Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja
Published: 2nd, August 2025 GMT
Ce-ce-ku-ce ya ɓarke a Jihar Neja, bayan da Gwamna Mohammed Umaru Bago, ya bayar da umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM da ke Minna, Babban Birnin Jihar.
Ya kuma umarci ’yan sanda da Kwamishinan Tsaron Cikin Gidan jihar su rufe tashar, tare da soke lasisinta.
Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa HOTUNA: Yadda aka yi Jana’izar Sarkin Gudi na Yobe bayan rasuwarsa a AbujaYa kuma bayar da umarnin bincikar mai gidan rediyon, kan zarginsa da tayar da hankalin jama’a da kuma adawa da gwamnati.
“Tashar na yaɗa kalaman tunzuri,” in ji mai magana da yawun gwamnan, Bologi Ibrahim.
“Gwamna ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki a kan gidan rediyon da kuma mamallakinsa.”
Sai dai shugabannin gidan rediyon sun ƙaryata zargin.
Daraktan harkokin Badeggi FM, Abubakar Shuaib, ya ce an zalunce su ne ba tare da wata hujja ba.
“Abin da ya dace shi ne a kai wa Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talabijin ta Ƙasa (NBC) ƙorafi, tun da ita ce ke sanya idanu kan shirye-shiryenmu kullum.
“Ba za mu taɓa aikata wani abu da zai tayar da zaune tsaye a jihar ba. Aikinmu dai shi ne mu riƙa sa ido kan shugabanni, ba mu da wani buri na cin zarafin kowa,” in ji shi.
Wannan ba shi ne karon farko da ‘yan jarida ke fuskantar matsin lamba a ƙarƙashin mulkin Gwamna Bago ba.
A shekarar 2023, wani ɗan jarida daga tashar Voice of America, Mustapha Nasiru Batsari, ya ce wani Kwamishina ya zage shi tare da ƙoƙarin ƙwace masa na’urar naɗar bayanai a fadar gwamnatin jihar.
A shekarar 2025 ma, Gwamnatin Jihar ta tsare wani ɗan jarida, Yakubu Mustapha Bina, na tsawon sa’o’i, tare da ƙwace wayoyinsa saboda ya wallafa wani rahoto da ya soki gwamnati.
Umarnin da gwamnan ya bayar ya fusata jama’a da ƙungiyoyi masu zaman kansu.
Ƙungiyar Amnesty International ta bayyana matakin a matsayin cin zarafi da rashin bin doka.
“Zargin gidan rediyo da laifin da gwamnati ke yi shi ne ƙoƙarin kauce wa gaskiya. Gwamna ba shi da hurumin rufe tashar bisa doka. Wannan wani yunƙuri ne na murƙushe ’yancin ’yan jarida da danne muryar jama’a,” in ji Amnesty International.
Muhammad Alfa Muhammad, shugaban ƙungiyar Accountability Ambassadors da ke Minna, shi ma ya soki matakin.
“Rufe gidan rediyo ba tare da bin matakan doka ba babban hatsari ne. Idan akwai wata matsala da gidan rediyon, to ya kamata a miƙa ƙorafi ga NBC. Duk wani mataki da ya saɓa da haka zalunci ne,” in ji shi.
Mutane da dama da ƙungiyoyin fararen hula, da ma ’yan jam’iyyar APC da ke goyon bayan gwamnatun sun nuna damuwa matakin.
Wasu na ganin wannan mataki na iya hana sauran ’yan jarida yin aikinsu saboda tsoro.
Yahaya Adam Idrees, wanda aboki ne ga Gwamnan Jihar Neja, ya bayyana ra’ayinsa a shafin Facebook.
“Dokar ƙasa ta Najeriya ta bai wa kowa ’yancin faɗin albarkacin baki. Ya kamata a sake nazarin wannan doka. Hana kafafen watsa labarai aiki ba abin da ya dace ba ne,” in ji shi.
Wasu mutane sun buƙaci a buɗe gidan rediyon na Badeggi FM nan take, tare da kira ga gwamnatin da ta daina amfani da ƙarfi wajen hana kafafen watsa labarai masu zaman kansu yin aikinsu.
Sun ce aikin ’yan jarida muhimmi abun ne a kowace dimokuraɗiyya kuma dole ne a kare shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamna Umaru Bago
এছাড়াও পড়ুন:
Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
Wani gidan shan kofi a birnin Dubai ya fara sayar da kofi guda na haɗaɗɗen kofi a kan kusan Dala 1,000, wato kimanin Naira miliyan 1.5, wanda da haka ya zama mafi tsada a duniya.
Gidan shan kofin mai suna Julith Café — da ke cikin unguwar masana’antu da ya zama sabuwar cibiyar masu son kofi, shi ne ya ƙaddamar da wannan sabon nau’in abin sha mai daraja.
Ana sa ran gidan shan kofi ɗin zai fara ba da wannan abin sha ga mutane kimanin 400 kacal, ciki har da wani ɗan adadi da aka tanadar wa dangin gidan sarautar Dubai.
Wani daga cikin masu mallakar gidan, Serkan Sagsoz, ya ce sun zaɓi Dubai ne saboda “birni ne da ya dace da irin jarin da ke nuna ƙawa da kuma salo.
“Mun ga Dubai a matsayin wuri mafi dacewa don wannan kasuwanci. Wannan birni ne da ke son abubuwan da suka bambanta,” in ji Sagsoz.
’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangiKofin kofi ɗin, wanda ake sayarwa a kan Dirhami 3,600 (kimanin 980), an yi shi ne daga ’ya’yan kofi na musamman da ake kira Nido 7 Geisha ,daga ƙasar Panama — waɗanda aka saya a gasa ta duniya bayan tashin rububin mai tsanani tsakanin masu saye.
Kamfanin Julith Café ya ce ya biya kimanin Dirhami miliyan 2.2 (dala 600,000) don sayen kilo 20 na waɗannan ’ya’yan kofi, abin da ya kafa sabon tarihin farashi mafi tsada da aka taɓa sayen kofi a duniya.
Sagsoz ya bayyana cewa kofi ɗin yana da ƙamshi da ɗanɗano na musamman. “Yana da ƙamshin furanni farare irin na jasmine, ɗanɗanon lemo da bergamot, har da ɗanɗano irin na apricot da peach. Kamar zuma yake — laushi kuma mai daɗi sosai.”
A bara, wani gidan kofi mai suna Roasters ya kafa tarihin Guinness na kofin kofi mafi tsada a duniya a Dubai, inda ya sayar da shi a kan Dirhami 2,500, amma yanzu Julith Café ta karya wannan tarihin.
Wasu mazauna Dubai sun ce duk da abin mamaki ne, amma abin ba baƙo ba ne a garin da aka sani da abubuwan alfarma.
“Abin mamaki ne amma ai wannan Dubai ce,” in ji wata mazauniya mai suna Ines.
“Ai akwai masu kuɗi, wannan wani sabon abin alfahari ne kawai,” in ji wata mai suna Maeva.
Ana sa ran gidan shan kofi ɗin zai fara ba da wannan abin sha ga mutane kimanin 400 kacal, ciki har da wani ɗan adadi da aka tanadar wa dangin gidan sarautar Dubai.
Shin idan kuna da kudin za ku saya?