Malaman Kwalejin Nuhu Bamalli sun tsunduma yajin aiki
Published: 30th, September 2025 GMT
Malaman Kwalejin Kimiyya da Ƙere-ker ta Nuhu Bamalli da ke Zariya a Jihar Kaduna sun tsunduma yajin aiki.
Ƙungiyar Malaman Kwalejin Kimiyya da Ƙere-kere (ASUP) reshen makarantar ta fara yajin aikin ne daga yau Talata, 39 ga Satumba, 2025.
Ƙungiyar ta fara yajin aikin ne bayan zaman da ta yi da wakilan gwamnatin jihar, inda Babban Sakataren Gwamnatin Jihar, ya buƙaci su ƙara haƙuri, yana mai alamta cewa Gwamna Uba Sani ya ba da izinin biyan buƙatunsu.
Sanarwar da Kwamared Usman Shehu Suleiman ya sanya wa hannu ta ce, “Daga Talata , 30 ga Satumba 2025 mu fara yajin aiki har sai abin da hali ya yi.”
An shiga taron gaggawa kan takun saƙar PENGASSAN da Matatar Dangote ASUU ta bayar da wa’adin tsunduma yajin aiki a faɗin NijeriyaYa ƙara da cewa yajin aikin zai ci gaba da gudana har zuwa lokacin da suka samu amincewar gwamnati da buƙatun malaman a hukumance.
Uwar ƙungiyar ASUP ta buƙaci tafiya yajin aikin sai abin da hali ya yi ne idan gwamnatin jihar ba ta amince da tsarin albashin Kwalejojin Kimiyya da Ƙere-kere (PSS) bayan albashin watan Satumba.
Sauran buƙatun sun haɗa da aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS/CONTEDIS ga ɗauƙacin ma’aikata a manyan makarantu mallakar jihohi da kuma ƙara yawan shekarun yin ritayar waɗanda ba malamai ba zuwa shekara 65.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kimiyya da Ƙere ƙere Yajin aiki yajin aikin
এছাড়াও পড়ুন:
Na kusa komawa APC – Gwamnan Taraba
Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya ce zai fice daga jam’iyyar PDP tare da sauya sheƙa zuwa APC a hukumance a ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamba.
Ya bayyana haka ne yayin da yake duba aikin gyaran Filin Wasanni na Jolly Nyame da ke Jalingo a ƙarshen mako.
Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — Muftwang Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasaYayin da yake magana da ’yan jarida, Gwamna Kefas, ya ce ya yanke shawarar ficewa daga PDP ne saboda nemo hanyar da zai amfanar da al’ummar Taraba.
Ya ce: “Zan sauya sheƙa a hukumance daga PDP zuwa APC a ranar 19 ga watan Nuwamba. Wannan sauyi zai amfanar da al’ummar Taraba.”
Ya ƙara da cewa ana ci gaba da shirye-shiyen bikin tarbarsa.
Da aka tambaye shi ko akwai wani sharaɗi da aka gindaya masa kafin ya sauya sheƙa, ya ce babu ko ɗaya.
Mambobin Majalisar Zartarwa ta jihar sun nuna cikakken goyon bayansu ga gwamnan.
Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Muslim Aruwa, wanda ya yi magana a madadin sauran kwamishinoni, ya ce dukkanin muƙarraban gwamnan za su bi shi zuwa APC.
Ya ce: “Gwamna shi ne shugabanmu, duk inda ya je muna tare da shi.”
Aruwa, ya bayyana cewa shiga jam’iyyar da mulkin tarayya zai samar wa jihar ci gaba.
Ya ƙara da cewa: “Wannan sauya sheƙa na mutanen Taraba ne baki ɗaya, kuma muna tare da shi ɗari bisa ɗari.”