও পড়ুন:

Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za ta kammala aikin shimfiɗa layin dogo wanda ya taso daga Kaduna zuwa Kano a cikin shekarar 2026 mai zuwa.

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a yau Laraba.

Kazalika, takwaransa na sufuri, Sa’idu Ahmed Alkali ya jaddada hakan ne a yayin jawabinsa a wajen wani taron tuntuɓa tsakanin ’yan ƙasa da gwamnati da ke gudana a Jihar Kaduna.

Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa

A cewar ministan, lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau mulki kashi 15 cikin 10 na aikin kawai aka kammala.

Wata sanarwa da ma’aikatar yaɗa labarai ta fitar ta ambato ministan yana cewa “amma zuwa yanzu an kammala kashi 53 cikin 100.”

A 2024 Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa ta samu rancen kuɗin da za ta kammala aikin daga wani bankin kasuwanci na ƙasar China, abin da ministan ya jaddada a yau ɗin.

Kazalika, ministan ya ce Gwamnatin Tarayyar ta samu duka kuɗin gudanar da aikin gina layin dogo daga birnin Maiduguri na Jihar Borno zuwa garin Aba na Jihar Abiya.

“Layin dogon mai tsawon kilomita 1,443 zai ratsa jihohin Borno, da Yobe, da Gombe, da Bauchi, da Filato, da Kaduna, da Nasarawa, da Binuwai,” in ji sanarwar da kakakin ministan Rabiu Ibrahim ya fitar.

Sai dai sanarwar ba ta bayyana inda gwamnatin ta samo kudin ba.

Ministan ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta gyara layin dogo na dakon kaya tsakanin Legas zuwa Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba
  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba