NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Da Ɗangote, PENGASSAN Ba Su Bi Ba Don Magance Taƙaddamarsu
Published: 29th, September 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Gwamnatin Tarayya ta gayyaci Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (PENGASSAN) da Matatar Ɗangote don a sasanta a yau.
Hakan ya biyo bayan umarnin da ’yan ƙwadagon suka bai wa mambobinsu ne na shiga yajin aiki bayan da Matatar Ɗangote ta salami ma’aikata fiye da 800.
Sai dai wasu masana suna ganin tun farko bai kamata lamarin ya kai ga haka ba, da an bi wasu hanyoyi.
NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Gubar Cikin Abinci DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya KamataWaɗannan hanyoyi shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai binciko.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
Rahotanni sun tabbatar da rasuwar wasu sojoji huɗu, bayan ’yan ta’adda sun kai hari yankin Ngamdu na Jihar Borno.
Jihar Borno ta daɗe tana fama da hare-haren ta’addanci, musamman daga ƙungiyar Boko Haram.
Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno An yi jana’izar sojojin da ’yan bindiga suka kashe a KebbiKo da yake wasu mazauna yankin sun ce sojoji 10 ne suka mutu, sai dai mai magana da yawun rundunar Operation Haɗin Kai, Laftanar Kanar Sani Uba, bai tabbatar da hakan ba cikin sanarwar ya fitar a ranar Juma’a.
Amma rahotanni sun bayyana cewa sojoji huɗu ne suka mutu, yayin da wasu biyar suka jikkata a yayin harin.
A cewar Kanar Sani, ’yan ta’addan sun yi amfani da roka, jirage marasa matuƙa, da bama-bamai wajen kai harin.
Sai dai sojojin sun mayar da martani, inda suka kashe da dama daga cikin ’yan ta’addan.
Ya ƙara da cewa wasu motocin yaƙi na sojojin sun lalace, amma duk da haka dakarun sun yi tsayin daka wajen yaƙar maharan.
Bayan harin, ’yan ta’addan sun yi ƙoƙarin hana bin hanyar Ngamdu zuwa Damaturu, wanda hakan ya tilasta rufe hanyar na ɗan lokaci.
Daga baya,sojoji sun cire bama-bamai guda uku, sannan suka sake buɗe hanyar ga matafiya.
Laftanar Kanar Uba, ya ce an ƙara wa dakarun kayan yaƙi da harsasai domin ci gaba da fafatawa.
Rahotanni sun nuna cewa gawarwakin ’yan ta’adda kusan 15 aka samu a kusa da ƙauyen Bula Wura.
Rundunar Sojin Najeriya ta yaba wa jarumtar dakarun, tare da tabbatar wa jama’a cewa zaman lafiya ya samu a yankin.