Aminiya:
2025-11-08@18:18:37 GMT

Sojoji sun kashe ’yan ta’dda 1,770 sun kama 3,070 a Arewa —Janar Musa

Published: 26th, April 2025 GMT

Rundunar Sojin Najeriya ta samar da cewa dakarunta sun kashe ’yan ta’adda 1,770, sun kama wasu 3,070 a yankin Arewa maso Yamma a shekaru uku da suka gabata.

Rundunar ta kuma yi nasarar ceto mutane fiye da 2,515 da harin ya rutsa da su ta hanyar gudanar da ayyukan haɗin gwiwa a jihohin da lamarin ya shafa.

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ne ya sanar da hakan a yayin wani gangamin wayar da kan jama’a a Jihar Katsina, wanda aka gudanar ga mazauna ƙananan hukumomin Batsari da Dutsin-Ma.

Janar Musa ya ce, sun kuma ƙwato sama da makamai 1,000 da alburusai 12,000 a hare-haren da suka kai a jihohin Arewa maso Yamma guda biyar, wato Katsina, Kaduna, Kebbi, Sokoto, da Zamfara, tare da daƙile ayyukan ta’addanci.

Magidanci ya kashe kansa saboda mutuwar matarsa a Neja Janyewar sojoji ke ba Boko Haram damar ƙwace yankuna —Zulum

“Sojoji na yin iya ƙoƙarinsu wajen yaƙi da matsalar tsaro,” in ji shi, yana mai jaddada cewa nasarorin da aka samu wani ɓangare ne na ƙoƙarin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin ƙasar.

Aikin na da nufin ƙarfafa haɗin gwiwar al’umma da shugabannin sojoji da mazauna yankuna a wani yunƙuri na ƙulla alaƙa mai ƙarfi da ƙarfafa sanya ido a tsakanin al’ummomi.

A yayin taron wayar da kan al’umma, Janar Musa ya tunatar da mazauna yankin cewa wanzar da zaman lafiya nauyi ne na haɗin gwiwa. Ya kuma yi kira ga al’ummomin da su ba da rahoton abubuwan da ake zargi da kuma tallafa wa juna.

Janar Musa ya kuma bayyana cewa, a halin yanzu sojoji na sake yin wani shiri domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkan al’ummomin da ke kan gaba a matsalar tsaro.

Wannan yana nuna ci-gaba da sadaukar da kai ga ɗaukar matakan tsaro da barazana yayin da mazauna da yawa suka yarda da ingantaccen tsaron.

Al’umma a Batsari sun yaba da ƙoƙarin baya-bayan nan, musamman tattaunawar da aka yi da masu laifin da suka tuba, wanda ya taimaka wajen raguwar tashin hankali.

Duk da haka, wasu sun bayyana damuwarsu. Malam Lawal Rabi’u, wani mazaunin yankin, ya nuna damuwarsa kan hare-haren ’yan bindiga daga ƙananan hukumomin da ke maƙwabtaka da su inda har yanzu ba a fara aiwatar da shirin na sulhu ba.

Duk da waɗannan ƙalubalen, babban saƙon sojoji yana ba da ƙarfi da begen yin gamayya. Kiran da Janar Musa ya yi na haɗin kai inda ya ce, “Tare, za mu iya dakatar da ci gaba da tashin hankali da muryar zaman lafiya,” ya yi ƙarfi a tsakanin waɗanda suka halarta, yana mai jaddada ra’ayin cewa dawwamammen zaman lafiya ya dogara ne da haɗin gwiwar sojoji da ’yan Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda Arewa maso Gabas Janar Musa ya zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

“Lamarin daya kai miliyan daya na wadanda suka nemi a basu bashin karatu, lalle abin ya nuna a gaskiya matasa sun son su kyautata yadda rayuwarsu data wasu zata kasance a gaba, musamman ma yadda suka maida hankali wajen neman ilimi.

Ya ci gaba da bayanin “Wannan yana nunawa a fili yadda jagorancin na Shugaban kasa Bola Tinubu ya damu da lamarin ilimi domin shi ne ginshikin ci gaban al’umma kamar yadda ya ce,”.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ilimi Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu October 18, 2025 Ilimi Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma October 18, 2025 Ilimi Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU October 18, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock
  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita