Aminiya:
2025-12-12@15:15:49 GMT

An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano

Published: 12th, April 2025 GMT

Yan sanda sun cafke wasu mutum takwas da ake zargi da faɗan daba a yankin Ƙofar Na’isa zuwa Ƙofar Ɗan Agundi da ke ƙwaryar birnin Kano.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan cikin wani saƙon bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba — Ganduje Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas

Kiyawa ya ce a ranar Alhamis da ta gabata ce suka samu kiraye-kirayen waya cewa wasu sun fito da makamai suna faɗan daba, lamarin da ya sanya aka tura jami’ai domin ɗaukar mataki.

Kakakin ’yan sandan ya ce a wannan lokaci babu wanda aka kama sakamakon arcewa da masu faɗan daban suka yi.

“Wasu sun fito faɗan daba, sun ji wa kansu raunuka a Ƙofar Na’isa, amma ba wanda ya zo wajen ’yan sanda a kai shi asibiti,” a cewar Kiyawa.

Sai dai Kiyawa ya ƙara da cewa jami’ansu sun sake komawa unguwar da daddare, inda suka cafke mutum takwas da raunuka a jikinsu da wuƙaƙe.

Kazalika, ya ce sun tattara sunayen mutane daban-daban da ake zarginsu da faɗace-faɗacen daba kuma nan ba da jimawa ba za su shiga hannu.

Aminiya ta rawaito yadda ake zaman ɗar-ɗar a yankin Ƙofar Na’isa da kuma Ƙofar Ɗan Agundi tun bayan dawowar faɗan daban a yayin bukukuwan sallah ƙarama da aka yi kwanan nan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faɗan Daba Jihar Kano Ƙofar Ɗan Agundi Ƙofar Na isa faɗan daba

এছাড়াও পড়ুন:

‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’

Wani mazaunin Kano, Namadi Bawa, ya bayyana yadda ya shiga cikin daji a Jihar Zamfara domin kai kudin fansa ga ’yan bindiga da suka sace ɗan uwansa, inda ya tarar da su cikin mawuyacin hali na rashin lafiya, kafin daga bisani ya samu ya kubutar da shi. A tattaunawar mutumin da Aminiya, y ace an sace ɗan uwan nasa ne a Gusau babban birnin jihar Zamfara, a kan hanyarsa ta dawowa daga Sakkwato.A cewar Namadi, ɗan uwansa ya ci karo da shingen da ya yi kama da na jami’an tsaro a hanya, sai dai daga baya aka gano ’yan bindiga ne suka yi masa kwantan bauna tare da wasu fasinjoji.

“Sun kira ni suka tambaya ko na san ɗan uwana, na ce eh. Suka ce sun sace shi kuma yana hannunsu. A lokacin kwana ɗaya kenan da sace shi,” in ji Namadi.

Cinikin kuɗin fansa da tafiya daji domin kai musu

Ya ce masu garkuwar sun fara neman kuɗin fansa har Naira miliyan 16, amma bayan tattaunawa aka rage zuwa miliyan bakwai.

Namadi ya ce masu garkuwar sun yi gargaɗin cewa ba za su lamunci rage wani abu daga adadin kudin da aka yi cinikin ba, suna gargaɗin cewa muddin suka ƙirga kuɗin suka ga ba su cika ba, za a ga ba daidai ba.

“Sun ja hankali cewa kada a rage ko ƙwandala a ciki, idan aka rage za a ga ba daidai ba,” in ji shi.

Namadi ya bayyana yadda ya je da kansa ya kai kudin cikin daji.

A cewarsa, an umurce shi ya tsaya a wani ƙauye kafin daga bisani a nuna masa hanyar shiga. Daga bisani aka ba shi wata riga ya saka kafin ya isa wurin da aka karɓi kudin.

“Na zaci za su ƙirga kudin, amma sai suka tattaka su da ƙafa, suka ce sun cika. Bayan haka suka ce na gangaro daga kan dutsen da suka kai ni. Na yi ta kallo ko zan ga ɗan uwana, amma daga baya ne suka nuna min shi tare da wasu da aka sace, duk suna kwance cikin yanayin rashin lafiya,” in ji shi.

Yanayin dajin da masu garkuwar

Namadi ya ce yanayin da ya tarar da su ya nuna suna fama da cutar kwalara, inda aka ajiye su a bukka a tsakiyar dajin da ba motar da za ta iya shiga sai babur.

“Na san idan a wannan yanayin ne, ba za su yi dogon zango ba. Ta su za ta kare,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ɗan uwansa da sauran da aka sace sun shiga mawuyacin hali, inda dole ne aka kai ɗan uwansa asibiti bayan an karɓo shi saboda yanayin da aka same shi.

Namadi ya kuma ce duk da fargaba da tashin hankalin da ya shiga, addu’a ce ta taimaka masa ya dawo gida lafiya.

“Mu ci gaba da addu’a saboda tana da tasiri a kan mutanen nan. Insha Allahu Allah zai kawo ƙarshen su,” in ji shi.

Cin karo da wasu masu garkuwar a hanyar dawowa

Bayan ya karɓo ɗan uwansa, Namadi ya ce a hanyarsa ta fita daga dajin ya sake cin karo da ’yan bindigar sun kamo wasu mutanen, suna kaɗa su zuwa cikin daji.

“Sun ba ni shawara kada na bi ta inda na zo, saboda akwai ƙungiyoyin masu garkuwa da dama a yankin waɗanda ba sa ga maciji da juna da za su iya sake kama mu,” in ji shi.

Daga nan sai ya ce duk da muggan makaman da ’yan bindigar ke da su, ba su fi ƙarfin gwamnati ba.

Ya yi kira ga gwamnati da ta ƙara ƙoƙari wajen kawar da ’yan bindiga a yankin, tare da fatan addu’ar jama’a za ta taimaka wajen kawo ƙarshen matsalar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu Ta Umarci EFCC Ta Biya Wani Ƴan Kasuwar Kano Miliyan 5, Ta Nemi Afuwar Su
  • ‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi