Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC
Published: 3rd, August 2025 GMT
Ya danganta mutuwar ta ƙanana da matsakaitan sana’oi a ƙasar, kan rashin samun rancen kudaɗen da za su ci gaba da ka kasuwancin su da rashin kayan aiki, da rashin kasuwa da ba a samu sosai da kuma rashin gudanar da ingantaccen shiri, kafin su fara gudanar da kasuwancinsu.
Ya sanar da cewa, ya zama wajibi, ƴan kasuwa musamman ƙanana da matsakaitan sana’oi a su sani cewa, bab wani batun yin wani holewa, na jin daɗi
Ya bayyana cewa, sama da ƙanana da matsakaitan sana’oi 40 a ƙasar nan, burin su ba shi ne, na ƙara yawan adadin alƙaluma ba, anna burin shi ne, na ƙarfafa zurewar kasuwancinsu.
“Alƙaluma sun nuna cewa, akwai ƙanana da matsakaitan sana’oi 40 a ƙasar nan, wanda hakan ya nuna cewa, sun kai kimanin kaso 96 a cikin dari, na kasuwancin da ake yi a ƙasar, inda kuma ake da kaso 84 na masu aikin yi, musamman duba da cewa, fannin na taimaka wa, wajen samar da ayyukan yi da kuma bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin ƙasar da ya kai kimanin kaso 48, a duk shekara, ” Inji Olowo.
Ya ci gaba da cewa, wannan sabon tsarin na kasuwacin, zai taimaka wajen cimma samar da tsarin tabatar da ci gaban ƙanana da matsakaitan sana’oin hannu.
“Babu wata hanya da zamu iya cimmma burin samaun dala tiriliyan daya, ba tare da yin amfani da ɓangaren ƙanana da matsakaitan sana’oin hannu,” A cewarsa.
Shi kuwa shugaban Cibiyar ta LCCI,Gabriel Idahosa, ya bayar da tabbacin cewa, Cibiyar za ta bayar da goyo baya domin a cimma wannan tsarin, na samar da takardun shedar gudanar da kasuwancin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
A yanzu haka dai ratotannin sun tabbatar da cewa APC da ADC suna gogayya wajen neman samun goyon bayan mutanen arewa kafin babban zaɓen 2027 ya ƙariso.
A ranar 1 ga Yuli, manyan ƴan adawa da suka hada da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi da dan takarar shugaban ƙasa a APC a 2023, Rotimi Amaechi, da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sun gabatar da ADC a matsayin hadakar jam’iyyar adawa domin ƙalubalantar Tinubu a 2027.
Shugabannin ADC sun ci gaba da yin ƙoƙari don samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da sauran yankuna tun bayan buɗe jam’iyyar.
A taron, Mark ya buƙaci shugabannin arewacin Nijeriya da su daina dabi’ar zargi da kuma amincewa na suna da alhakkin ƙalubalen da yankin ke fuskanta.
Ya ce, “Wannan wata dama ce da kuma girmamawa kasancewa a gabanku yau don magana kan batun halin da muke ciki a yanzu da kuma sauya makomarmu. Ina kira a gare ku mu yi gaggawar samun haɗin kai da ƙarfafa dangantaka a matsayin hanyar magance ƙalubalen da yankinmu ke fuskanta.
“Arewacin da muka sani ya kasance wata ƙasa ce mai ɗimbin tarihi da albarkatun ma’adinai da ƙasa noma da al’adu masu yawa da kuma ƙarfin tasiri.
“ɗuk da wadannan albarkatu, muna fuskantar ƙalubale masu yawa da suka hada da rashin tsaro da talauci da rikice-rikicen ƙabilanci da addinai da rarrabuwar kai a siyasa da matsalolin zamantakewar da na tattalin arziki. Wadannan ƙalubale ba su faru a dare daya ba kuma ba za su kau ba har sai mun hada kai wajen daukar matakin da ya dace.
“ɗole ne mu yarda da cewa mu ne masu gina matsalolinmu, dole ne mu daina zargin kawunanmu idan muna son samun mafita ɗorewar yankinmu.”
Tsohon shugaban majalisar dattawa ya ƙara bayyana cewa rarrabuwar kawuna ta hana wa arewacin ƙasar nan ci gaba, yayin da halin ko-in-kula da rashin daukan mataki ya ƙara zurfafa rarrabuwar da ta riga ta wanzu.
“ƙalubalen da ke fuskantar arewacin Nijeriya suna da alaƙa da juna. Rashin tsaro yana janyo ficewar masu zuba jari, wanda hakan ke ƙara tsananta talauci. Talauci yana jawo aikata muyagun laifuka. ƙabilanci na rage ƙarfin haɗin kanmu wajen neman kyakkyawan shugabanci. Rugujewar harkokin siyasa na tabbatar da cewa ba za a samu ingantaccen ci gaba a yankinmu. Wannan ba arewar da muka gada ba ne,” in ji ADC.
ɗon dawo da martaban yanki, Mark ya jaddada cewa akwai buƙatar matanen arewa su sake tunani da yin Nazari wajen daukan matakan da suka dace.
Ya kira ga dukkan mutanen arewa su dauki wannan a matsayin babban nauyi na haɓaka haɗin kai wajen inganta yankin maimakon zama a rarrabe.
A nasa ɓangaren, Lawal ya bayyana cewa gamayyyar ƙungiyar tuntuɓa kan harkokin siyasa ta arewa ta amince da ADC a matsayin jam’iyyar da ta iya tunkarar APC a zaɓen 2027.
Tsohon sakataren gwamnatin tarayya ya ce wakilai daga dukkanin jihohin arewa 19 sun cimma yarjejeniya cewa gwamnatin Shugaba Tinubu ba ta wani yuƙuri wajen magance matsalolin yankin.
Ya ce masu ruwa da tsaki daga arewacin ƙasar nan sun amince su tashi tsaye su yada saƙonsu wajen samn haɗin kan mutane da cimma matsaya kan zaɓe mai zuwa.
A martaninsa, daraktan yada labarai na APC ya ce jam’iyyar mai mulki ba ta damu da abin da ake kira da suna hadakar jam’iyya ba.
Ibrahim ya bayyana cewa Shugaba Tinubu na jagorantar gwamnati mai cike da samun goyon bayan dukkan mutanen Nijeriya.
Ya ce, “Jam’iyarmu ta APC, tana samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da kuma dukkan sauyan yankunan Nijeriya gaba daya, sai dai wadanda ba su gamsu ba da suka kafa jam’iyyar ADC a yanzu.”
Ya bayyana cewa APC ta jajirce wajen sabunta fata ga ƴan Nijeriya kuma yana nuna tabbacin cewa jam’iyyar za ta ƙara samun nasara a 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp