Matan Sojojin da aka tsare sun nemi a yi wa mazajensu afuwa
Published: 2nd, October 2025 GMT
Matan Sojoji da aka tsare bisa laifuka daban-daban a yaƙin da ake yi da ’yan Boko Haram ko Ƙungiyar ISWAP a garin Maiduguri jihar Borno, a bikin cika shekaru 65 da samun ’yancin kai sun roƙi shugaba Bola Tinubu da hukumomin soja da su tausaya musu ta hanyar yi wa mazajensu afuwa.
Matan da yawansu ya haura 30 tare da wasu yara ’yan ƙasa da shekara biyu da suka haɗa da ‘yan uwa da abokan arziki sun ziyarci cibiyar ’yan jarida ta Nijeriya (NUJ) da ke Maiduguri a ranar Laraba don miƙa wannan koke na su.
Mai magana da yawun, su Madam Rose Emmanuel David a lokacin da take zantawa da manema labarai ta ce, an tsare wasu mazajensu ta hanyar aikata ƙananan laifuffuka sama da shekara guda.
Rose ta jaddada cewa hakan ya jefa su cikin halin wahala matuƙa musamman wajen shawo kan matsalolin iyali, saboda hakan ya tilasta musu yin sana’o’in da ba su dace da su ba domin ɗaukar nauyin kuɗin makaranta da ciyar da ‘ya’yansu.
Sun yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya da hukumomin soji sun shafe shekaru suna yin afuwa ga ’yan Boko Haram, ’yan fashi da sauran masu aikata muggan laifuka.
“Don haka ya zama wajibi su bayyana ra’ayinsu, ta hanyar roƙo a madadin mazajensu da ke tsare a ofishin ’yan sandan Soja (MP) da ke Maiduguri ko su ma sa samu ‘yancinsu da kuma haɗuwa da mu iyalansu.”
“Muna nan a madadin mazajenmu da aka tsare sojojin Nijeriya a ofishin ’yan sandan Soja na runduna ta 7 da ke Maiduguri don miƙa kokenmu.”
“Muna cikin tawali’u da neman jin ƙai da gafara, kasancewar da yawa an tsare su tsawon watanni da shekaru kan laifuka dabam-daban, tun daga lokacin sun amince da kura-kuransu, sun yi tunani sosai, kuma yanzu suna neman dama ta biyu don yi wa ƙasarsu hidima.
“Muna cikin girmamawa muna kira ga mai girma shugaban ƙasa, kuma babban kwamandan sojojin ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da ya yi musu afuwar shugaban ƙasa.”
“Muna kuma kira ga majalisun dokoki na ƙasa, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, da dukkan ’yan Nijeriya da su goyi bayan wannan roƙo na mu don ganin an sako mana mazajenmu, wadda ya kamata a tuna cewa, an yi afuwa ga tubabbun ‘yan tada ƙayar baya da ‘yan bindiga da suka taɓa tayar da fituntuni a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Ta Kai Wa Sojojin MDD Hari A Kasar Lebanon
Tankar yakin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta bude wuta akan dakarun zaman lafiya na MDD dake kudancin Lebanon
Dakarun zaman lafiyar na MDD dake kudancin Lebanon (UNIFiL) sun sanar da cewa tankar yakin “Isra’ila” ta buder wuta akansu, da hakan ya tilasta musu guduwa zuwa inda za su buya.
Rundunar ta “UNIFIL” ta kuma bayyana abinda ya faru da cewa keta kudurin MDD ne mail amba 1701, tare da yin kira ga “Isra’ila’ da ta dakatar da abinda take yi.
Wannan dai ba shi ne karon farko ba da dakarun zaman lafiyar na MDD suke keta kudurin MDD ta hanyar kai hare-hare da kuma yin kutse a cikin yankunan dake kan iyaka.
A ranar 27 ga watan Oktoba ma dai rundunar ta MDD ta sanar da cewa ta harbo wani jirgin sama maras matuki na Haramtacciyar Kasar Isra’ila da ya rika shawagi akan sojojinta masu sintiri da zummar kai musu hari. Haka nan kuma a waccan ranar wani jirgin saman maras matuki na “Isra’ila” ya jefa bom a kusa da dakarun a garin Kafar-kalla.
A baya a ranar 12 ga watan Oktoba wani jirgin na “Isra’ila” da ya jefa bom, ya jikkata daya daga cikin dakarun zaman lafiyar na MDD.
An kafa rundunar UNFEL ne dai a 1978 bayan da sojojin Haramtacicyar Kasar Isra’ila su ka kutsa cikin kudancin Lebanon, an kuma karfafa ayyukan rundunar a 2006 da fitar da kuduri 1701. Da akwai sojoji 10,000 akarkashin wannan rundunar domin sa ido akan dakatar da yaki daga Isra’ila da kuma karfafa sojojin Lebanon a kudancin tafkin “Litani”.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya November 16, 2025 Kasar Afghanistan Na Kokarin Karkata Akalar Kasuwancinta Zuwa Iran November 16, 2025 Kanada Ta Tsare Tsohon Wakilin Majalisar Dinkin Duniya Mai Bincike Kan Laifukan Yakin Israila. November 16, 2025 Zarfi: HKI Ce Kawai Take Ayyana Nukiliya Ba Bisa Kaida Ba A Yammacin Asiya. November 16, 2025 Shugaban kasar venuzuwela Yayi Tir Da Atisayan Soji Da Trinidad and Tobago Ke yi. November 16, 2025 IRGC ta kama wani jirgin ruwan dakon mai a gabar tekun kudancin Makran November 16, 2025 Iran : sojojin Amurka a yankin Caribbean barazana ne ga zaman lafiya November 16, 2025 Lebanon za ta kai karar Isra’ila a MDD kan gina Katanga a iyakarta November 16, 2025 AU ta sake watsi da ikirarin Trump cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya November 16, 2025 Falasdinu ta yi wasan sada zumunci a Spain November 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci