Ana ci gaba da yin kiraye-kiraye ga HKI da ta kawo karshen hare-haren da take kai wa kasar Syria,jim kadan bayan da sojojin HKI su ka sanar da cewa; a karon farko jirgin sama maras matuki na ‘yan sahayoniya ya sauka a Suwaidah.

 A daren jiya Juma’a ne dai HKI ta kwana tana luguden wuta akan yankuna mabanbanta na kasar ta Syria da su ka hada da birnin Damascuss har da daura fa fadar shugaban kasa.

 HKI tana kai wannan hare-haren ne dai da sunan bayar da kariya ga ‘yan Duruz domin hana sojojin Syria ci gaba da kai musu hare-hare.

Jami’in diplomasiyyar MDD mai kula da kasar Syria Geir Otto Pedersen ya rubuta a shafinsa na X sakon yin tir da keta hurumin kasar Syria da Isra’ila take yi da su ka hada da birnin Damascus.

Haka nan kuma jami’in na MDD ya yi kira da a kawo karshen wadannan hare-haren akan Syria, da kauce kai wa farafen hula hari. Bugu da kari ya bayyana kai harin da cewa keta dokokin MDD ne da kuma kokarin hana tarwatsewar hadin kasar da ‘yancinta.

HKI ta bude kai hari ne akan kasar Syria da sunan kare ‘yan Duruz, da hakan yake kama hanya ce ta tarwatsa Syria da mayar da ita kananan kasashe.

Dama dai tun farko-farkon faduwar gwamnatin Syria, HKI take aiki tukuru domin ganin kasar ba ta ci gaba da zama a dunkule ba, ta tarwatse ra koma kananan kasashe.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Syria

এছাড়াও পড়ুন:

An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi

’Yan bindiga sun sace Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Honarabul Samaila Bagudu, a garinsu da ke Ƙaramar Hukumar Bagudu.

Rahotanni sun bayyana cewa ’yan bindigar sun mamaye garin Bagudu ne da yammacin ranar Juma’a tare da yin harbe-harbe don tsorata al’umma.

Maharan sun yi awon gaba da ɗan majalisar ne a kan hanyarsa ta dawowa daga masallaci bayan ya an idar da sallah masallaci a garin na Bagudu.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya ce an sanar da hukumomin tsaro, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da kuɓutar da Mataimakin Shugaban Majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan