Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba
Published: 29th, September 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa da ƴan Nijeriya cewa za a ci gaba da samun isasshen man fetur duk da barazanar shiga yajin aiki da ƙungiyar PENGASSAN ta yi kan taƙaddama da matatar man Dangote. Wannan na zuwa ne bayan raɗe-raɗin cewa matatar ta dakatar da tsarin siyar da ɗanyen mai da ake biya sa da Naira.
A wata sanarwa daga ma’aikatar kuɗi ta tarayya, daraktan hulɗa da jama’a Mohammed Manga ya bayyana cewa an gudanar da taron kwamitin kula da tsarin “buyqn Naira-don sayen ɗanyen mai” ƙarƙashin jagorancin Ministan Kuɗi, Wale Edun. Taron ya samu halartar Ministan tsare-tsare, da shugaban FIRS, da wakilai daga NNPC, CBN, NMDPRA da Afreximbank.
Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar NairaSanarwar ta bayyana cewa matatar Dangote ta tabbatar ba za a samu tangarɗa ba wajen samar da man fetur, tare da jaddada cewa tsarin biyan Naira zai ci gaba da aiki yadda aka tsara. Haka kuma, an tabbatar cewa Ƙorafe-ƙorafen PENGASSAN na cikin abubuwan da za a bincika kuma a tattauna
Gwamnati ta ce tana ɗaukar matakan gaggawa cikin gaskiya wajen warware duk wani saɓani domin kare kowanne tsagi, da tabbatar da tsaron makamashi, da kiyaye daidaito a kasuwar man fetur. An kuma yi kira ga ƴan ƙasa da su kwantar da hankalinsu yayin da ake ci gaba da shawo kan batun.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yajin Aiki
এছাড়াও পড়ুন:
Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
“Shekaru goma da suka wuce, gudummawar da ma’adanai ke bayarwa ga GDP na kasarmu bai wuce 0.5% ba, amma a yau ya karu zuwa 1.8% – alkalumman NBS suka nuna a cikin rabi na biyu na 2025 wanda ba a taba ganin irinsa ba”.
Da yake tsokaci kan ci gaban fannin, Ministan ya bayyana cewa, makon hako ma’adanai na Nijeriya ya yi nuni da yadda masana’antar ke sauya tunani zuwa tsari mai kyau, da sabbin abubuwa, da ke lalubo masu zuba jari na kasa da kasa.
Ya bayyana cewa, sauye-sauyen sun tattara ne a kan gaskiya, rage haɗari, da inganta masana’antar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA