HausaTv:
2025-07-31@14:42:08 GMT

An Kammala Jana’izar Paparoma Farancis A Birnin Vatican

Published: 27th, April 2025 GMT

Fafa roma Farancis shugaban cocin catholica ya koma makwancin na din din din a Santa Maria Maggiore Basilica, wanda kuma ake kira St. Mary Major, daya daga cikin fitattun coci-coci guda 4 mafi daraja a birnin Vatican .

Shafin yanar gizo na labarai ‘Afrika News’ ya bayyana cewa Farancis shi ne paparoma na farko daga yankin Laten Amurka, wanda kuma ya kirkiro abubuwa da dama a cocin daga ciki shi ne ya fara zaben inda za’a yi masa kabari.

Kuma shi ne ya fara zaben a bisneshi a wajen birnin Vatikan tun shekaru fiye da 120 da suka gabata. Wato tun bayan Paparoma Leo 13.

Tashar talabijin ta CNN ta nakalto cewa fafaroman ya bukaci a yi masa kabari mai sauki a wajen birnin Roma wato Basilica di Santa Maria Maggiore.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 

Wani mutum ya rasu yayin da yake ƙoƙarin raba wani mutum da matarsa da fada a yankin Babban Birnin Tarayya.

Da farko mutumin ya faɗi ne a sume kafin daga bisani rai ya yi halinsa a yankin Dogon-Ruwa da ke Ƙaramar Hukumar Abaji.

Wani ganau, Barnabas Yakubu, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da yamma ne ma’auratan, waɗanda makwabta ne ga mamacin, suka fara faɗa ne bayan wata rashin fahimta, shi kuma Ayuba, bayan jin hayaniyar, ya fito daga ɗakinsa don shiga tsakani.

A cewarsa, mamacin ya dawo ne daga gonarsa kuma yana shirin yin wanka lokacin da ya ji maƙwabcinsa yana dukan matarsa.

Ya ce, Ayuba nan take ya ajiye soso da gugar ruwansa ya ruga don shiga tsakani amma ya faɗi sumamme a yayin.

Ayuba, wanda aka yi imanin yana cikin koshin lafiya kafin faruwar lamarin, an garzaya da shi asibiti a garin Gawu, inda likitocin da ke bakin aiki suka tabbatar da mutuwarsa.

Sarkin yankin, bayan samun labarin lamarin, ya sanar da ’yan banga tare da ba da umarnin kama ma’auratan, waɗanda daga baya aka mika su ga jami’an tsaro a Gawu.

Ibrahim, daya daga cikin ’yan bangan, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa, “Mun fahimci cewa ƙaramar rashin fahimta ce kawai ta kai ga faɗan tsakanin makwabcin mamacin da matarsa.”

Ya ƙara da cewa an kai gawar mamacin kauyensa na Paiko a Jihar Neja don binnewa.

’Yan sanda a yankin Gawu sun tabbatar da faruwar lamarin, inda suka ce har yanzu ana ci gaba da bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran