HausaTv:
2025-04-26@03:55:01 GMT

 Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa

Published: 12th, April 2025 GMT

Wanda ya jagoranci sallar juma’a a Tehran ya bayyana cewa; Tun cin nasarar juyin musulunci, Iran ta zabi hanyar tattaunawa, saboda ta tabbatar da kyakkyawar niyyarta da kuma aiki da hankali a mu’amalrta da duniya.

Limamin na Tehran Ayatullah Saiddiki ya ce, a yayin tattaunawar da za a yi a tsakanin Iran da Amurka wacce za ta kasance ta hanyar shiga tsakani, Iran za ta ji abinda daya bangaren zai fada, sannan kuma ta bayar da jawabi, domin tabbatarwa da duniya cewa ita daula ce mai aiki da hankali, kuma ba ta tsoron tattaunawa.

Ayatullah Siddiki ya yi ishara da zancen jagoran juyin musulunci akan yadda bangaren da ake tattaunawar ba ya aiki da abubuwan da aka cimmawa da amincewa da su.

Haka nan kuma limamin na Tehran ya ambato jagoran juyin musuluncin na Iran yana bayyana yadda Amurka take kiyayya da Jamhuriyar da musulunci na Iran da addinin musulunci da kuma alkur’ani mai girma, saboda asarar manufofinta da ta yi a cikin Iran.

Ayatullah Siddiki ya kuma amabci cewa maganar da shugaban kasar Amurka yake yi na tattaunawa kai tsaye da Iran ba koma ba ne, sai yaudara da ba ta da tushe. Kuma saboda yadda Amurka ba ta aiki da duk wata yarjejeniya da aka cimmawa, don haka zama da ita gaba da gaba domin tattaunawa bai dace da mu ba.

Har ila yau, ya kuma ce, Shirin Iran na Nukiliya na zaman lafiya yana ci gaba da samun bunkasa saboda jagoranci na hikima na jagoran juyin juya halin musulunci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Musanta Yin Shawarwari Ko Tattaunawa Da Amurka Kan Batun Harajin Kwastam

Ya kara da cewa, “Za mu gwabza yaki, idan yakin ya zama dole, amma kofofinmu a bude suke idan Amurka tana son a tattauna,” kana ya ce, Sin na neman hawa teburin tattaunawa da yin shawarwari ne kawai bisa daidaito, da mutuntawa da kuma samun moriyar juna. (Abdulrazaq Yahuza Jere).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muscat Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Kama Hanyar Zuwa Birnin Domin Ci Gaba Da Tattaunawa Da Amurka
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Natenyahu Ba Zai Hadi Fada Da Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ba
  • Muna Farin Ciki Da Karramawar Da Gwamna Abba Ke Samu Saboda Aiki Tukuru – Hon. Ibrahim
  • Faransa ta jaddada aniyarta na ci gaba da tattaunawar nukiliyar iran
  • Sin Ta Musanta Yin Shawarwari Ko Tattaunawa Da Amurka Kan Batun Harajin Kwastam
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Iran ta jinjinawa Sin da Rasha a matsayin kawayenta na kut-da-kut
  • Arakci: Mun Yi Tattaunawa Mai Kyau Da Mahukuntan Kasar China
  • Iran ta jaddada cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Gudanar Da Tattaunawa Kan Tsaronta Ba
  • Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa