Ana ci gaba da yin kiraye-kiraye ga HKI da ta kawo karshen hare-haren da take kai wa kasar Syria,jim kadan bayan da sojojin HKI su ka sanar da cewa; a karon farko jirgin sama maras matuki na ‘yan sahayoniya ya sauka a Suwaidah.

 A daren jiya Juma’a ne dai HKI ta kwana tana luguden wuta akan yankuna mabanbanta na kasar ta Syria da su ka hada da birnin Damascuss har da daura fa fadar shugaban kasa.

 HKI tana kai wannan hare-haren ne dai da sunan bayar da kariya ga ‘yan Duruz domin hana sojojin Syria ci gaba da kai musu hare-hare.

Jami’in diplomasiyyar MDD mai kula da kasar Syria Geir Otto Pedersen ya rubuta a shafinsa na X sakon yin tir da keta hurumin kasar Syria da Isra’ila take yi da su ka hada da birnin Damascus.

Haka nan kuma jami’in na MDD ya yi kira da a kawo karshen wadannan hare-haren akan Syria, da kauce kai wa farafen hula hari. Bugu da kari ya bayyana kai harin da cewa keta dokokin MDD ne da kuma kokarin hana tarwatsewar hadin kasar da ‘yancinta.

HKI ta bude kai hari ne akan kasar Syria da sunan kare ‘yan Duruz, da hakan yake kama hanya ce ta tarwatsa Syria da mayar da ita kananan kasashe.

Dama dai tun farko-farkon faduwar gwamnatin Syria, HKI take aiki tukuru domin ganin kasar ba ta ci gaba da zama a dunkule ba, ta tarwatse ra koma kananan kasashe.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Syria

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Wani mazaunin yankin, Abdullah Zuru, ya ce yankin ya samu zaman lafiya a baya, inda manoma suka koma gonakinsu kafin wannan mummunan hari.

Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi, Nafiu Abubakar, bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba dangane da harin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
  • Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom
  • Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025
  • Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kai Hare-Hare Kan Cibiyoyin Leken Asirin Isra’ila
  • Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Da Ke Tel-Aviv Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin