Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (1)
Published: 12th, April 2025 GMT
Manyan Ayyukan Malamin makaranta
Malaman makaranta suna da ayyuka wadanda sun fi karfin ayi su a cikin aji saboda wurin ba huruminsu ba ne,abubuwan sun hada da irin kwarewar da suke da ita,wadda za su yi amfani da ita wajen renon/ koyar da daliban da kuma yadda rayuwarsu a matsayin ‘yan makaranatrasu za ta kasance.
Ayyukan Malaman makaranta sun hada da:
Shirya tsarin yadda za a koyar da darussa: Shiryawa da tsara yadda za a koyar da darussa yin hakan ya kunshi ayi abu cikin tsari da lura domin tabbatar da an shirya abubuwa masu amfani wadanda zasu amfani dalibai lokacin da aka koya masu.
Matsayinka na Malamin makaranta idan kana shirin shiga aji koyarwa kamata ya yi tsarin yadda za ka koyar ya yi daidai da manhajar abubuwan da suka kamata a koya masu,ka bayyana dalilan da suka sa za ka koyar da shi darasin,wajen yin amfani da tsare- tsare da suka shafi nau’oin koyarwa daban- daban.
Shirya gabatar ko gudanar da aiki kamar yadda ya dace wata hanya ce da zata bada damar gabatar da aiki kamar yadda ya dace.Muddin dai kana da tsarin yadda za ka koyar a hannunka wanda aka tsara da kan ka hakan zai ja,hankalin wadanda zaka koya mawa su kagara ka koyar dasu,musamman ma kamar yadda ka saba tun farko kana, mai jan hankalin su daliban naka.
Karfafawa dalibai kasancewa ana yin abin tare da su:Matukar kana bukatar ka kasance wanda yake da da’awar koyarwa wadda suma dalibai su kasance ana damawa tare da su/tafiya tare da su,ta yadda su ma, za su san cewa lalle tafiyar tare dasu ake yin ta,sai ta kasance sun saki jikinsu bu wata maganar jin kunya sai su rika bada tasu gudunmawar da kuma musayar ra’ayi.
A, matsayinka na Malamin makaranta za ka iya kara wa wadanda kake lura karatunsu kana iya basu kwarin gwiwa,suma su rika bada gudunmawa inda zaka bude layi wanda zaku rika magana ta samar da fa’idoji na koyarwa,wato kamar yadda zaka raba su zuwa shiyya-shiyya inda zasu rika tattaunawa, da kuma mahawara. Idan ana samun irin hakan a aji yana kara samun sabuwa da karuwa wadda take kara sabuwa da karuwa da ilimi na kowane dalibi.bugu da kari kuma ga yadda kowane dalibi a cikin aji zai ji dadi da kuma gamsuwa a irin hanyoyin da ake amfani da su wajen koya masu,saboda kuwa yana gane abubuwan da ake koya ma sa kwarai da gaske.
Yin bincike da kuma samar da sabbin abubuwan taimakawa koyarwa:Abin so da kauna ne Malaman makaranta koda wane lokaci su zama ma su yin bincike domin su kasance,a cikin kowane hali ake cike kan abinda ya shafi lamarin koyar da ilimi a makaranta suna iya tafiyar da hakan.Matsayin ka na Malami akwai bukatar ka zama cikin yin bincike domin ka bunkasa manhajar abubuwan da za ka koyar domin kar,a same manhajar da ta rasa wasu abubuwan da suka kamata ta kunsa.
Hakanan ma ka na iya amfani da al’amuran fasaha domin ka samar da kayan da za kayi amfani dasu wajen aikin koyarwar ka,ba domin komai ba sai don ka samar da wani hali ko yanayi,hakanan ma ka na iya maida lamarin koyarwar naka abinda za’a rika gani ba sai jiba kadai,ta hanyar yin amfani da dabaru masu yawa na koyar da ‘yan makaranta,wadanda zasu iya nuna lalle gaskiya,a kowace rana ana samun ci gaba wajen amfani da dabaru daban- daban na zamani domin saukaka koyarwa yadda kowa zai iya gane ko fahimtar halin da ake ciki.
Gyara aikin da dalibai suka yi da rubuta duk makin da suka samu:Rubuta makin da dalibi ya samu yana da matukar muhimmaci musamman ma a harkar koyarwa, hakan yana taimakawa sani ko gani irin kwazon da kowane dalibi yake da shi,wannan kuma ya ta’allaka ne kan irin kwazon da ya nuna.
Muddin kana rubuta makin da kowane dalibi tya samu a jarabawar da ka yi masu ko aikin da ka basu, hakan zai baka dama ta yin amfani da hakan wajen bada labarin irin kwazon da kowa yake da shi,ko rashin kokari wanda hakan zai sa,ka san yadda za ka bullowa lamarin.
Idan kana rubuta makin da kowane dalibi ya samu yin hakan zai taimaka maka ajiye da kuma sanin dukkanin kokarin da kowane daga cikinsu ya yi, wanda ta hakan ne za aka iya turwa Iyayensu,su kasance da masaniyar halin da ‘ya’yansu suke ciki a makaranta dangane da abubuwan da ake koya masu.
Samarwa/taimakawa masu koyo da babban taimako: Malaman makaranta suna bayar da taimako wanda kuma ya bambanta domin taimakawa kowane dalibi lamarin da yake nuna cewa kowane dalibi yana da muhimmanci, inda yake da tasa bajimtar,matsalolin da yake fuskanta,da kuma irin yadda ya dace a koyar da shi. Duk idan aka ba kowa taimakon daya kamace shi wannan kuma ana yin hakan ne domin kowane dalibi ya kai irin kololuwar da zai iya kai wa daidai da bukatar sa.
Matsayin ka na Malami kana iya ganewa da kuma gane bukatar musamman ka kowane dalibi da ta shafi yadda za’a koya ma sa, da irin salo- salon da za’ayi amfani da su,kayan da za’ayi amfani da su, domin su gamsar da koyarwa ta musamman da kuma irin kokarin na daliban.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Makaranta Malaman makaranta da kowane dalibi kowane dalibi ya makaranta sun za ka koyar abubuwan da kamar yadda
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
A wannan yanayi na matsin tattalin arziki a Nijeriya, mata na gasar neman haihuwar ’yan uku domin cin gajiyar tallafin tsabar kuɗi da abinci da tufafi da ragunan suna a Jihar Sakkwato.
Burin wadannan mata ta karu ne sakamakon yadda farin ciki nau’i uku ya lullube Malama Bela’u Sabo da iyalanta, bayan da ta haifi ’yan uku a garin Kaurar Yabo da ke Karamar Hukumar Yabo ta jihar.
Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargiA yayin da mai jego da angon karni da ’yan uwa suke tsaka da murna, wannan karuwar haihuwa ta kara jawo musu sha-tara ta arziki, inda matar gwamnan jihar, Hajiya Fatima Ahmad Aliyu, ta taso takanas zuwa kauyen ta domin yin barka.
Zuwa barkan wadannan ’yan uku ya faranta ran ba ma iyalan mai jegon ba, har ma da daukacin al’ummar garin Kaurar Yabo, domin kuwa, shi ne ziyarar farko da matar gwamnan Jihar Sakkwato ta taba kawo musu.
A yayin gaisuwar ne matar gwamnan ta gwangwaje Malama Bela’u da akwatuna uku cike da kayan fitar suna da tufafin jarirai da ragunan suna guda uku da buhuna 10 na hatsi da kuma tsabar kudi naira dubu dari biyar.
Ta kuma yi alkawarin bayar da irin wannan tallafi ga duk matar da ta da samu karuwar ’yan uku a jihar, lamarin da ya sa mata neman Allah Ya sa su a danshin wannan mai jego.
Haihuwar ’yan uku ta zo min da sauƙi — Mai jegoMalama Bela’u Sabo a tattaunawa da wakilinmu ta ce “a lokacin da na samu karuwar na yi tawakkali da Allah, kuma yaran da na samu Allah Ya yi masu albarka.”
Wakilinmu ya nemin jin yadda yanayin cikin da kuma haihuwar ’yan ukun ya kasance wa maji jegon, idan aka kwatanta da ’ya’ya takwas da ta haifa kafin su, inda ta shaida masa cewa, “akwai bambanci gaskiya don su ba su motsi, dayan ma ke dan motsi can ba a rasa ba.
“Na haife su babu wata matsala ko wahala, cikin sauki suka fito, kan haka ina fatan sake samun ’yan uku in Allah Ya ba ni don suna sanya farin ciki.
“Matar gwamna ta zo ta yi min barka, zuwan ya zo da muhimmanci, ta ba ni kudi dubu 500 da buhu 10 da akwati uku da kwalin sabulu da kwalin Klin da jirgin wanka.
“Yara ta kawo masu kala 42, ta ba ni kala 10 turame da leshi da sauran kayan shafawa, na gode Allah, Ya kuma saka da alheri,” in ji mai jego.
‘Na samu fiye da abin da na roka’Angon karni, Malam Sabo Kaurar Yabo, ya ce “A lokacin da na samu labarin na samu karuwar yaro uku a lokaci guda, sai na ji kamar an yi min kyautar Aljanna, farin ciki ya mamaye ni.
“Ina buri da rokon Allah Ya ba ni tagwaye sai na samu uku gaba daya, wannan ita ce haihuwa ta tara, yanzu ina da ’ya’ya 11 da mace guda.
“Har yanzu in zan sake samu ’yan uku zan yi maraba da su ganin yadda suke da dimbin alheri, don matar gwamna ta kawo min raguna da kimarsu ta kai naia miliyan biyu. Sun share min hawayena.
‘Zan so in sami ’yan uku’Ganin wannan irin kabakin arziki da kuma alkawarin mai tsoka da matar gwamnan ta sa wasu matan jihar kara kwadayin haihuwar ’yan uku.
Wata matar aure mai da daya da ke burin haihuwar ’yan uku, Suwaiba Sani ta shaida wa wakilimu cewa, “Abin akwai farin ciki! Matar gwamna ta kawo maka kaya don haihuwa, ka ga ’yan uku wasu mutane ne na musamman. Zan so in same su, matar gwamna ta hidimta min, na samu daukaka nima.”
A ranar Litinin da ta gabata wakilinmu ya samu labarin an sake samun karuwar ’yan uku a garin Addam da ke Karamar Hukumar Shagari.
Sai dai har zuwa kammala wanann rahoton, matar gwamna ba ta kai ga zuwa garin ba don cika alkawarin da ta dauka.
‘Kayan barka ba sa raino’Wasu matan jihar da wakilin namu ya zanta da su don jin ko za su so su haifi ’yan ukun, bayan wannan da matar gwamnan ta yi, sun nuna sabanin haka.
Maryam Ibrahim mai ’ya’ya huɗu ta ce ta sha wahalar rainoni tagwaye don haka ba ta son ’yan uku.
“Na samu ’yan biyu a haihuwa ta biyu, kula da su da wuya, ba na burin haihuwar ’yan uku gaskiya, don biyun na san yadda na sha wahalarsu, kayan barka ba su ne raino ba, ni kam hakan bai sauya ra’ayina.”
Sadiya Muhammad ta ce, “Ni ba ni da burin na haifi ’yan uku a rayuwata, amma idan Allah Ya ba ni zan yi murna, yanzu haihuwata biyu ta uku na kan hanya.”
“Alkawarin matar gwamna bai tura ni zuwa sanya raina ga abin da ban gani ba, kuma ita abin buki ne kawai za ta kawo, sauran kula da su har su girma ba ruwanta da shi fa.
“Amma da ta yi wani tsari na daukar nauyin karatun yara zuwa jami’a, da zai sa wasu kwadayin samun yaran don ganin za a rage masu wani nauyi ba harkar buki ba.”