Aminiya:
2025-11-18@11:02:30 GMT

Gwamna Fubara ya kori duk Kwamishinonin Ribas

Published: 2nd, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara ya kori dukkan Kwamishinoni da sauran masu riƙe da muƙamai a gwamnatinsa.

A cewar wata sanarwa da aka fitar a Fatakwal babban birnin jihar a yammacin Laraba ta hannun babban sakataren yaɗa labaransa, Nelson Chukwudi matakin korar ya fara aiki nan take, kuma ya biyo bayan hukuncin da kotun ƙoli da ta yanke na baya-bayan nan.

Matan Sojojin da aka tsare sun nemi a yi wa mazajensu afuwa 2027: Zan iya haƙura da takara in mara wa matashi mai jini a jika baya – Atiku

Gwamnan, a yayin wani zama da ya yi da hadimansa domin murnar cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai a gidan gwamnati da ke Fatakwal, ya gode wa jami’an da ke barin gado bisa ayyukansu da kuma gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar cikin shekaru biyu da suka gabata.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Gwamnan Jihar Ribas, Sir Siminalayi Fubara, ya godewa ’yan muƙarrabansa bisa ayyukansu da kuma gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar cikin shekaru biyu da suka gabata.

“Gwamnan ya bayyana mahimmancin ’Yancin kan Nijeriya, ya kuma yi kira ga dukkan ’yan Nijeriya da su yi aiki tare da Shugaban Ƙasa domin gina ƙasa mai zaman lafiya da tsaro da wadata da kyakkyawar makoma ga kowa da kowa.

Gwamnan ya sauke dukkan kwamishinoni da sauran jami’an gwamnati da hukuncin Kotun Ƙoli ya shafa na naɗin nasu nan take.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwamishinoni Siminalayi Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Dole ku ceto daliban da aka sace a Kebbi Shugaban Sojoji

Babban Hafsan Sojin Kasa na Najeriya, Laftanar-Janar Waidu Shuaibu, ya umarni dakarun soji cewa ya zama tilas su nemo sannan su ceto daliban da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Makarantar ’Yan Mata ta Gwamnati (GGCSS) da ke yankin Maga a Jihar Kebbi.

Janar Waidi Shuaibu ya bayar da umarnin ne a yayin ziyarar aiki da ya kai, Jihar Kebbi, washegarin harin ’yan bindiga suka kai makarantar da ke Karamar Hukumar Danko Wasagu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dole ku ceto daliban da aka sace a Kebbi Shugaban Sojoji
  • GGCSS Maga: Halin da iyaye ke ciki bayan sace ’ya’yansu
  • Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
  • Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
  • Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • Fintiri ya yi watsi da korar Wike daga PDP
  • PDP ta kori Wike, Fayose, Anyanwu da wasu
  • Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya