Aminiya:
2025-11-27@21:48:45 GMT

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Da Ɗangote, PENGASSAN Ba Su Bi Ba Don Magance Taƙaddamarsu

Published: 29th, September 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Gwamnatin Tarayya ta gayyaci Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (PENGASSAN) da Matatar Ɗangote don a sasanta a yau.

Hakan ya biyo bayan umarnin da ’yan ƙwadagon suka bai wa mambobinsu ne na shiga yajin aiki bayan da Matatar Ɗangote ta salami ma’aikata fiye da 800.

Sai dai wasu masana suna ganin tun farko bai kamata lamarin ya kai ga haka ba, da an bi wasu hanyoyi.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Gubar Cikin Abinci DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata

Waɗannan hanyoyi shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai binciko.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi

A ranar Alhamis, 27 ga watan Nuwamban 2025 ce Allah ya yi wa fitaccen malamin addinin Musuluncin nan kuma jigo a Darikar Tijjaniyya a Najeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi rasuwa.

Ya rasu yana da sama da shekaru 100 a duniya.

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani

Baya ga tarin iliminsa da yawan shekaru, akwai wasu tarin baiwa da Allah Ya ba malamin, wadanda ba kowa ne ya san da su ba.

Aminiya ta yi nazari a kansu, inda ta zakulo muku abubuwa 18 da ya kamata ku sani a kansa.

Ga wasu daga ciki:

Ya fi kowa yawan zuri’ar da ta haddace Alkur’ani a duniya, inda yake da ’ya’ya da jikoki da tataba-kunne kusan 300 da suka haddace Alkur’ani mai girma Kundin tattara bayanai na Cholan Book Of World Records, ya ba shi shaidar girmamawa saboda yawan zuri’a mahaddata Yana da ’ya’ya 95 Yana da jikoki 406 Yana da tattaba-kunne 100 ’Ya’yansa mahaddata Alkur’ani 77 Jikokinsa mahaddata Alkur’ani 199 Tattaba-kunnensa mahaddata Alkur’ani 12 Shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Koli da ke bayar da fatawa a addinin Musulunci a Najeriya An haife shi a watan Janairun 1927, wanda ya yi daidai da watan Muharram 1346 Bayan Hijira A ranar Laraba aka haife shi a a garin Nafada da ke Jihar Gombe a yanzu Kwararre ne a fannin Alkur’ani da Tafsiri da Ma’arifa da Hadisi da Harshen Larabci da Li’irabi da Fikihu Jami’ar Tarayya da ke Lafiya a Jihar Nasarawa ta ba shi Digirin girmamawa Gwamnatin Najeriya ta ba shi lambar girmamawa ta kasa ta OFR Ya musuluntar da dubban mutane Yakan yi saukar Alkur’ani duk bayan kwana biyu Mutane fiye da 140,924 suka haddace Alkur’ani a makarantunsa da ke fadin Najeriya Ya kafa makarantun haddar Alkur’ani sama da 1,500 a Najeriya da wasu kasashen Afirka Karkashin gidauniyasa, an gina dakunan karatu guda 133,060 a Arewacin Najeriya Ya shafe shekaru sama da 50 yana gabatar da tafsirin Alkur’ani a cikin watan Ramadan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci
  • Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
  • NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta