Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
Published: 12th, April 2025 GMT
Mata a Jihar Jigawa sun yi kira da gwamnati da kungiyoyin agaji masu zaman kansu da su samar da magungunan samun tazarar haihuwa kyauta domin inganta tsarin iyali.
Matan da suka tattauna da wakilinmu a cibiyoyin kula da lafiya na Kudai da Kachi dake Dutse, a yayin bikin ranar Lafiyar Uwa ta duniya, wato “Safe Motherhood” a turance, sun bayyana damuwarsu kan rashin samuwar kayayyakin bada tazarar haihuwa.
Wata uwa mai yara uku, Malama Karimatu Sani, ta ce duk lokacin da ta je siyan maganin samar da tazarar haihuwa, ana bata wadanda lokacin aikinsu ya wuce, wanda hakan na iya haifar da illa ga lafiyar mata.
“Sau da dama sai na jira asibiti ya samu sababbin kaya, ina addu’ar kada na samu ciki kafin a kawo wadannan magunguna da ake badawa kyauta.” in ji ta.
Wata mai suna Maryam Abubakar, ta bayyana cewa tana kashe kudi masu yawa wajen zuwa asibiti don dubawa ko kayan sun samu.
Ta koka da cewa siyan kayan bada tazarar haihuwa daga shagunan magani a waje yana da tsada sosai wanda hakan yana hana mata damar siya.
A madadin mata na jihar, ta yi kira ga gwamnati da kungiyoyin agaji da su kawo musu dauki domin mutane da dama suna rungumar tsarin tsara iyali a matsayin mafita ga matsalolin da ke damun al’umma.
A gefe guda, wata ma’aikaciyar lafiya a cibiyar kula da lafiya ta Kachi, Amina Sulaiman, ta tabbatar da cewa kayayyakin samar da tazarar haihuwa sun kare a asibitin tun watanni biyu da suka wuce.
“Muna takaicin yadda mata sukan zo don yin tsarin iyali amma babu biyan bukata saboda rashin kayan aiki da magunguna”.
Hajiya Amina Sulaiman ta yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da ssusamar da kayayyakin don ragewa mata radadin rayuwa.
A bara ne gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da kwamiti mai mambobi ashirin da uku kan Lafiyar Uwa, da ke da alhakin farfado da hanyoyin kula da lafiyar uwa a jihar.
Sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim, yayin kaddamar da kwamitin a ofishinsa, ya bayyana cewa aikin kwamitin ya hada da duba yadda ake aiwatar da shirin Lafiyar Uwa da kirkirar tsarin aiwatarwa domin karfafa abinci mai gina jiki da shawarwari don samun kulawa da uwa da jarirai.
Sauran ayyukan sun hada da yin bincike kan yadda shirin ke gudana da kirkirar hanyoyi don karfafa tura mata zuwa cibiyoyin lafiya daga cikin al’umma.
Yayin kaddamar da kwamitin, Malam Bala Ibrahim ya kara da cewa an fara aiwatar da shirin ne a shekarar 2006 karkashin shirin tallafin na DFID.
Ya ce daya daga cikin muhimman sassa na shirin shi ne tsarin daukar gaggawa, inda aka samar da motoci don daukar mata masu nakuda zuwa cibiyar lafiya mafi kusa don samun ingantacciyar kulawa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, maza da mata da dama daga yankunan karkara a jihar Jigawa sun rungumi tsarin bada tazarar haihuwa da shirin Lafiyar Uwa, suna kuma cin moriyar su ta bangaren lafiya da tattalin arziki.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Tsarin Iyali da tazarar haihuwa Lafiyar Uwa
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa
A shekarar bara, ’yan kasuwa, musamman masu hadahadar kayan abinci da na amfanin gona a Nijeriya, kakarsu ta yanke saka, saboda tashin gwauron zabon da kayan a kasar.
Galibin wadannan amfanin gona na kasuwanci ana fitar da su zuwa kasashen a duniya.
Hukumar Bunkasa Fitar da Kayayyaki ta Nijeriya (NEPC) ta sanar a watan Agusta na shekarar ta 2024, cewa Najeriya ta samu gagarumin ci-gaba a fannin fitar da kayayyaki da ba na man fetur ba a watanni shidan farkon shekarar, inda ta samu kudin shiga kimanin dala biliyan 2.7.
Yawan bukatar kayan a kasuwannin duniya ya kawo hauhawar farashin kayan abinci na yau da kullum da amfanin gona na kasuwanci.
An kuma yi hasashen cewa farashin zai ci gaba da tashi a shekarar 2025.
A lokacin da farashin ke hauhawa, ’yan kasuwa da dama sun zuba jari mai yawa, musamman a harkar ridi da waken suya, da fatan samun gagarumar riba idan bukatar kayayyakin ta karu a kasuwannin duniya.
Sai dai a cikin wani yanayi mai matukar daure kai, sai ga shi farashin na ta faduwa warwas, musamman a Arewacin kasar nan.
Ma’aunin Farashin Kayayyaki (CPI) ya nuna an samu saukar farashin da kimanin kaso 25 cikin 100, daga N87 zuwa N65 a cikin watan Maris din 2025, kamar yadda kamfanin mai zaman kansa na farko a Nijeriya da aka ba lasisin hada-hadar musayar kudaden kayayyaki, AFED, ya bayyana.
Alhaji Abdullahi Usman, Shugaban Kamfanin kayayyakin abinci na Mumin Foods Ltd, wanda a cewarsa ya fi shekara 30 yana kasuwancin ridi, ya bayyana cewa faduwar farashin na da nasaba da yadda bukatar amfanin gonar da ake nomawa a Nijeriya ta ragu matuka a kasuwannin duniya.
Ya ce, sai sai abin takaici, tun bayan da bukatar kayayyakin ta karu, ’yan kasuwa da dama sun rika fito da kudade suna sayen kayan, ciki har da kayan abinci.
Dan kasuwar ya bayyana cewa saukar farashin ya kara nuna yadda kasashe suka dage wajen noma abin da za su ci, shi ya sa kasuwannin Nijeriya suka cika suka batse da kayayyaki, wanda hakan ya sa ala tilas farashinsu ya fadi.
Ya ce “Mutane sun fito da mazajen kudade wajen sayewa tare da boye kayayyakin, duk da wasu ’yan kasashen waje na hankoron sayen amfanin gonar da ake nomawa a Nijeriya musamman kasancewar sun yi amanna da cewa na asali ne ba wanda aka gurbata da sinadarai wajen noma su ba.
“Da farko dai alkaluma sun nuna komai na tafiya yadda ake bukata, sai mutane suka ci gaba da karuwa.
“Sai dai abin takaici, sai bukatar wadannan kayan daga kasashen ta ragu sosai, wanda hakan ne ya tilasta faduwar farashin kayayyakin amfanin gonar,” in ji shi.
Bayanai sun nuna cewa kilo ɗaya na ridi wanda a bara aka sayar da shi N2,300, a yanzu ana sayar da shi N1,600.
Sai kuma kilo daya na zobo wanda shi kuma a bara yake 2,300, a bana ya dawo naira1,500.
Wasu majiyoyi a harkar hada-hadar amfanin gona sun ce ana hasashen akwai yiwuwar farashin ya ci gaba da faduwa yayin da kasashen waje ke ci gaba da rage yawan bukatar kayan na Najeriya.
Haka kuma an yi amannar cewa faduwar farashin kayan abincin zai kawo sauki ga iyalan da ke rayuwar hannu-baka-hannu-kwarya na dan wani lokaci, ba lallai ta ci gaba da zama a haka ba.
Bugu da kari, mutanen da ke sayar da wadannan kayayyakin ba su cika yin asara ba kasancewar suna da inda za su ajiye su har zuwa lokacin da farashin zai musu inda suke so.
Masana tattalin arzikin amfanin gona kuma na hasashen cewa dawowar Indiya fitar da kayan da take nomawa zuwa kasashen ketare, zai sa yawan bukatar kayayyakin ta ragu a duniya, wanda hakan zai iya sawa farashin ya dada sauka, na daya daga cikin dalilan da suka jawo karyewar farashin a Najeriya a ’yan watannin nan.
Alhaji Abdullahi Usman, shugaban Mumin Food Limited, ya ce karancin masu sayan kayan masarufin Nijeriya a cinikayyar kasa da kasa na da alaka da faduwar kayan masarufi a cikin kasa Nijeriya.
Ya kara da bayanin cewa, “Abin takaici, yadda bukatun ’yan Nijeriya suke karuwa na sayen kayan masarufi, wasu daga cikin ’yan kasuwa sun saye kayan masarufin da kayan gonar, kara da cigaban da aka samu kwanan nan wanda ya ba wa ’yan kasashe dama su inganta amfanin gonarsu kuma su rage shigowa da kayan ketare, ya sa farashin wasu kayan masarufi ya sauka.
“Mutane da dama suna ajiye kayan masarufi musamman a lokacin da wasu kasashe suka nuna suna bukatar wani nau’i na kayan masarufi daga Nijeriya, saboda kayan masarufin Nijeriya ba su da sinadaran zamani.
“Amma cikin babu zato sai bukatun wadannan kasashe suka yi kasa wanda hakan ke da alaka da saukar farashin kayan masarufin.
“Bugu da kari, faduwar farashin yana kawo rangwamen wucin gadi ga masu sayen dai-dai wanda suke a gida.
“Amma masu ta’ammali da kayan masarufi abin ba ya shafar su, saboda suna da hanyar ajiye kayan har zuwa wani lokacin da ya yi musu,” kamar yadda dan kasuwan ya bayyana.
Masana noma da tattalin arziki sun tabbatar da rahoton cewa kasar Indiya ta dawo fitar da kayan masarufi zuwa kasashen ketare, a maimakon sayowa daga can, wanda hakan ke nuni da cewar za a iya samun faduwar farashinsu a ƙasashen da suke sayar wa da Indiya kaya.
Daga wani masanin tattalin arziki daga Kwalejin Ilimi na Sa’adatu Rimi da ke Kano, Mallam Hassan Ali, “Darajar naira da kuma dalar Amurka na taka rawar gani wajen saukaka wa al’amuran shigo da kaya.
“Haka kuma, Babban Bankin Kasa (CBN) ya ce hadahadar canjin naira zuwa dalar Amurka yana yawo tsakanin N1,478 d kuma N1,551 daga watan 1 na Janairu, 2025 har zuwa yanzu.”
Ya bayyana cewa, “Wannan na nuni da faduwar sama da kaso 8% daga N1,688 da yake a kididdigar wasu watanni na shekarar 2024.
Haka zalika, yanayin lokaci kusan shi ne kashin bayan hawa da faduwar farashi a kasuwar kayan masarufi, saboda lokacin shuka da girbi yana shafar yanayin hadahadar kayan abincin da kuma farashinsu.
Kusan akwai hasashen cewa makonni bayan girbe amfanin gona (lokacin kaka) farashin kayan abinci da sauran kayan gona yana faduwa kasa saboda yawan saya da kuma fitar da su da manoma ke yawan yi a wannan lokacin.”
A Jihar Kano an samu rohoton cewa ana samun sauye-sauyen tashin farashin kayayyakin masarufi da dama, musamman canjin yanayi da ake samu da kuma yadda ake samar da kayayyakin da suka shafi amfanin gonar.
Wani manomin ridi daga Jihar Jigawa, Alhaji Sagir Bello Black, ya sanar cewa a lokutan girbi farashin kayayyaki yana raguwa sakamakon yawan wadatar kayayyakin masarufi a kasuwa, sannan kuma yakan tashi a lokacin rani saboda karancin kayayyakin.
Ya kara da cewa, gazawar samar da isashen kayayyakin da ’yan kasuwa ke bukata irin na baya saboda rashin ruwan sama ko yawan ruwan sama, da tashe-tashen hankula da rashin tsaro, na haifar da hauhawar farashin kayayyakin amfanin gona.
Alhaji Aminu Gumel, wani dan kasuwar ridi wanda a cewarsa ya shafe sama da shekara 30 yana kasuwancin ridi, ya bayyana cewa ya sayi kayayyaki na miliyoyin nairori don fitarwa, amma abokan kasuwancinsa na kasashen waje ba su biya ba tukuna, sabanin yadda al’amura suka kasance a shekarun baya.
Alkasim Idris Ajingi, manomin citta, ya kara da cewa, “A shekarar 2023 Nijeriya ta fuskanci karancin noman citta sakamakon cutar kwari da ta lalata kusan kashi 70% na amfanin gona.”
Ya kara da cewa, “Wannan annoba ta kawo raguwar wadata da samuwar kayayyakin wanda ya kawo hauhawar farashin citta da ninki shida na tsawon shekaru daga N50,000 zuwa N300,000 a kowane buhu.
Ya kara da cewa, “Lokacin da manoma ke fuskantar matsalolin noma a wannan lokacin kuma kayayyaki ke raguwa shi ya sa farashin kaya dole ne ya tashi.”
Kayayyakin Nijeriya sun samu karɓuwa a duniya
Kayan masarufin Nijeriya sun samu karbuwa a kididdigar kasuwar duniya.
Misali, likafar kasuwar waken suya a kasar ta ci gaba, saboda hana shigowa da shi a 2023/2024.
Bincike ya nuna yadda matakin ya taka rawar gani wajen karuwar bukatar ’yan Nijeriya a kan waken suya.
Rahoto ya bayyana cewa waken suyar da ake fitarwa daga Nijeriya ya yi tashin gwauron zabo da sama da 1000%.
Haka ne ya sa farashin yake karuwa a cikin gida da kasuwannin kasa da kasa ya karu daga dala miliyan 10.8 a 2022, zuwa dala miliyan 201 a 2023, da farashin cikin gida wanda ya ƙaru da sama da 1 million a kowane awo.
Bugu da kari, bincike ya tabbatar da cewa kilo din waken suya an sayar da shi akan N1,300 a shekarar da ta wuce, kuma ana sayar da shi a kan N7,500 a yanzu.
Mista Chucks Idowu, wani attajiri da ke kasuwancin waken suya ma kasa da kasa, ya ce kasashen da suke bukatar waken suyar daga Nijeriya su ma suna noma tasu, shi ya sa bukatarta a kasuwar duniyar yake raguwa.
Ya kara bayyana cewa, “Karin farashin waken suyar, a shekarar da ta gabata ya sa mutane da dama suka saya suka ajiye, kuma yanzu farashin ya fadi, dole suka fito da shi don sayarwa a halin da kasuwa take a yanzu ko ba don komai ba, za su so su ci abinci.