Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba
Published: 29th, September 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa da ƴan Nijeriya cewa za a ci gaba da samun isasshen man fetur duk da barazanar shiga yajin aiki da ƙungiyar PENGASSAN ta yi kan taƙaddama da matatar man Dangote. Wannan na zuwa ne bayan raɗe-raɗin cewa matatar ta dakatar da tsarin siyar da ɗanyen mai da ake biya sa da Naira.
A wata sanarwa daga ma’aikatar kuɗi ta tarayya, daraktan hulɗa da jama’a Mohammed Manga ya bayyana cewa an gudanar da taron kwamitin kula da tsarin “buyqn Naira-don sayen ɗanyen mai” ƙarƙashin jagorancin Ministan Kuɗi, Wale Edun. Taron ya samu halartar Ministan tsare-tsare, da shugaban FIRS, da wakilai daga NNPC, CBN, NMDPRA da Afreximbank.
Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar NairaSanarwar ta bayyana cewa matatar Dangote ta tabbatar ba za a samu tangarɗa ba wajen samar da man fetur, tare da jaddada cewa tsarin biyan Naira zai ci gaba da aiki yadda aka tsara. Haka kuma, an tabbatar cewa Ƙorafe-ƙorafen PENGASSAN na cikin abubuwan da za a bincika kuma a tattauna
Gwamnati ta ce tana ɗaukar matakan gaggawa cikin gaskiya wajen warware duk wani saɓani domin kare kowanne tsagi, da tabbatar da tsaron makamashi, da kiyaye daidaito a kasuwar man fetur. An kuma yi kira ga ƴan ƙasa da su kwantar da hankalinsu yayin da ake ci gaba da shawo kan batun.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yajin Aiki
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
An kulle Fadar Shugaban Kasar Amurka ta White House tare da wasu gine-ginen gwamnati da dama, sakamakon harbin ɗan bindigar da ya raunata sojoji biyu a kusa da fadar.
A yayin, an harbe masu tsaron fadar biyu har lahira.
Gwamna Patrick Morrisey da farko ya ce an kashe sojojin, amma daga baya ya ce yana samun “rahotanni masu karo da juna” game da halin da suke ciki, yana mai da cewa za a fitar da ƙarin bayani idan an tabbatar.
A cikin wani rubutu a shafin X, ya ce, “Yanzu muna samun rahotanni masu cin karo da juna game da halin sojojin biyu, kuma za mu bayar da ƙarin bayani idan mun samu cikakken rahoto.
“Addu’o’inmu suna tare da waɗannan jarumai, iyalansu, da dukan al’ummar Amurka.”
A cewar rahotanni, Shugaba Donald Trump yana gidansa na hutu a Mar-a-Lago da ke Palm Beach, Florida, a lokacin da lamarin ya faru.
Mai magana da yawun Fadar White House, Karoline Leavitt, ta ce cikin wata sanarwa: “Fadar White House ta san da wannan mummunan lamari kuma tana bin diddigi. Shugaban kasa ya samu cikakken bayani.”
’Yan sandan birnin Washington DC sun ce an kama wanda ake zargi da harbin.
Sojojin National Guard sun kasance a Washington DC tsawon watanni a matsayin wani bangare na matakin Trump na yaki da laifuka a babban birnin ƙasar.
A cikin wani rubutu a dandalinsa na Truth Social, Trump ya ce: “Dabban da ya harbi mambobin National Guard biyu, wanda dukkansu suka ji rauni mai tsanani kuma yanzu suna a asibitoci daban-daban, shi ma ya ji rauni sosai, amma duk da haka, zai ɗanɗana kuɗarsa.”