Iran Da Afganistan Sun Tattauna Al-Amura Masu Muhiammaci A Kabul
Published: 26th, January 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi wanda ya jagoranci tawagar yan siyasa da kuma tattalin arzikin kasarsa zuwa birnin Kabul babban birnin kasar Afganistan, a yau Lahadi sun tattauna al-amura masu muhimmanci tsakaninsu da kuma yanking aba daya.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa ministan ta hadu da tokwaransa na rikon kwarya Amir Khan Muttaki a birnin Kabul inda suka tattauna al-amura da suka shafi kasashen biyu.
Ministocin biyu sun tattauna al-amura da suka shafi kasashen biyu, wadanda suka hada da makobtaka, musulunci, al-adu da sauransu. Kasashen biyu malobta ne na shekaru aru-aru.
A nashi bangaren Muttaki ya godewa kasar Iran kan daukar bakwantan miliyoyin yan kasar Afganistan, ya kuma bayyana cewa gwamnatin Taliban tana iya kokarinta don ganin sun dawo gida musamman ganin cewa al-amura sun fara kyautata a kasar.
Sannan daga karshe ya ce kasashen biyu zasu yi aiki tare don yaki da yan ta’adda a kasashen biyu musamman a kan iyakokin kasashen biyu
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai
A yammacin ranar Talata Arsenal ta karbi bakuncin PSG a matakin wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin zakarun Turai na bana.
An dai barje gumi ne a filin wasa na Emirates, inda PSG ta yi wa Arsenal ci daya mai ban haushi har gida.
DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a BornoPSG ta fara cin ƙwallo ta hannun Ousmane Dembele a minti na huɗu da take leda, haka suka je hutu har da zagaye na biyu, amma Gunners ba ta farke ba.
Wannan shi ne karo na biyu da suka fuskanci juna a Champions League a kakar nan, inda Gunners ta yi nasarar cin 2-0 a Emirates a cikin watan Oktoba.
Arsenal da Paris Saint-Germain da Inter Milan da Barcelona su ne kungiyoyin da 4 da suka kai matakin zagayen daf da karshe na gasar.
A wannan Larabar ce kuma za a yi karon batta tsakanin Inter Milan da Barcelona, bayan kimanin shekara 15 da aka yi makamancin wannan karawar daf da karshe tsakanin ƙungiyoyin biyu a Gasar Zakarun Turai.
Inter Milan ce ta kai zagayen ƙarshe a 2010, sai dai wannan karon Barcelona na fatan lashe kofin bana da zarar ta fuskanci Arsenal ko Paris St Germain a watan gobe.
Sai dai, Barca da Inter sun fuskanci juna a gasar ta zakarun Turai a 2022/23, inda ta Italiya ta yi nasara 1-0 cikin Oktoban 2022 a wasa na biyu suka tashi 3-3 a Sifaniya.
Wannan shi ne karon farko da Barcelona ke fatan kai wa karawar ƙarshe a Champions League, tun bayan da ta lashe na biyar jimilla a 2015.