HausaTv:
2025-05-18@15:27:49 GMT

Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje

Published: 28th, April 2025 GMT

Shugaban kasar Iran ya nuna murnarsa da yin maraba lalai da masu zuba hannun jari daga kasashen waje a Iran

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana Iran a matsayin dandalin da ta dace wajen zuba hannun jari da gudanar da harkar kasuwanci, yana maraba da masu zuba hannun jari na kasashen waje da ‘yan kasuwa na duniya da su shiga harkokin tattalin arziki da zuba hannun jari a Iran.

A yayin bikin bude baje koli karo na bakwai na baje kolin kayayyakin da Iran ke fitarwa zuwa kasashen ketare (Iran Expo 2025) a safiyar yau Litinin, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi maraba da baki na kasashen waje da suka halarci wannan baje kolin, yana mai cewa, “Ko da yake ana gabatar musu da wani hoto na daban da ya yi hannun riga da hakikanin Iran da al’ummar kasarta a ketare, amma Iran kasa ce mai karbar baki, kuma al’ummarta masu tausayi da nuna jin kai.”

Yana mai jaddada cewa: Iran wata kafa ce da ta dace da zuba hannun jarin kasuwanci da yawon bude ido na ketare, Pezeshkian ya bayyana cewa da wannan karfin, kuma ta hanyar ciniki, zuba hannun jari, da hadin gwiwa, za a iya samar da makoma mai haske ga duniya, mai cike da tsaro da zaman lafiya.

Ya kuma yi nuni da cewa: Yake-yaken da suka gani a duniya sun samo asali ne sakamakon rashin mutunta hakkokin bil’adama da na kasashe, Pezeshkian ya jaddada mutunta yankin kasar Iran da hakkokin kasashe, yana mai bayyana Shirin Iran na gudanar da duk wani hadin gwiwa a fannin kimiyya, tattalin arziki, siyasa, da zamantakewa da duniya, da kuma mika ilimi ga sauran kasashe ba tare da iyakancewa ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: zuba hannun jari Pezeshkian ya

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora: Jawaban Trump A Ziyar Da Ya Kai Wasu Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Abin Kunya Ne Gare Shi Ga Kuma Amurkawa

Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya yi watsi da wasu kalaman shugaban kasar Amurka Donal Trump a ziyar da ya kammala a wasu kasashen larabawa na yankin Tekun farisa, ya kuma bayyana wasu kalamansa a matsayin kungiya ga kansa da kuma mutanen Amurka. Har’ila yau Jagoran ya kara da cewa da dama daga cikin maganganunsa basu cancanci maida martani ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a yau Asabar, a lokacinda yake ganawa da wasu malaman makaransu daga larduna daban daban na kasar, a Husainiyyar Imam Khonaini (q) a nan Tehran.

Jagoran ya kara da cewa : Trump yace yana son amfani da karfin da Amurka take da shi don samar da zaman lafiya wanda karaye ce, saboda. Shi da jami’an gwamnatin Amurka da suna amfani da karfi wajen kashe mutanen Gaza, sannan suna farwa kasashe da yaki, inda zasu iya. Haka ma suna amfani da karfi wajen goyon bayan ma’aikatansu a kasashen duniya da dama don kare bukatu da manufofinsu a wadannan kasashe.

A wani wuri a jawabinsa jagoran ya bayyana cewa, gaskiya ne ana amfani da karfi don samar da zaman lafiya a wani lokaci, kamar yadda JMI take bunkasa karfinta na makamai da kuma dabarbarun yaki a ko wani lokaci.

Amma Amurka da kawayenta da dama suna amfani da karfinsu suna goyon bayan HKI don ta kashe yara a Gaza, ta rusa asbitoci a gaza, ta kuma rusa gidajen mutane a Gaza da Lebanon da Yemen da duk inda zasu iya yin haka.

Imam Khaminae ya sifanta HKI a matsayin mabubbukan barna da rashin zaman lafiya da cusa  gaba cikin kasashen yammacin Asiya. Yace ” HKI a wannan yankin tana kamar cutar daje ce, wacce dole a tumbuketa daga wannan yankin.

Dangane da fadin shugaba Trump kan cewa gwamnatocin kasashen yankin ba zasu iya tabbata a kan kujerun shugabancin kasashensu na kwana goma ba. Jagoran yace wannan ma kariya ce ba haka ba, wannan tsarin ya fada, tare da gwagwarmayan kasashen wannan yankin sai an kori Amurka daga cikinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • Ayatullah Khamenei : “Ba inda Rundunar Amurka ta taba shinfida zaman lafiya “
  • Senegal ta karbi wani sansaninta na uku daga hannun Faransa
  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa
  • Jagora: Jawaban Trump A Ziyar Da Ya Kai Wasu Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Abin Kunya Ne Gare Shi Ga Kuma Amurkawa
  • Iran: Aiwatarda Yarjeniyar Zaman Lafiya Tsakanin Armenia Da Arzerbaijan Zai Tabbatar Da Zaman Lafiya A Tsakanin Kasashen Biyu
  • Shuwagabanin Larabawa Sun Yi Alkawalin Sake Gina Gaza, Suna Kuma Kokarin Tsagaita Wuta Da Farko
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Ce Ba Ta Tsoron Duk Wata Barazana Don Neman Tauyaye Mata Hakki
  • Iran da E3 sun kuduri aniyar bin hanyoyin diflomasiyya dangane da shirin nukiliyar Iran
  • Pezeshkian : Zaman lafiya muke nema, ba yaki ba