Babu wanda na cewa zan janyewa takara a 2027 — Atiku
Published: 2nd, October 2025 GMT
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya musanta cewa yana son ya janyewa wani takara saboda matashin ɗan takara kafin zaɓen 2027.
A baya dai tsohon mataimakin shugaban Ƙasa Atiku ya nuna sha’awarsa ta tsayawa takarar shugaban Ƙasa a 2027.
An kama masu kai wa ’yan bindiga makamai da ƙwayoyi Gwamna Fubara ya kori duk Kwamishinonin jiharAtiku dai ya fice daga Jam’iyyar PDP bayan ya tsaya takarar Shugaban Ƙasa a zaɓen da ya gabata.
A watan Agusta, Atiku Abubakar da wasu ’yan siyasa na adawa da suka haɗa da: tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, tsohon Gwamnan Ribas, Rotimi Amaechi da tsohon Gwamnan Anambra, Peter Obi da dai sauransu, sun koma jam’iyyar ADC a matsayin jam’iyyar da za su yi amfani da ita wajen ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a 2027.
A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Paul Ibe ya fitar Atiku ya ce, “Ya zama dole a fayyace wasu rashin fahimtar wasu kalamai da suka taso daga rahoton wata hira da Atiku Abubakar da wasu sassan kafafen yaɗa labarai suka yi da BBC Hausa.
“Bayan nazartar faifan bidiyo da bayanan hirar – a ainihin Hausa da fassarar Turanci – ya nuna cewa ko kaɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasar bai fito fili ya bayyana ko ya ba da shawara ko ma ya nuna cewa yana da niyyar janyewa ga kowa ba.”
A cewarsa, “Atiku Abubakar a fili ya faɗa cewa matasa, da sauran masu neman takarar shugaban ƙasa, suna da ‘yancin shiga yin takara.”
Ya kuma ƙara jaddada cewa, “idan matashin ɗan takara ya fito ta hanyar nasarar lashe zaɓen fidda gwani, zai goyi bayan wannan ɗan takara ba tare da wani shakku ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alhaji Atiku Abubakar Atiku Abubakar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati, UNICEF da ’yan jarida sun haɗa don yaƙar cututtukan da aka manta da su a Gombe
Gwamnatin Tarayya, tare da haɗin gwiwar UNICEF da gwamnatin Jihar Gombe, sun shirya taron wayar da kai da ’yan jarida domin yaƙi da cututtukan da ba a cika kula da su ba.
Ofishin UNICEF na Bauchi ya haɗa kai da ’yan jarida da JPHCDA da wakiliyar Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, Hauwa Abubakar, domin tattaunawa kan yadda za a rage yaɗuwar cututtukan a jihar.
Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — Kwankwaso Babu Janar ɗin da ISWAP ta kama a Borno — SojojiA taron, ’yan jarida sun samu damar jin bayanai daga masana da kuma yadda aikace-aikacen yaƙi da cututtukan ke tasiri a cikin al’umma.
Gwamnatin Jihar Gombe tana ware Naira miliyan 25 duk shekara domin yaƙi da NTDs, amma har yanzu akwai wuraren da ake buƙatar ƙarin tallafi.
Ƙungiyar Amen Health Care and Empowerment Foundation, ta ce tun 2015 ake samun ci gaba wajen yaƙi da cututtuka kamar onchocerciasis, lymphatic filariasis, da schistosomiasis.
Ƙungiyar ta kuma ce an yi wa waɗanda ke fama cututtukan tiyata kyauta.
Wakilin UNICEF, Hillary Adie, ya ce matsanancin talauci da rashin tsafta na taimaka wa yaɗuwar cututtukan.
Ya jaddada muhimmancin tsaftar muhallin zama.
Hauwa Abubakar, ta yi kira da a ƙara haɗa kai tsakanin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.
Ita kuwa Shugabar UNICEF ta Bauchi, Dokta Nuzhat Rafique, ta yaba wa Gombe kan ci gaban da ta samu, tare da roƙon ’yan jarida su ci gaba da wayar da kan jama’a game da cututtukan.