An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
Published: 12th, April 2025 GMT
’Yan sanda sun cafke wasu mutum takwas da ake zargi da faɗan daba a yankin Ƙofar Na’isa zuwa Ƙofar Ɗan Agundi da ke ƙwaryar birnin Kano.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan cikin wani saƙon bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba — Ganduje Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a LegasKiyawa ya ce a ranar Alhamis da ta gabata ce suka samu kiraye-kirayen waya cewa wasu sun fito da makamai suna faɗan daba, lamarin da ya sanya aka tura jami’ai domin ɗaukar mataki.
Kakakin ’yan sandan ya ce a wannan lokaci babu wanda aka kama sakamakon arcewa da masu faɗan daban suka yi.
“Wasu sun fito faɗan daba, sun ji wa kansu raunuka a Ƙofar Na’isa, amma ba wanda ya zo wajen ’yan sanda a kai shi asibiti,” a cewar Kiyawa.
Sai dai Kiyawa ya ƙara da cewa jami’ansu sun sake komawa unguwar da daddare, inda suka cafke mutum takwas da raunuka a jikinsu da wuƙaƙe.
Kazalika, ya ce sun tattara sunayen mutane daban-daban da ake zarginsu da faɗace-faɗacen daba kuma nan ba da jimawa ba za su shiga hannu.
Aminiya ta rawaito yadda ake zaman ɗar-ɗar a yankin Ƙofar Na’isa da kuma Ƙofar Ɗan Agundi tun bayan dawowar faɗan daban a yayin bukukuwan sallah ƙarama da aka yi kwanan nan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faɗan Daba Jihar Kano Ƙofar Ɗan Agundi Ƙofar Na isa faɗan daba
এছাড়াও পড়ুন:
Babu Janar ɗin da ISWAP ta kama a Borno — Sojoji
Rundunar Soji ta ƙaryata rahotannin da ke cewa an yi garkuwa da kwamandan Bitget ta 25 da ke Jihar Borno a wani harin kwanton ɓaunan mayaƙan ƙungiyar ISWAP.
Ta buƙaci jama’a su yi watsi da wannan labarin ƙarya, tare da yin addu’ar samun nasarar sojojin Najeriya da ke bakin daga.
Rundunar ta ce sojojin sun murƙushe wani harin kwanton ɓauna da ISWAP ta kai musu a yayin da suke sintiri domin kare al’ummomin da ke kewaye da Wajiroko a yankin Azir Multe a Ƙaramar Hukumar Damboa da ke Jihar Borno.
Ta ce sojojin sun gamu da kwanton ɓauna ne daga ’yan ta’adda yayin da suke dawowa daga aikin sintiri a gefen Dajin Sambisa.
Mayaƙan ISWAP sun sace Janar sun kashe sojoji a Borno Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a NejaRundunar ta jaddada cewa Kwamandan Brigedi ta 25, Birgediya Janar M. Uba, shi ne ya jagoranci tawagar, wacce ta haɗa da mambobin CJTF, kuma sun koma sansaninsu lafiya.
Ta ce sojojin sun fuskanci harin ne cikin ƙwazo, inda suka yi musayar wuta da makiya har suka fatattake su.
Sanarwar rundunar, ta hannun muƙaddashin kakakinta, Laftanar-Kanar Appolonia Anele, ta ce a yayin arangamar, sojoji biyu da mambobin CJTF biyu sun kwanta dama.
Hedikwatar tsaro ta yaba da jarumtakar dakarun, tare da yin ta’aziyya ga iyalai da abokan aikin waɗanda suka rasa rayukansu.
Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar-Janar Waidi Shaibu, ya jinjina wa jarumtar dakarun da ke ci gaba da aiki a ɗaya daga cikin yankunan da suka fi haɗari a ƙasar, yana mai cewa sadaukarwarsu abin karramawa ne a kullum wajen kare Najeriya.