Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC
Published: 3rd, August 2025 GMT
Ya danganta mutuwar ta ƙanana da matsakaitan sana’oi a ƙasar, kan rashin samun rancen kudaɗen da za su ci gaba da ka kasuwancin su da rashin kayan aiki, da rashin kasuwa da ba a samu sosai da kuma rashin gudanar da ingantaccen shiri, kafin su fara gudanar da kasuwancinsu.
Ya sanar da cewa, ya zama wajibi, ƴan kasuwa musamman ƙanana da matsakaitan sana’oi a su sani cewa, bab wani batun yin wani holewa, na jin daɗi
Ya bayyana cewa, sama da ƙanana da matsakaitan sana’oi 40 a ƙasar nan, burin su ba shi ne, na ƙara yawan adadin alƙaluma ba, anna burin shi ne, na ƙarfafa zurewar kasuwancinsu.
“Alƙaluma sun nuna cewa, akwai ƙanana da matsakaitan sana’oi 40 a ƙasar nan, wanda hakan ya nuna cewa, sun kai kimanin kaso 96 a cikin dari, na kasuwancin da ake yi a ƙasar, inda kuma ake da kaso 84 na masu aikin yi, musamman duba da cewa, fannin na taimaka wa, wajen samar da ayyukan yi da kuma bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin ƙasar da ya kai kimanin kaso 48, a duk shekara, ” Inji Olowo.
Ya ci gaba da cewa, wannan sabon tsarin na kasuwacin, zai taimaka wajen cimma samar da tsarin tabatar da ci gaban ƙanana da matsakaitan sana’oin hannu.
“Babu wata hanya da zamu iya cimmma burin samaun dala tiriliyan daya, ba tare da yin amfani da ɓangaren ƙanana da matsakaitan sana’oin hannu,” A cewarsa.
Shi kuwa shugaban Cibiyar ta LCCI,Gabriel Idahosa, ya bayar da tabbacin cewa, Cibiyar za ta bayar da goyo baya domin a cimma wannan tsarin, na samar da takardun shedar gudanar da kasuwancin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
Wani sojan Ƙasar Amurka ɗan asalin Jihar Kano, Suleiman Isah, wanda yake aiki a rundunar sojin Amurka, ya ce ba zai yaƙi da ƙasarsa ta haihuwa ba saboda yaɗa labaran ƙarya game da yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.
Isah, wanda ya shiga rundunar sojin Amurka shekaru biyu da suka gabata, yana aiki ne da rundunar California Army National Guard, mai dakaru sama da 18,000.
Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin AmurkaA wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook wanda Aminiya ta tabbatar, Isah ya mayar da martani kan jita-jitar cewa Amurka za ta ɗauki matakin yaƙi a kan Najeriya saboda zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.
Ya bayyana cewa ba zai taɓa amfani da makami a kan mutanensa ba.
“Ba zan shiga Najeriya na kashe iyayena ba saboda ƙaryar cewa ana kashe Kiristoci,” in ji shi.
Ya ce duk da yake yana Allah-wadai da kashe-kashe da tashin hankali, bai kamata matsalar tsaro a Najeriya a danganta da wani addini ba.
“Ba zan ƙaryata batun kisan Kiristoci da Musulmai ba,” in ji shi.
“Shekau, Bello Turji, Dogo Gide da sauransu ba suna kai wa wani addini ɗaya hari ba ne kaɗai.”
Maganganun Isah na zuwa ne daidai lokacin Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi a kan Najeriya.
Sai dai Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini ba ce, inda ta ce matsalar na shafar Musulmai da Kiristoci baki ɗaya.