An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
Published: 12th, April 2025 GMT
’Yan sanda sun cafke wasu mutum takwas da ake zargi da faɗan daba a yankin Ƙofar Na’isa zuwa Ƙofar Ɗan Agundi da ke ƙwaryar birnin Kano.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan cikin wani saƙon bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba — Ganduje Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a LegasKiyawa ya ce a ranar Alhamis da ta gabata ce suka samu kiraye-kirayen waya cewa wasu sun fito da makamai suna faɗan daba, lamarin da ya sanya aka tura jami’ai domin ɗaukar mataki.
Kakakin ’yan sandan ya ce a wannan lokaci babu wanda aka kama sakamakon arcewa da masu faɗan daban suka yi.
“Wasu sun fito faɗan daba, sun ji wa kansu raunuka a Ƙofar Na’isa, amma ba wanda ya zo wajen ’yan sanda a kai shi asibiti,” a cewar Kiyawa.
Sai dai Kiyawa ya ƙara da cewa jami’ansu sun sake komawa unguwar da daddare, inda suka cafke mutum takwas da raunuka a jikinsu da wuƙaƙe.
Kazalika, ya ce sun tattara sunayen mutane daban-daban da ake zarginsu da faɗace-faɗacen daba kuma nan ba da jimawa ba za su shiga hannu.
Aminiya ta rawaito yadda ake zaman ɗar-ɗar a yankin Ƙofar Na’isa da kuma Ƙofar Ɗan Agundi tun bayan dawowar faɗan daban a yayin bukukuwan sallah ƙarama da aka yi kwanan nan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faɗan Daba Jihar Kano Ƙofar Ɗan Agundi Ƙofar Na isa faɗan daba
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
An tabbatar da mutuwar mutum ɗaya, tare da ƙona gidaje sama da 100, wanda ake zargin wasu makiyaya ne a unguwannin manoma da ke Ƙaramar hukumar Karim Lamido a Jihar Taraba suka yi.
An kai wa mazauna unguwar Bandawa Gwenzu, waɗanda suka haɗa da: Gwenzu da Langwanshin da Danzhan hari a daren Laraba.
Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a BornoDa yake magana da tashar Talabijin na Channels TV ta wayar tarho a ranar Alhamis, shugaban matasan Uunguwar yankin, Ishaya Peter ne ya bayyana harin a matsayin rashin gaskiya da abu mai muni kuma ya yi Allah-wadai da harin.
A cewarsa, mazauna garin na zaune suna tattaunawa, kwatsam sai suka ji ƙarar harbe-harbe daga nesa lamarin da ya sanya suka yi gaggawar gudu domin tsira da rayukansu.
Ya ce, ya ji muryoyin makiyaya tare da wasu maƙwabtansu da ke tunkarar ƙauyen, kuma duk yunƙurin hana su ya ci tura.
Peter ya ce sun bayar da sanarwar gargaɗi na sa’o’i kafin su kai harin ga hukumomin tsaro, amma ba a ɗauki matakin daƙile faruwar lamarin ba.
Ba za mu iya daƙile harin ba saboda sun zo da bindigogi kuma mu mutane ne masu son zaman lafiya ba mu da makami sai baka da kibiya, abin yankar ciyawa shi ke nan,” inji shi.
“Ɗaya daga cikinmu ya mutu ne dalilin rashin iya yin iyo a lokacin da yake tsallaka kogi, yayin da suka far mana, ƙauyukan ba kowa ne kuma har yanzu muna ƙirga asarar da muka yi.
“An buƙaci mata da yara da su ƙauracewa ƙauyukan saboda ba mu san lokacin da za su sake kai farmaki ba.”
Rundunar ‘yan sandan Jihar Taraba ba ta mayar da martani kan wannan sabon harin ba.
Idan dai za a iya tunawa, a cikin watan Mayun wannan shekara ne makamancin wannan lamari ya faru a yankin na Bandawa, wanda ya yi sanadin mutuwar mutum uku tare da jikkata wasu da dama.