Sarkin Kano Na 15, Aminu Ado Bayero Zai Naɗa Ɗan Uwansa Sanusi Ado A Matsayin Galadiman Kano
Published: 27th, April 2025 GMT
Wannan naɗi ya zama wani babban mataki a cikin mulkin Sarkin Kano Aminu Ado Bayero, wanda ke ci gaba da kiyaye al’adun masarautar tare da haɗa kan al’umma.
Sai dai kuma a cikin wannan wata ne Sarkin Kano na 16 Sanusi Lamido Sanusi II, ya fara naɗa Alhaji Mannir Sanusi (Hakimin Bichi) a wannan muƙami bayan rasuwar tsohon Galadima.
Za a iya cewa dai yanzu bayan Sarakuna biyu Kano na da Galadima biyu da aka naɗa a wata guda sakamakon Sarkuna biyun dake da’awar zama halattaccen Sarki, duk da dai Sarki Sanusi Lamido II shi yake gidan Rumfa yayin da Sarki Aminu ke gida masauƙin baƙi da na Nassarawa da ya mayar da shi sabuwar fadarsa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Bayero
এছাড়াও পড়ুন:
Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3
Cibiyar Blue Sapphire ta kaddamar da wani shiri na musamman da aka kirkiro domin ƙarfafa gwiwar mata ’yan kasuwa a fannin dinkin kayan sawa da kuma harkokin kirkira a arewa maso yammacin Najeriya.
Cibiyar na aiwatar da wannan shiri ne tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar ’Yan Kasuwa Mata ta Arewa (ANWE) da Jami’ar Northwest Kano, tare da tallafin Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU).
Dukiyar sama da miliyan 500 ta kone a gobarar kasuwar katako ta Gombe ‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’Da take jawabi a wajen kaddamarwar a Kano ranar Talata, shugabar cibiyar, Maryam Lawan Gwadabe, ta ce an kirkiro shirin ne domin samar wa mata amintaccen muhallin da za su yi amfani da shi wajen bunƙasa kasuwancinsu.
Ta ce shirin zai gudana a jihohin Kano, Katsina da Sakkwato domin ƙarfafa tattalin arzikin mata da kuma tabbatar da sun samu dogaro da kai.
“Mun sanya wa shirin suna Women Venture Studio domin tabbatar da cewa mata za su ji daɗin kasancewa a cikin muhalli mai tsaro. Masu ba da shawara a nan su ne ’yan kasuwa da matan da suka yi nasara, waɗanda za su saurara, su jagoranta, kuma su tallafa wa mahalarta shirin,” in ji ta.
Maryam ta ƙara da cewa cibiyar tana bayar da wuraren yin aiki na zahiri da na intanet, domin tabbatar da cewa ana damawa da mat aba tare da an ware su ba.
Shugabar cibiyar ta kuma ce matakin farko na shirin zai haɗa da horar da mata 150, wato mata 50 daga kowacce jiha.
Ita ma da take jawabi, Shugabar ANWE, Hafsat Sahabi Dange, ta ce shirin ya fi mayar da hankali kan mata a fannin kirkira, musamman a harkar dinka kaya, sana’o’in hannu da fasaha.
“Manufarmu ita ce mu sauya waɗannan kasuwancin zuwa tsarin zamani domin mata su iya yin gogayya, ba kawai a Najeriya ba, har ma a duniya. Wannan shiri zai shafi ’ya’ya mata da kuma mata ta hanyar amfani da kirkirarsu da kuma ƙarfafa musu tsarin kasuwanci a Arewacin Najeriya,” in ji ta.
A nata bangaren, wakiliyar Tarayyar Turai a Najeriya da ECOWAS, Inga Stefanovic, ta ce EU ta ware sama da Yuro miliyan 700 a matsayin tallafi domin tallafa wa ayyuka daban-daban a fadin Najeriya.
Ta jaddada cewa haɗin gwiwar EU da Najeriya ya shafi fannoni da dama ciki har da fasahar zamani, bunkasa tattalin arziki, dimokuraɗiyya, zaman lafiya da tsaro, lafiya, ilimi, samar da makamashi da kuma noma.