HausaTv:
2025-07-31@06:26:34 GMT

Iran Ta Gabatar Da Tayin Shiga Tsakanin Don Sasanta Indiya Da Pakisatan

Published: 26th, April 2025 GMT

A dai-dai lokacinda kasashen Indiya da Pakisatn suke tada jijiyoyin wuta kan wani harin ta’addanci da ya kai ga mutuwar mutane 27 masu yawon shakatawa a yankin Kashmir na kasar Indiya, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya gabatar da tayin shiga tsakani don dai-daita tsakanin kasashen biy.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka, a shafinsa na X, ya kuma kara da cewa Iran tana da dangantaka mai karfi tsakaninta da kasashen biyu, kuma makobta ne kuma yan uwa wadanda suke da tsohuwar dangantaka ta al-adu a tsakaninsu na karnuka, ba za muyi kasa a guiwa wajen sasantasu ba, idan sun bamu wannan damar.

A cikin makon da ya gabata ne wasu yan bindiga suka bude wuta kan wasu maso yawan shakatawa a yankin Kashmir na kasar Iran inda mutane 27 suka mutu. Gwamnatin Undiya tana zargin Pakistan da hannu dumu-dumu a cikinsa, a yayinda gwamnatin kasar Pakisatan ta musanta hakan ta kuma yi allawadai da harin. Amma ta kara da cewa idan indiya ta kuskura ta yi amfani da makami a kanta to zata rana.

A daren jamm’an da ta gabata dai bangarorin biyu sun kai ga musayar wuta a tsakaninsu a kan iyakokin kasashen biyu.

Ministan ya bayyana cewa kasar zata yi amfani da ofisoshin jakadancin kasashen biyu a Islamabad da kuma New Delhi don shiga tsakanin  su idan sun amince da hakan.

Kasashen indiya da Pakistan dai sun dade suna takaddama kan mallakar Yankin Kashmir kuma sun sha shiga yaki saboda hakan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

Tawagogin wakilan kasashen Sin da Amurka sun hallara a kasar Sweden yau Litinin, domin fara wani sabon zagayen tattaunawa game da cinikayya da tattalin arziki. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza
  • An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden
  •  Bakai’i: Iran Tana Son Ganin An Yi Taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Kasashen Iran Da Rasha