Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC
Published: 3rd, August 2025 GMT
Ya danganta mutuwar ta ƙanana da matsakaitan sana’oi a ƙasar, kan rashin samun rancen kudaɗen da za su ci gaba da ka kasuwancin su da rashin kayan aiki, da rashin kasuwa da ba a samu sosai da kuma rashin gudanar da ingantaccen shiri, kafin su fara gudanar da kasuwancinsu.
Ya sanar da cewa, ya zama wajibi, ƴan kasuwa musamman ƙanana da matsakaitan sana’oi a su sani cewa, bab wani batun yin wani holewa, na jin daɗi
Ya bayyana cewa, sama da ƙanana da matsakaitan sana’oi 40 a ƙasar nan, burin su ba shi ne, na ƙara yawan adadin alƙaluma ba, anna burin shi ne, na ƙarfafa zurewar kasuwancinsu.
“Alƙaluma sun nuna cewa, akwai ƙanana da matsakaitan sana’oi 40 a ƙasar nan, wanda hakan ya nuna cewa, sun kai kimanin kaso 96 a cikin dari, na kasuwancin da ake yi a ƙasar, inda kuma ake da kaso 84 na masu aikin yi, musamman duba da cewa, fannin na taimaka wa, wajen samar da ayyukan yi da kuma bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin ƙasar da ya kai kimanin kaso 48, a duk shekara, ” Inji Olowo.
Ya ci gaba da cewa, wannan sabon tsarin na kasuwacin, zai taimaka wajen cimma samar da tsarin tabatar da ci gaban ƙanana da matsakaitan sana’oin hannu.
“Babu wata hanya da zamu iya cimmma burin samaun dala tiriliyan daya, ba tare da yin amfani da ɓangaren ƙanana da matsakaitan sana’oin hannu,” A cewarsa.
Shi kuwa shugaban Cibiyar ta LCCI,Gabriel Idahosa, ya bayar da tabbacin cewa, Cibiyar za ta bayar da goyo baya domin a cimma wannan tsarin, na samar da takardun shedar gudanar da kasuwancin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Sun jaddada cewa dole ne manyan kafafen sada zumunta su kare ‘yancin yin magana.
Sun kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, ‘yan jarida, da masu fafutukar kare haƙƙin bil’adama su tashi tsaye don hana abin da suka kira yunƙurin mayar da Nijeriya “mulkin kama-karya a intanet.”
Lamarin ya biyo bayan wa’adin sati guda da DSS ta bai wa Sowore da ya goge wasu wasu rubuce-rubuce game da Shugaba Bola Tinubu, wanda ya ƙi amincewa.
Hakan ya sa hukumar ta shigar da shi ƙara a kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp