Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
Published: 14th, October 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta kammala aikin titin Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano kafin ƙarshen shekara mai zuwa.
Ministan Kasa a Ma’aikatar Ayyuka, Barista Bello Muhammad Goronyo, ne ya bayyana haka bayan ya kai ziyara domin duba yadda aikin ke tafiya a ranar Talata.
Barista Goronyo ya ce Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya ba da umarni cewa a tabbatar da kammala aikin cikin lokaci, ganin muhimmancin hanyar wajen haɗa Arewa da Kudancin ƙasar da kuma babban birnin tarayya Abuja.
Ya bukaci kamfanin da ke gudanar da aikin da ya hanzarta kammalawa kafin wa’adin da aka tsara, tare da gyara ramukan da ke hanyar domin sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a.
Ministan ya kuma nuna damuwarsa kan halin da masu amfani da hanyar ke ciki, inda ya jaddada bukatar gaggauta cike ramuka da gyaran sassan da ke da matsala domin inganta sufuri da tsaron fasinjoji.
Rel/Ibrahim Idris K/Namoda
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi
Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, ya caccaki matakin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta dauka na fara yajin aiki na tsawon makonni biyu, yana mai bayyana matakin a matsayin wanda bai kamata ba kuma bai dace ba ganin irin kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na biyan kusan dukkanin bukatun kungiyar. Da yake magana a wani shiri na gidan Talabijin na Channels, ‘The Morning Brief’ a ranar Litinin, Alausa ya bayyana rashin jin dadinsa da matakin da ASUU ta dauka na tsunduma yajin aiki duk da kokarin da gwamnatin ke yi akansu. “A cikin shekaru biyun da suka gabata, babu wani batun yajin aikin ASUU, saboda kokarin da gwamnati ke yi akan biyan duk bukatunsu. “A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, ni da mataimakin shugaban kwamitin tattaunawa na gwamnatin tarayya, mun tattauna da ASUU, zan iya gaya muku a yau, a zahiri, an biya kusan dukkan bukatun ASUU, don haka ban ga dalilin da ya sa ASUU ta fara yajin aikin ba.” In ji Ministan ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano October 13, 2025
Ra'ayi Riga Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang October 13, 2025
Labarai Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista October 13, 2025