An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
Published: 12th, April 2025 GMT
’Yan sanda sun cafke wasu mutum takwas da ake zargi da faɗan daba a yankin Ƙofar Na’isa zuwa Ƙofar Ɗan Agundi da ke ƙwaryar birnin Kano.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan cikin wani saƙon bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba — Ganduje Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a LegasKiyawa ya ce a ranar Alhamis da ta gabata ce suka samu kiraye-kirayen waya cewa wasu sun fito da makamai suna faɗan daba, lamarin da ya sanya aka tura jami’ai domin ɗaukar mataki.
Kakakin ’yan sandan ya ce a wannan lokaci babu wanda aka kama sakamakon arcewa da masu faɗan daban suka yi.
“Wasu sun fito faɗan daba, sun ji wa kansu raunuka a Ƙofar Na’isa, amma ba wanda ya zo wajen ’yan sanda a kai shi asibiti,” a cewar Kiyawa.
Sai dai Kiyawa ya ƙara da cewa jami’ansu sun sake komawa unguwar da daddare, inda suka cafke mutum takwas da raunuka a jikinsu da wuƙaƙe.
Kazalika, ya ce sun tattara sunayen mutane daban-daban da ake zarginsu da faɗace-faɗacen daba kuma nan ba da jimawa ba za su shiga hannu.
Aminiya ta rawaito yadda ake zaman ɗar-ɗar a yankin Ƙofar Na’isa da kuma Ƙofar Ɗan Agundi tun bayan dawowar faɗan daban a yayin bukukuwan sallah ƙarama da aka yi kwanan nan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faɗan Daba Jihar Kano Ƙofar Ɗan Agundi Ƙofar Na isa faɗan daba
এছাড়াও পড়ুন:
An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
Wasu mahara da ake zargin ‘yan Boko Haram ne sun kai hari gidan babban Jami’in kula da ofishin ‘yan sandan na Tattaɓa, ASP Mohammed Modu, da ke yankin Bara a ƙaramar hukumar Gulani, Jihar Yobe.
Kamar yadda rahoton Jami’an tsaro ke nunawa cewa, da misalin ƙarfe 1:30 na tsakar daren ranar 9 ga Disamba, maharan suka mamaye gidaje uku na jami’in, suka sace babur ɗinsa na Haojue da kekuna uku da mota ƙirar Golf 3, da sauran kayansa kafin su ƙona gidaje uku da motar Honda Civic.
Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota Manchester United ta shiga zawarcin Sergio RamosAn yi zargin cewa, wani mai kai rahoto ne ga ‘yan ƙungiyar da ke cikin al’ummar wannan yankin ya bada rahoton Jami’in ga waɗannan maharan.
Jami’an tsaro sun ziyarci wurin da lamarin ya faru kuma sun tattara bayanai game da ɓarnar, ba tare da an samu rahoton asarar rayuka ba.
An shawarci jami’in da ya yi taka-tsantsan yayin da ake ƙara tsaurara sa ido da sintiri a yankin don hana sake kai hari a yankin.