Mata a Jihar Jigawa sun yi kira da  gwamnati da kungiyoyin agaji masu zaman kansu da su samar da magungunan samun tazarar haihuwa kyauta domin inganta tsarin iyali.

Matan da suka tattauna da wakilinmu a cibiyoyin kula da lafiya na Kudai da Kachi dake Dutse, a yayin bikin ranar Lafiyar Uwa ta duniya, wato “Safe Motherhood” a turance, sun bayyana damuwarsu kan rashin samuwar kayayyakin bada tazarar haihuwa.

Wata uwa mai yara uku, Malama Karimatu Sani, ta ce duk lokacin da ta je siyan maganin samar da tazarar haihuwa, ana bata wadanda lokacin aikinsu ya wuce, wanda hakan na iya haifar da illa ga lafiyar mata.

“Sau da dama sai na jira asibiti ya samu sababbin kaya, ina addu’ar kada na samu ciki kafin a kawo wadannan magunguna da ake badawa kyauta.” in ji ta.

Wata mai suna Maryam Abubakar, ta bayyana cewa tana kashe kudi masu yawa wajen zuwa asibiti don dubawa ko kayan sun samu.

Ta koka da cewa siyan kayan bada tazarar haihuwa daga shagunan magani a waje yana da tsada sosai wanda hakan yana hana mata damar siya.

A madadin mata na jihar, ta yi kira ga gwamnati da kungiyoyin agaji da su kawo musu dauki domin mutane da dama suna rungumar tsarin tsara iyali a matsayin mafita ga matsalolin da ke damun al’umma.

A gefe guda, wata ma’aikaciyar lafiya a cibiyar kula da lafiya ta Kachi, Amina Sulaiman, ta tabbatar da cewa kayayyakin samar da tazarar haihuwa sun kare a asibitin tun watanni biyu da suka wuce.

“Muna  takaicin yadda  mata sukan zo don yin tsarin iyali amma babu biyan bukata saboda rashin kayan aiki da magunguna”.

Hajiya Amina Sulaiman ta yi kira ga  hukumomin da abin ya shafa da ssusamar da kayayyakin don ragewa mata radadin rayuwa.

A bara ne gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da kwamiti mai mambobi ashirin da uku kan Lafiyar Uwa, da ke da alhakin farfado da hanyoyin kula da lafiyar uwa a jihar.

Sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim, yayin kaddamar da kwamitin a ofishinsa, ya bayyana cewa aikin kwamitin ya hada da duba yadda ake aiwatar da shirin Lafiyar Uwa da kirkirar tsarin aiwatarwa domin karfafa abinci mai gina jiki da shawarwari don samun kulawa da uwa da jarirai.

Sauran ayyukan sun hada da yin bincike kan yadda shirin ke gudana da kirkirar hanyoyi don karfafa tura mata zuwa cibiyoyin lafiya daga cikin al’umma.

Yayin kaddamar da kwamitin, Malam Bala Ibrahim ya kara da cewa an fara aiwatar da shirin ne a shekarar 2006 karkashin shirin tallafin  na DFID.

Ya ce daya daga cikin muhimman sassa na shirin shi ne tsarin daukar gaggawa, inda aka samar da motoci don daukar mata masu nakuda zuwa cibiyar lafiya mafi kusa don samun ingantacciyar kulawa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, maza da mata da dama daga yankunan karkara a jihar Jigawa sun rungumi tsarin bada tazarar haihuwa da shirin Lafiyar Uwa, suna kuma cin moriyar su ta bangaren lafiya da tattalin arziki.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Tsarin Iyali da tazarar haihuwa Lafiyar Uwa

এছাড়াও পড়ুন:

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

Bisa rahoton bunkasar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da nahiyar Afirka na shekarar 2025, wanda aka gabatar a jiya Juma’a 13 ga wata, an ce a halin yanzu, an samu babban sauyi a tsarin ciniki tsakanin Sin da Afirka, an kuma kyautata tsarin zuwa mai shafar fannoni da dama, mai inganci, mai kunshe da fasahohin zamani, kana a nan gaba za a samu karin damar hadin gwiwarsu a fannonin masana’antu, da aikin noma, da sadarwa, da tattalin arziki ta yanar gizo, da ayyukan more rayuwa, da makamashi mai tsafta, da hada-hadar kudi da sauransu.

A matsayin daya daga cikin manyan nasarorin da aka cimma a gun bikin baje koli na tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka karo na 4, an gabatar da rahoton ne a taron gabatar da shirye-shiryen ayyukan hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka, wanda aka gudanar a wannan rana.

Rahoton ya yi bayanin cewa, a shekarun baya-baya nan, an fadada cinikayyar Sin da Afirka, yawan kudin cinikayyar kaya tsakaninsu a shekarar 2023 ya zarce dalar Amurka biliyan 280, kuma yawan kudin cinikin hidimomi a tsakaninsu a shekarar 2021 ya kai sama da dalar Amurka biliyan 41 da miliyan 866, kana an kyautata tsarin cinikinsu.

A daya bangaren kuma, yawan jarin da Sin ta zubawa Afirka ya karu, wanda yawancinsu suka shafi sha’anin gine-gine. Haka zalika, an samu nasarori a fannin gina ayyukan more rayuwa, da gudanar da ayyuka a fannonin sufuri, da wutar lantarki, da sadarwa, da madatsun ruwa da sauransu, da kuma yin hadin gwiwarsu a fannonin ba da ilmi, da aikin noma, da kiwon lafiya, da samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba da sauransu. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu