Leadership News Hausa:
2025-11-18@09:03:29 GMT

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Published: 29th, September 2025 GMT

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Ƙungiyar ma’aikatan man fetur da iskar gas ta Nijeriya, wato PENGASSAN, ta fara yajin aiki a faɗin Nijeriya daga daren Litinin, 29 ga Satumba, 2025. Wannan na zuwa ne bayan umarnin da shugabancin ƙungiyar ya bayar tun ranar Lahadi, inda aka umurci mambobi da su tsaida aiki a dukkan kamfanoni da cibiyoyi da hukumomin da suke aiki a su.

A sakamakon haka, an kulle ƙofar shiga shalƙwatar hukumar NUPRC da ke Abuja, inda ɗaruruwan ma’aikata suka taru a waje ba tare da an bari sun shiga ba. Wannan mataki ya haddasa tsaiko a gudanar da ayyuka, musamman a sashen kula da harkokin mai da iskar gas na ƙasar.

Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

PENGASSAN ta bayyana cewa yajin aikin ya samo asali ne daga korar kusan ma’aikata 800 a Matatar Man Dangote, inda aka zargi kamfanin da maye gurbinsu da baƙi daga ƙasashen waje. Ƙungiyar ta ce wannan lamarin babban cin zarafi ne ga dokokin ƙwadago na Nijeriya da na Ƙungiyar Kwadago ta Duniya (ILO).

Sakatare Janar na PENGASSAN, Lumumba Okugbawa, ya yi kakkausar suka ga Matatar Dangote, yana mai zargin kamfanin da korar ma’aikatan ne saboda shiga ƙungiyar ƙwadago. Ya ce wannan doka ce aka karya, tare da tabbatar da cewa ƙungiyar ba za ta janye daga yajin aikin ba sai an warware matsalar tare da dawo da ƴan uwansu bakin aiki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Tinubu ba ta shirya kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga ba — Amnesty

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International ta yi kakkausar suka kan sabon harin da ’yan bindiga suka kai makarantar sakandare ta ’yan mata da ke garin Maga a Jihar Kebbi, wanda ya kai ga sace ɗalibai mata sama da 25 tare da halaka mai gadi da mataimakin shugaban makarantar.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, Amnesty ta bayyana lamarin a matsayin abin takaici da kuma nuna gazawar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu wajen kare rayuka da dukiyoyin ’yan kasa ballantana kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga.

CAF ta fitar da ’yan wasa uku da suka rage a takarar gwarzon Afirka na bana Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas

Ƙungiyar ta ce bincikenta ya gano cewar ’yan bindigar sun kai hari ne da misalin ƙarfe 5 na safiya, inda suka tilasta wani ma’aikacin makarantar ya nuna musu ɗakin kwanan daliban mata, sannan suka yi awon gaba da su.

Amnesty ta ce wannan harin ya sake nuna cewa, “gwamnatin Tinubu ba ta da wani ingantaccen tsari na kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga, duk da matakan da ake ce an ɗauka, domin babu wani gagarumin sauyi da aka gani a ƙasa.”

Ƙungiyar ta buƙaci gwamnati da hukumomin tsaro su ɗauki matakan gaggawa domin ceto ɗaliban cikin aminci, tare da gano musabbabin yawaitar sace-sacen mutane a sassan ƙasar, abin da ta ce yana barazana ga ilimi da zaman lafiyar al’umma.

Gwamnatin Najeriya ta yi Allah wadai da sace ɗaliban

A nata ɓangaren, gwamnatin Najeriya ta bayyana tsananin damuwa kan harin, inda ta ce ta bai wa jami’an tsaro umarnin gano da ceto ɗaliban cikin gaggawa.

Cikin wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai, Muhammad Idris ya fitar, ya ce gwamnati za ta tabbata an kamo waɗanda suka kai harin domin su fuskanci hukunci.

Ya ƙara da cewa gwamnati na tare da iyaye da ’yan uwan waɗanda abin ya shafa, tare da jaddada cewa za a yi duk wani abu mai yiyuwa domin ganin yaran sun koma gida cikin aminci.

Za mu dawo da duk ɗaliban da aka sace —Jami’an Tsaro

Wata rundunar haɗin gwiwa ta jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji da ’yan sanda, na ci gaba da laluben ɗaliban bayan ’yan bindiga sun awon gaba da su.

Da sanyin safiyar Litinin, 17 ga watan Nuwambar 2025, mahara suka shiga a makarantar ’yan matan, inda bayanai ke nuni da cewa an sace ɗalibai 25 tare da halaka mataimakin shugaban makarantar da wani maigadi kana suka jikkatar da dama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sace Ɗalibai: Gwamnatin Tinubu ba ta shirya kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga ba — Amnesty
  • Hauhawar farashi ya ƙara raguwa a Nijeriya — NBS
  • Shugaban Nukiliyar Iran Yace Amurka Da Israila Sun Shiga Sabon Mataki Mai Hadari
  • ’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
  • Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
  • ’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
  • Na kusa komawa APC – Gwamnan Taraba
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • Ma’aikatan lafiya sun tsunduma yajin aiki
  • Ma’aukatan lafiya sun tsunduma yajin aiki