Mai Martaba Sarkin Dutse, Dr Hameem Nuhu Muhammadu Sunusi ya kaddamar da rabon zakkar kudi ta shekarar musulunci ta 1446 a gundumar Yayari dake Karamar Hukumar Buji.

A jawabin sa, Mai Martaba Sarkin ya ja hankalin al’umma da su ci gaba da fitar da hakkin Allah domin samun makoma a nan duniya da kuma gobe kiyama.

Ya nuna gamsuwa da nasarorin da Gundumar ta samu wajen tattara zakka a masarautar sa.

Daga bisani ya karrama Hakimin Yayari, Alhaji Garba Muhammad da Dagaci da kuma Mai Unguwar cikin garin Yayari.

A jawabin sa, Sa’in Dutse, Mallam Mahmud Yunusa yace gundumar Yayari ce ta zo na 1 a tattara zakkar kudi yayin da Gundumomin Gantsa da Fagam suka zo na 2 da na 3.

 

Ya ce an raba zakkar fiye da naira miliyan goma ga mutane 300, inda wasu suka sami zakkar naira dubu 20 zuwa naira dubu 35.

A jawabin sa, shugaban Karamar Hukumar Buji Najibullah Falalu Tukur Gantsa yace Karamar Hukumar zata ci gaba da hadin kai da gundumar Yayari da sauran gundumomin hakimanta wajen ganin Karamar Hukumar ta rike matsayinta na ja gaba wajen tattara zakka.

Ya kuma yabawa mai Martaba Sarkin Dutse bisa jajircewar sa wajen ganin al’umma suna fitar da hakkin Allah.

 

Mai martaba sarki ya samu rakiyar Galadiman Dutse da sauran ‘yan majalissar Sarki.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Mai Martaba Sarkin Karamar Hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026

Gwamnatin Jihar Gombe ta ƙaddamar da taron sauraron ra’ayoyi jama’a kan shirye-shiryen tsara kasafin kuɗin shekarar 2026 a wani yunƙuri na jaddada ƙudirinta na gudanar da mulki cikin gaskiya da haɗin kai.

Da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Gwamnan Jihar, Dakta Manassah Daniel Jatau, ya bayyana cewa wannan mataki na nuna jajircewar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya wajen tabbatar da cewa ra’ayoyin jama’a na taka muhimmiyar rawa a tsara kasafin kuɗi da aiwatar da shi.

Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja

Ya ce tattaunawar ta bai wa gwamnati damar haɗa kai da sarakunan gargajiya, mata, matasa, ƙungiyoyin farar hula da sauran masu ruwa da tsaki, domin bayar da shawarwari kan muhimman fannoni kamar ilimi, lafiya, noma da gine-gine, da za su amfanar da al’umma baki ɗaya.

Dakta Jatau ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta samu ci gaba wajen alkinta kuɗaɗe cikin tsari da gaskiya, wanda hakan ya sa Gombe ke samun matsayi mai kyau a ɓangaren ingantaccen gudanar da kuɗi da sauƙin kasuwanci a Najeriya.

“Kasafin kuɗin 2026 zai mai da hankali ne kan ci gaba da ayyukan da ake yi, tare da ƙara zuba jari a muhimman fannoni, da tabbatar da daidaito da manufofin ci gaban ƙasa da na duniya,” in ji shi.

A nasa ɓangaren, Kwamishinan Kasafi da Tsare-Tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Salihu Baba Alkali, ya bayyana taron a matsayin wata hanya ta buɗe ƙofa tsakanin gwamnati da jama’a domin samun fahimta da amincewa.

Ya buƙaci mahalarta taron da su bayar da shawarwari masu amfani da za su taimaka wajen samar da kasafin kuɗin da zai kasance mai ɗorewa kuma mai amfani ga kowa da kowa.

Kwamishinan ya kuma gode wa mahalartan bisa yadda suka bayar da gudunmawa, yana mai tabbatar da cewa za a yi la’akari da shawarwarinsu a cikin tsarin ƙarshe na kasafin kuɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
  • Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba