Manyan Ayyukan Malamin makaranta

Malaman makaranta suna da ayyuka wadanda sun fi karfin ayi su a cikin aji saboda wurin ba huruminsu ba ne,abubuwan sun hada da irin kwarewar da suke da ita,wadda za su yi amfani da ita wajen renon/ koyar da daliban da kuma yadda rayuwarsu a matsayin ‘yan makaranatrasu za ta kasance.

 

Ayyukan Malaman makaranta sun hada da:

Shirya tsarin yadda za a koyar da darussa: Shiryawa da tsara yadda za a koyar da darussa yin hakan ya kunshi ayi abu cikin tsari da lura domin tabbatar da an shirya abubuwa masu amfani wadanda zasu amfani dalibai lokacin da aka koya masu.

Matsayinka na Malamin makaranta idan kana shirin shiga aji koyarwa kamata ya yi tsarin yadda za ka koyar ya yi daidai da manhajar abubuwan da suka kamata a koya masu,ka bayyana dalilan da suka sa za ka koyar da shi darasin,wajen yin amfani da tsare- tsare da suka shafi nau’oin koyarwa daban- daban.

Shirya gabatar ko gudanar da aiki kamar yadda ya dace wata hanya ce da zata bada damar gabatar da aiki kamar yadda ya dace.Muddin dai kana da tsarin yadda za ka koyar a hannunka wanda aka tsara da kan ka hakan zai ja,hankalin wadanda zaka koya mawa su kagara ka koyar dasu,musamman ma kamar yadda ka saba tun farko kana, mai jan hankalin su daliban naka.

Karfafawa dalibai kasancewa ana yin abin tare da su:Matukar kana bukatar ka kasance wanda yake da da’awar koyarwa wadda suma dalibai su kasance ana damawa tare da su/tafiya tare da su,ta yadda su ma, za su san cewa lalle tafiyar tare dasu ake yin ta,sai ta kasance sun saki jikinsu bu wata maganar jin kunya sai su rika bada tasu gudunmawar da kuma musayar ra’ayi.

A, matsayinka na Malamin makaranta za ka iya kara wa wadanda kake lura karatunsu kana iya basu kwarin gwiwa,suma su rika bada gudunmawa inda zaka bude layi wanda zaku rika magana ta samar da fa’idoji na koyarwa,wato kamar yadda zaka raba su zuwa shiyya-shiyya inda zasu rika tattaunawa, da kuma mahawara. Idan ana samun irin hakan a aji yana kara samun sabuwa da karuwa wadda take kara sabuwa da karuwa da ilimi na kowane dalibi.bugu da kari kuma ga yadda kowane dalibi a cikin aji zai ji dadi da kuma gamsuwa a irin hanyoyin da ake amfani da su wajen koya masu,saboda kuwa yana gane abubuwan da ake koya ma sa kwarai da gaske.

Yin bincike da kuma samar da sabbin abubuwan taimakawa koyarwa:Abin so da kauna ne Malaman makaranta koda wane lokaci su zama ma su yin bincike domin su kasance,a cikin kowane hali ake cike kan abinda ya shafi lamarin koyar da ilimi a makaranta suna iya tafiyar da hakan.Matsayin ka na Malami akwai bukatar ka zama cikin yin bincike domin ka bunkasa manhajar abubuwan da za ka koyar domin kar,a same manhajar da ta rasa wasu abubuwan da suka kamata ta kunsa.

Hakanan ma ka na iya amfani da al’amuran fasaha domin ka samar da kayan da za kayi amfani dasu wajen aikin koyarwar ka,ba domin komai ba sai don ka samar da wani hali ko yanayi,hakanan ma ka na iya maida lamarin koyarwar naka abinda za’a rika gani ba sai jiba kadai,ta hanyar yin amfani da dabaru masu yawa na koyar da ‘yan makaranta,wadanda zasu iya nuna lalle gaskiya,a kowace rana ana samun ci gaba wajen amfani da dabaru daban- daban na zamani domin saukaka koyarwa yadda kowa zai iya gane ko fahimtar halin da ake ciki.

Gyara aikin da dalibai suka yi da rubuta duk makin da suka samu:Rubuta makin da dalibi ya samu yana da matukar muhimmaci musamman ma a harkar koyarwa, hakan yana taimakawa sani ko gani irin kwazon da kowane dalibi yake da shi,wannan kuma ya ta’allaka ne kan irin kwazon da ya nuna.

Muddin kana rubuta makin da kowane dalibi tya samu a jarabawar da ka yi masu ko aikin da ka basu, hakan zai baka dama ta yin amfani da hakan wajen bada labarin irin kwazon da kowa yake da shi,ko rashin kokari wanda hakan zai sa,ka san yadda za ka bullowa lamarin.

Idan kana rubuta makin da kowane dalibi ya samu yin hakan zai taimaka maka ajiye da kuma sanin dukkanin kokarin da kowane daga cikinsu ya yi, wanda ta hakan ne za aka iya turwa Iyayensu,su kasance da masaniyar halin da ‘ya’yansu suke ciki a makaranta dangane da abubuwan da ake koya masu.

Samarwa/taimakawa masu koyo da babban taimako: Malaman makaranta suna bayar da taimako wanda kuma ya bambanta domin taimakawa kowane dalibi lamarin da yake nuna cewa kowane dalibi yana da muhimmanci, inda yake da tasa bajimtar,matsalolin da yake fuskanta,da kuma irin yadda ya dace a koyar da shi. Duk idan aka ba kowa taimakon daya kamace shi wannan kuma ana yin hakan ne domin kowane dalibi ya kai irin kololuwar da zai iya kai wa daidai da bukatar sa.

Matsayin ka na Malami kana iya ganewa da kuma gane bukatar musamman ka kowane dalibi da ta shafi yadda za’a koya ma sa, da irin salo- salon da za’ayi amfani da su,kayan da za’ayi amfani da su, domin su gamsar da koyarwa ta musamman da kuma irin kokarin na daliban.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Makaranta Malaman makaranta da kowane dalibi kowane dalibi ya makaranta sun za ka koyar abubuwan da kamar yadda

এছাড়াও পড়ুন:

Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar

Majalisar Dokokin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Bashar Aliyu Gummi, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta hada kai da ayyukan tsaro a Jihar domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, kamar yadda babi na biyu na kundin tsarin mulki ya tanada.

 

A zaman taron na ranar Talata, mambobin sun yi zargin cewa, ‘yan bindiga sun mamaye al’ummomi da dama a fadin jihar Zamfara, kuma sun zargi Gwamnan da mayar da hankali kan burin siyasa da kuma zargin abokan hamayya.

 

Sun kuma yi zargin cewa, Gwamnan bai kai ziyara ko aika tallafi ga al’ummomin da hare-hare ya shafa ba, inda suka ce ziyarar da ya shirya kai wa al’ummar Banga da ke karamar hukumar Kaura Namoda ta kasance da alaka da siyasa gabanin zaben fidda gwani na majalisar dokokin jihar.

 

A nasa gudunmuwar, Bashir Abubakar Masama na Bukkuyum ta Arewa ya yabawa kokarin gwamnatin tarayya na yaki da ‘yan fashi, inda ya bayyana cewa Adapka, Zauma, Gwashi, da Mayanchi a mazabarsa sun sha fama da hare-hare akai-akai.

 

Da yake goyon bayan kudirin, Bashir Bello Sarkin Zango na Bungudu ta Yamma, ya yi zargin cewa, Gidan Bugaje, Zaman Gida, Kukan Tara, da Gidan Dan-Inna, gungun miyagu sun mayar da yankin nasu, yayin da shugaban marasa rinjaye Aliyu Ango Kagara na Talata Mafara ta Kudu ya sanya Morai, Bobbo, Makera, Jangebe, Gwaram, da Ruwan Gizo a matsayin kauyukan da lamarin ya fi shafa a mazabarsa.

 

‘Yan majalisar sun bukaci gwamnatin tarayya da ta yi watsi da gwamnatin jihar a harkokin tsaro.

 

Sun yi kira ga mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda tare da bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro.

 

A nasa bangaren, Ibrahim Tudu Tukur na Bakura ya yi zargin cewa al’ummarsa na ci gaba da zama a killace da ‘yan bindiga, inda ya bayar da misali da harin da aka kai a kwanan nan a Damri, Dakko, Sama, Sabon Garin Damri, da Sade, yayin da Faruk Musa Dosara na Maradun ya yi kira da a duba yiwuwar tsige Gwamnan bisa zarginsa da yin sakaci da aikinsa.

 

Ya kuma jaddada bukatar mazauna yankin su baiwa jami’an tsaro sahihin bayanai kan duk wani nau’in da ake zargi da aikata laifuka domin a kama su kafin su aikata wani laifi.

 

Sun kuma yi alkawarin ci gaba da yin kira da a samar da shugabanci na gari a Zamfara domin ci gaban jihar.

 

AMINU DALHATU.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli
  • Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
  • Kungiyar Ba Da Agaji Ta Sanar Da Yadda Cutar Kwalara Take Lashe Rayukan Mutane A Kasar Sudan
  • Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara
  • Iran Ta Bukaci Mayar Da Martani Kan Aniyar Isra’ila Ta Mamaye Yankunan Kasashe Domin Kafa ‘Babbar Isra’ila’
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar